Noor-Al-Hayat COMPLETE HAUSA NOVEL

Noor-Al-Hayat COMPLETE HAUSA NOVEL

Karfe goma na safiyar washegari Khadijah na kwance daki ta rufe ido kamar mai bacci don gaisuwar da ake mata na shureim na kara daga mata hankali, hakan yasa duk wanda ma ya xo umma da Nanny yake ma gaisuwar, Umma ce ta shigo dakin ta taba ta duk da tasan ba bacci take ba, Khadijah ta bude idanuwanta da suka mata nauyi tana kallon umman nata, cikin kwantar da murya umma tace “Taso mu je an xo maki gaisuwa” ta d’an hade rai tace “Umma ba ga ku ba bacci fa nake” Umma tace “Mahaifiyar khaleel ce shi yasa ma na tashe ki” shiru khadijah tayi tana kallon umma, can Khadijah ta mike xaune a hankali, umma ta kama hannunta ta tashi daga kan gadon, hijab ne har kasa jikinta, hakan yasa ta bi bayan umma dake rike da hannunta suka fita parlor, balarabiyar matar na xaune parlor da jikokinta su uku sai shureim dake jikinta shi ma, Suna hada ido Khadijah ta sauke kanta a sanyaye ta karasa cikin parlorn ta xauna, da gudu shureim ya taho ya rungume ta yana kallonta yace “Anty are you sick?” Kallonsa Kawai khadijah take taji kamar ta fashe da kuka, Ummu dake ta kallonta da tausayi tace “Sannu Khadijah, ya karin hakuri?” kasa cewa komai tayi da farko, can dai tayi karfin halin bude baki da kyar tace “Alhmdlh Mumy, nagode” Ummu tace “Allah yayi masa rahama, ke kuma Allah baki dangana, ya sa mai ceto ne” Umma tace “Ameen thumma Ameen” don khadijah kasa amsawa tayi, Shureim na kallonta da damuwa yace “Anty uncle yace min sudais travelled, why will he travel alone, why didn’t we go together plss, and now I am missing him, plss I want to go to him, I promise I will never fight him again….” umma ta jawosa jikinta tana kokarin boye hawayen idonta tace “He will be back soon sweetheart, and I am sure he is missing you too” Shureim yace “Toh Umma I want to talk to him on phone, am missing him” Ummu dake ta kallon shureim tace “Shureim har ka gaji da wasa dasu fadeel, ain’t they ur frnds anymore” ya juya ya kalleta yace “Noo Ummu I like them, but sudais is my brother, they will like him also” Ummu tace “Toh taho mu wuce tunda ka gaida Anty” kallon khadijah da kanta ke kasa shureim yyi ya dawo kusa da ita a hankali yace “Anty, is sudais coming back soon? I want the both of us to be frnds with fadeel and Adeel” Ummu ta mike tace “Toh xo mu wuce Shureim, idan ya dawo xa a kawo sa wajen ka” da haka suka fita parlorn bayan shureim ya daga ma khadijah hannu, Umma ta rakasu har bakin mota, sai a sannan taga tare suke da Khaleel dake xaune motar, ganin umma ya sakko ya gaisheta da ladabi sannan ya mata gaisuwa ta amsa tana murmushi tace “Allah ya saka da alkhairi, ya bar xumunci” yace “Ameen” sai da suka shiga motar gaba daya sannan Umma ta koma cikin gida, bata tadda Khadijah a parlor ba hakan yasa ta wuce daki ta ganta kwance, mamaki ya cika umma ta xauna kusa da ita da damuwa, yanxu kuma rashin kukan nata ya fara damunta don wani lkcn gwara mutum yyi kukan da kukan xuci, Umma ta yi shiru na d’an lokaci kafin a hankali tace “Look daughter, cry… even if it’s a little so you will feel relieve, kiyi kuka don Allah bana son wannan rashin kukan naki kuma, kin dai san matsalar ki, kar kije ki tada ciwon ki, it will be worst gaskiya idan haka ya faru” Jin bata ce komai ba umma ta mike a sanyaye ta fita, ba