RAUDHA 1-END

RAUDHA Page 1 to 10

Sai kawai gaba ɗaya mutanen wajen suka sanyo mata idanu suna kallon haɗaɗɗen yarinyan me cike da ban sha’awa a idanun duk me kallo, yarinya ƴar hutu da ji da kai

RAUDHA sai faman ɓata fuska take yi tatako zuwa wajen Ramcy tana ɗan lumshe idanun ta

Sai da Ramcy tariƙe hannun ta kafin suka nufo gidan

Ba maza ba har matan sakin baki da hanci kawai suka yi suna kallon ikon Allah, kuma akasarin su kallon arniya kawai suke mata sabida shigan dake jikin ta

Sai da suka zo gab shiga gidan ne, Amarya da har da ita ake kallon sannan ne tagane Ramcy ce ƴar uwanta, sai tadaka tsalle tanufo ta tana faɗin

“Rahma ke ce ashe?”

Ramcy da itama sai yanzu idanun ta suka kai kan Amarya Shatu sai tawashe baki tana sakin hannun RAUDHA suka rungume juna cike da farin ciki

“Wlh ban gane ki ba sai yanzu ashe kece?” Cewar Shatu bayan ta ɗago kanta tana kallon ta da murmushi a face ɗin ta

Duk ƴan matan sai suka nufo wajen su don ba ma idanun su abinci wajen kyakkyawar matashiyar nan me kama da ƴan ƙetare

“Ni ce wlh kin gammu sai yanzu”.

Murmushi Shatu tayi tana kallon RAUDHA dake tsaye tana bin mutanen wajen da kallo sai kace taga abun ƙyama, sai faman yamutsa fuska take yi

“Wannan kuma daga ina sarkin jajibe-jajibe?”

Sai da Ramcy takalli RAUDHA kafin tamayar da idanun ta kan Shatu da tayi maganar tace “mu shiga ciki mana ko anan ne zaki tarbe mu?”.

Dariya Shatu tayi tana kallon sauran ƴan matan wajen tace “ku jira Ni yanzu zan dawo”.

Gyaɗa mata kai kawai sukayi domin har yanzu sun kasa magana tunda sun samu abincin kallo

Riƙo hannun RAUDHA Ramcy tasake yi suka bi bayan Shatu da tayi gaba abinta

Dama tuni mutanen wajen sun soma gulma suna raɗe-raɗin ita kuma wancan wacece? Sai dai babu me basu amsa haka suka ci gaba da gulman su, yayinda ƙawayen amarya kuma suke jiran tadawo tabasu amsa

Suna shiga cikin gidan matan dake faman aiki suka sanyo musu idanu

Ramcy bata kalli kowa ba bare tagaishe su don tasan basu gane ta ba, haka tabi bayan Shatu har ɗakin Maman su, suna shiga babu kowa sai Maman Shatu ɗin tare da wata dattijuwa

Idanu suka sanyo musu cike da mamaki

Maman Shatu tace “ke Shatu wannan kuma daga ina?” Tayi maganar tana nuna RAUDHA da tatsaya ƙeƙam abakin ƙofa

“Mama baki gane ta bane? Rahma ce da baƙuwar ta”.

Sai Maman da Dattijuwar suka mayar da idanun su kan Ramcy da har ta zauna ma

“Ƴar ƙwal uba kece da wannan shigan banzan Ramatu?” Cewar Dattijuwar tana kai hannun ta jikin Ramcy taɗaga mata duka

Matsawa gefe Ramcy tayi tana dariya tace “ƴar tsohuwa me ran ƙarfe har dake a bikin nan?”

Mama tace “Rahma wacece wannan wai da kika zo mana da ita me kama da ingozi?”

Ɓata fuska Ramcy tayi tace “wai menene haka don Allah ƙawata ce fa muka zo da ita biki”.