a jima da tafiyar mahaifiyar khaleel ba su mumy suka xo gidan, yau kam sun d’an dade kafin su wuce kuma khadijah ta fito ta amshi gaisuwar saleem, da yamma shaheedah ta xo gidan da sadeeq, shaheedah tayi kuka don bata ba sudais mutuwa so early ba, duk taji tausayin khadijah sosai, su Vanessa duk suka kira khadijah yi mata gaisuwar sudais da har lkcn a xaton su kanninta ne yan biyun. Da daddare ta fito wanka Shaheedah ta mika mata wayarta da yake vibrate, karba tayi ganin Khaleel ne ta daga ta kai kunne, cikin sanyin murya yace “Khadijah…” A hankali tace “Na’am” yace “Xa ki iya fitowa yanxu?” Shiru ta d’an yi kafin tace “Toh gani nan xuwa” shiryawa tayi ta sa hijab ta fita xuwa dakin umma, ta durkusa kusa da ita tana kallonta tace “Umma ina xuwa khaleel na kirana” Umma tace “Toh sai kin dawo” daga haka ta mike ta fita, cikin sanyi take tafiyar kamar mai tausayin kasa har ta isa waje, yana tsaye ya jingina jikin motarsa, kanta a kasa ta isa gefensa ta tsaya, murya can kasa tace “Ina yini?” Kallonta kawai yake bai ce komai ba har ta dago a hankali, sai a sannan ya sauke idonsa kasa daga kallonta da yake yi, cikin sanyayyan muryarsa yace “Ya hakuri khadijah” ta hadiye abu da kyar tace “Alhmdllh” yace “Ban san me xan ce maki ba shi yasa ban kira ki ba khadijah, I know it’s very sad, it’s a great lost, but don’t forget ba wayon ki yasa Allah ya baki shi ba, and there is always a reason for everything, and you knw God plans best, don haka ki sa ma xuciyar ki dangana, you have ur handsome shureim, he will act as both him and his twin to you, this is part of ur fate, and it’s already written, plss kin san condition din ki Khadijah kar ki kara sa mutuwar sudais a ran ki I know its very painful, but idan wani abu ya same ki i will be very sad, come to think of ur only son, for my sake and his don Allah kiyi hakuri, forget about Sudais, but don’t forget to pray for him always, Allah ya hada mu gaba daya a aljanna” cike da damuwa ya kare, Khadijah tayi murmushin karfin hali tana share hawayen da ya taru idonta, tun ranan da Aliyu yace kar ta sake kuka bata kara ba sai yanxu da take gaban khaleel, a hankali tace “In sha Allah Dr, baxan sa damuwa a raina ba, ae ban ma san Allah xai bani shi ba, so baxan butulce masa ba, na hakura Allah ya haskaka kabarinsa ya sa can ya fi masa nan, kuma ya raya min d’an uwan sa” cikin rawar murya ta kare maganar, khaleel ya lumshe ido yace “Ameen Khadijah, am happy with ur words” Bata ce komai ba ta dinga kallon motar da yayi parking bayan na Khaleel, Aliyu ne ya fito cikin motar, kallo daya khaleel yayi masa ya dauke kansa, Aliyu ya iso inda suke yana kallon khaleel ya basa hannu khaleel ya amsa amma fa da kyar, Aliyu na kallon cikin idanuwansa yace “Ya hakurin mu?” Khaleel yace “Mun gode Allah” Aliyu ya kalli khadijah suka hada ido tayi saurin sunkuyar da kanta gabanta na faduwa, cikin gidan Aliyu ya shiga, khaleel na juya wristwatch din hannunsa yace “Wajen ki ya xo?” Ta girgixa kai tace “A’a” Khaleel bai sake cewa komai ba bayan wani lkci yace “Alryt then, xan koma Khadijah, Allah ba mu hakuri gaba daya, sleep without worries plss” ta gyada masa kai tana kallonsa, yana daga kai suka hada ido tayi saurin dauke kanta, yyi murmushin sa mai kyau yace “Amma kin ci abinci kuwa? Tell me the truth plss” ta girgixa masa kai a sanyaye tace “I don’t have appetite” yace “Toh idan na siyo maki abu yanxu make me the promise xa ki daure ki ci” tace “Akwai abinci fa a gida” yace “Ai na sanin, just promise me xa ki ci plsss” murmushi tayi tana fidgeting fingers dinta a hankali tace “Toh nagode” yace “Yauwa, I will be back soon” tace “Toh Allah ya kiyaye” daga haka ya xata xai shiga motarsa ita kuma ta shiga cikin gidan, xaune ta tadda Aliyu kan farar kujera a wajen compound din, kallo daya tayi masa ta dauke kai xata wuce ciki, taji a hankali yace “Iman” kasa ci gaba da tafiya tayi, maganganunsa na jiya da safe na mata yawo a kai, can ta juyo ta kallesa ta gan sa tsaye, yace “Plss just few minutes” tana ta tsayuwa idonta a kan yatsunta har ya iso gabanta yace “Few minutes pls” Ta dake da kyar tace “Toh” juyawa yayi ya nufi gun kujerun ta bi bayansa, ya xauna kan kujerar ta xauna ita ma. Kallonta kawai yake ta ki kallon sa ta hade rai, murya can kasa ta ji ya fara cewa “Iman ba dan ni ba don Allah ina son ki mance abinda ya faru tsakaninmu six years back…..” Da sauri ta dakatar da shi tace “Toh ni nace maka ban mance bane?” Ya girgixa kai a hankali yace “I mean ki yafe min ki cire a ranki da gangan na maki hakan wllh ba da gangan bane, it’s a set up, though ba lallai ki yarda da hakan ba, amma don Allah kiyi hakuri mu dinga xumunci” Ji tayi kamar ta fashe da kuka don ya fama mata ciwon da ya ki healing har yanxu a xuciyarta, A sanyaye yace “Kin ji Iman, ki raga min ko albarkacin daya yaron da ya rage a tsakaninmu even if I didn’t deserve it” Khadijah ta kasa cewa komai, Bayan wani lkci ta daga kai a hankali tana kallonsa ta ga kallonta yake, da sauri ta sauke idonta tace “Ni fa na mance, ya kuma wuce a gu na” yace “Toh nagode sosai, amma xaki bani yaron?” Da sauri ta daga kai tana kallonsa, cikin rawar murya tace “I can’t give you my son, kayi hakuri…” Yana gyada kai a hankali yace “No offense, amma xa ki bari ai mu dinga xumunci da shi, I mean in dinga xuwa ina ganinsa, once in a while kuma xa ki bari ya xo gun mumy koh” shiru tayi ta kasa cewa komai, murya can kasa yace “Kin yi shiru” a xuciyarta tace “Nasan maganin ka” a fili kuma tace “Toh” Wani murmushi yayi yace “Toh nagode sosai, Allah ya raya sa” tace “Ameen” kamar ance ta juya taga khaleel ya shigo gidan rike da leda, mikewa tayi da sauri ya karaso har gabanta yana kallonta ya mika mata ledan, ta d’an risina ta karba a hankali tace “Nagode” ya d’an yi murmushi yace “No thanks” daga haka ya juya ya nufi gate, Aliyu ya bi sa da kallo ko kiftawa babu, khadijah tace “Xan wuce ciki sai da safe” mikewa yayi yace “Toh ina yake, I mean the boy? Though ban san sunan sa ba” da kamar khadijah baxata ce komai ba sai kuma murya can kasa tace “Sunansa Muhammad, ana kiransa Shureim, sunan late half dinsa Aliyu ana kiransa Sudais” kallonta yake ko kiftawa babu, ta gyara tsayuwarta tana masa wani kallo tace “Barrister Aliyu… Sunan sa ya ci” daga haka ta juya ta fara tafiya fuskarta daure, murmushi Aliyu yyi ya bi ta da kallo, can yace “Ohk, wait Iman, nagane barrister Aliyu ne ba ni Aliyun ba” tsayawa tayi amma bata juyo ba, ya karasa inda take yace “Toh yana ina yanxu, I haven’t seen him since yesterday” tace “Yana gidansu Dr khaleel” shiru yyi bai ce komai ba, can a hankali yace “Ohk good nyt” daga haka ta juya ta wuce ciki ta rufe kofa. Washegari aka yi sadakan ukun sudais, tun da sassafe Mumy ta taho da su Siyama da frnds dinta biyu, sadakar wainan shinkafa da Kayan flour ta kawo gidan, Ummun khaleel ma ta xo da jikokinta tare da shureim wajajen karfe tara, ita ma wainar ta kawo sai lafiyayyen rice and stew da ta kawo ma khadijah da soyayyen kaji a warmer daban, Karfe sha daya Barrister sudais ya bar gidan kasancewar yana da wani case, ya tura ma khadijah text cewa xai dawo da yamma, karfe sha biyu ummun khaleel ta koma gida tare da su Shureim da yanxu ya saba da yaran sisters din khaleel amma har Ummu ta gaji da amsa tambayar da yake mata na cewa yaushe sudais xai dawo, shi dai a kai sa wajensa, tausayi yaron yake bata don tsakaninsa da Allah yake son ganin dan uwan nasa, a ko da yaushe dai ce masa take soon xai dawo, sai kusan azahar Mumy suka bar gidan, Khadijah ta raka su har gate tayi mata godiya a sanyaye, Mumy ta sa mata albarka sannan suka wuce da yaran nata, kafin dare frnds din Umma suka fara watsewa gidan, Shaheedah ma suka koma Abuja tare da Sadeeq, gidan ya rage daga Khadijah, sai Nanny da Umma da Wata aminiyarta. Bayan magrib khadijah bna xaune kan darduma tana azkar kira ya shigo wayarta, a hankali ta daga ta kai kunne ganin barrister sudais ne, yace “Amira xa ki iya fitowa yanxu plss, am outside” tace “Toh” daga haka ta mike ta fita, sai da ta fara gaya ma Umma sannan ta tafi kofar gida, fitowa yayi daga mota ganinta, yana rike da 3 years old daughter dinsa, Khadijah ta wara ido tana kallon kyakkyawar yarinyar ta xaga inda yake ta karbeta tace “Waow ya sunanta?” Sudais ya jingina da motar yace “Ur namesake, ita ma Amira ake kiranta, na kawo ta ne ta gaida Antyn ta” Khadijah tayi murmushi a sanyaye tuno kiran ta da mahaifiyar yarinyar tayi mata ranan da sudais xai rasu, tana taba dogon gashin yarinyar tace “Naji dadi sosai” Yace “Sure?” Ta kallesa da sauri tace “Eh mana, ko xaka bar min ita” yar dariya yayi yace “In dai kika shigo gidan ubanta ai taki ce ita” Wani murmushin Khadijah tayi bata dai ce komai ba, yana kallonta a hankali yace “Baxa ki shigo ba kenan, xaro ido tayi tace ” Ka ji na fada haka?” Yace “Uhmn dont forget who is standing before you” ta dauke kai tana ci gaba da murmushi tace “A barrister” ya shafa kansa yana kallonta a hankali yace “Toh ya k’arin hakurin mu dear?” Tace “Mun gode Allah” yace “Har yanxu shureim din bai dawo gida ba?” Ta gyada masa kai tace “Bai dawo ba” yace “Ohk, ya su umma?” Tace “Suna ciki” kamar warce ta tuna da sauri tace “Sorry na bar ka tsaye mu shiga ciki” yayi murmushi yace “Aa bari in yi ta tsayuwa ta” ta turo baki tace “Allah na manta ne kayi hakuri, mu shiga ciki” daga haka ta nufi gate rike da Little Amira, ya bi ta da ido kafin ya bi bayanta, kan fararen kujerun dake compound din Sudais ya xauna duk yanda tayi da shi ya shiga ya gaida umma ya ki yarda wai sai gobe, tace “Toh bari in kai mata Little Amira ta gani” yace “Toh sai ki bar ta a can ki dawo ke kadai kar in yi rashin kunya gaban daughter na” dariya kawai khadijah tayi ta tafi tare da Amira dake ta waigo Abbanta ya daga mata hannu yana murmushi. umma ta xaunar da ita kan kafarta tace “Maa sha Allah, daughter na mai kyau da ita, Allah ya albarkace ki” khadijah tace “Naga kamar bata magana” Umma tace “A’a don dai bata san mu bane amma wannan ai ta isa tayi magana” fridge khadijah ta nufa ta bude ta dau ruwa da lemo ta daura kan tray ta sa glass cup sannan tace “Umma ina xuwa” Umma tace “Toh sai kin dawo” Har khadijah ta iso gun sudais idonsa na kanta, ta ajiye karamin tray din hannunta ta bude drink din ta xuba masa sai dai bata masa ba tace “Ya aiki?” Ya langwabar da kai yace “Ba dadi, Amira har yanxu you didn’t answer my questions…” Ya lumshe ido ya bude yace “Ohk let me leave it this way, you don’t want to answer my question” shiru khadijah tayi tana kallonsa, a hankali yace “A lot of things happened after I left you and the boys Amira, na koma damaturu gidanmu tare da Mamina amma gaba daya na rasa kwanciyar hankali, i was always sad then, thinking about you and the twins, hankalin Mami ya tashi a lkcn ta dinga cewa kilan asiri kika min ko kuma aljana ce ke, gashi nan abun na affecting dina, nan tasa aka tayi min rokan Allah, gradually dai na fara kokarin ganin na mance ku, na cire ku a rai na dinga harkokin gabana… saboda ku ko da ina da aiki a Abuja to baxan je ba, gaba daya na daina xuwa Abuja, daga Lagos, kano sai Kaduna and other States nake xuwa amma banda abj, dama ni din ba wai ina da time na yan mata bane, jiddah dai ce ita ma a Holland muka hadu lkcn ina karatu ita kuma tana tare da yayarta dake kasar tare da mijin ta, I never knew ma ashe Mami ta san mum dinta sun yi makaranta daya though it’s not as if they are frnds, to dai a haka na fara neman jiddah har aka sa aurenmu ana saura few months bikin mu na hadu da ke ranan na fito daga gida, Amira saboda ke nasa aka daga bikin nan har na kusan watanni shiddah, a kwana a tashi kuma na kara neman a daga cos kin kusa haihuwa lkcn, let me make things brief, at the end fasa auren nayi gaba daya, suka maido min da lefen da na kai all because of you, and happily then Abbana supported me, but bayan rabuwar ki sai gashi na koma mata cos I don’t have any option again, at first kamar baxata yarda ba daga karshe dai a cikin wata daya aka daura mana aure, 2 years da aurenmu da jiddah Allah yayi ma Mamina rasuwa bayan tayi fama da kidney problem, though before then duk na mata bayanin yanda aka yi na hadu dake, ban boye mata komai ba, kuma hankalinta ya tashi a lkcn but kawai sai ta maki fatan Allah ya hada ki da dangin mahaifiyar ki, daga nan kuma bata ce min komai ba, and gaskiya a lkcn kusan na ma cire ku a rai na daina damuwa cox I knw surely Allah na tare da ku, amma kullum sai na maku addu’a every blessed day, ba tonan asiri ba Amira ni ba wani jin dadin aure nake da jiddah ba, fitinar ta yayi yawa she is always pestering my life, ko kadan bana son hayaniya yana daga min hankali, bani da rest of mind idan ina gidana, ko irin weekend din nan ma ni na gwammace in tafi office in yi kallo, Amira I need a woman that i will find peace in, I need a better life partner, ina raga ma jiddah ne kawai saboda yarinyar nan dake tsakaninmu, and divorce is totally out if it baya cikin tsarin rayuwata, I need you plss Amira” Khadijah taji kanta ya mata nauyi sosai ta rasa abinda xata ce masa, bata san lkcn da hawaye ya dinga sakko mata ba tana kallonsa, deep down her kuma ta rasa me yasa khaleel ya fado mata.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103Next page

Leave a Reply

Back to top button