Gaba ɗaya sai suka kama baki har Shatu suna sake maida idanun su kan RAUDHA dake tsaye har yanzu, sai dai yanzu sosai ta ɓata fuskarta tana sake sakar musu lumsassun idanun ta, kafin kuma tajuya tafice abinta

“Kun gani ko don Allah menene ruwan ku da ita? haka ake amsan baƙuwa?” Cewar Ramcy tana miƙe wa tsaye dasauri tafita

Sai suka juyo da kallon ga junan su

Shatu tace “cabb ɗi wai har yanzu Rahma bata dena halin ta ba? Ni nasan wlh daga shige-shigen ta ne ta samo wannan arniyan, wai ƙawancen ma har da arniya”.

Sai taja tsaki tana nufan ƙofa batare da tabi takan Mama da tsohuwa dake surutu ba

A zaure Ramcy ta cinma RAUDHA tayi saurin riƙo ta

A fusace RAUDHA tajiyo tana kallon Ramcy da shanyayyun idanun ta tace “meye kika riƙe Ni?”

Cikin lallami Ramcy tace “don Allah kiyi haƙuri Besty basu san ko ke wacece bane, amma zanyi musu bayani yanzu kin ji?”

Gajeren tsaki RAUDHA taja batare da tace uffan ba

Roƙon ta Ramcy taci gaba da yi daƙyar tasauka, amma da sharaɗin baza ta kwana anan ba sai dai su tafi Hotel

Gyaɗa mata kai kawai Ramcy tayi cike da son kwantar mata da hankali

Shatu ce tafito itama tagan su anan tsaye, sai kawai tasaki murmushi tace

“Yanzu party zamu je Rahma, ki taho muje tunda ga motoci sun zo”.

Murmushi Ramcy tayi tace “to zamu zo daga baya, aina ake yi?”.

Faɗa mata address ɗin wajen tayi kafin tafice abinta

Riƙo hannun ta tayi zasu koma ciki amma RAUDHA tatirje alamun baza ta je ba, sai ita Ramcy ɗin ne takoma ciki don sanar musu da tafiyan ta

Tana shiga ɗakin taga mutanen wajen duk sun shiga ciki suna tambayan yarinyan da tafita

Anan ne ma suke sanin ashe Ramcy ce ɗayar

Tana shigowa duk suka yi mata caa aka suna faɗin “shine zata wuce su bata gaishe su ba?” Ita dai haƙuri tabasu kafin tayi ma Mama ƙarya akan zasu wuce wajen party amma ba lallai tadawo nan ba sai gobe, zasu sauka gidan yarinyan da suke tare da ita (tana nufin RAUDHA)

Bata jira ma abinda zasu ce ba tafito tasami RAUDHA tariƙe mata hannu suka fito cikin gidan

Yawancin mutanen wajen duk sun shige cikin mota, ko kallon sauran mutanen da suka banko musu ido basu yi ba suka shiga cikin motan RAUDHA taja suka bar wajen.

            ????????????

Suna isa ɗan ƙaramin Hotel ɗin me ban sha’awa suka fito suka shiga ciki

Ramcy ce tayi musu booking ɗakin da zasu zauna, sai da tagama komi sannan suka nufi inda jerin ɗakunan suke, a upstairs ɗakin nasu yake

Bayan tabuɗe suka shiga

Direct Kan gadon RAUDHA tanufa tafaɗa tana ajiyan zuciya, lumshe idanun ta tayi tana jin zuciyarta babu daɗi, sosai ranta yasosu da yanda mutanen suke kiran ta da arniya

Zuwa Ramcy tayi tazauna gefen ta, shiru tayi naɗan wani lokaci kafin tace “Besty ko zamu je wajen partyn ne?”

Shiru babu amsa

Sai da tasake maimaita mata sannan ne RAUDHA tabuɗe idanun ta cike da ɓacin rai tace “Ni baza Ni ba”.

“Plz Besty kin San bazan iya tafiya in barki anan ba, sannan idan banje ba Shatu zata ji haushi tunda nazo mata biki ne kiyi haƙuri da abinda akayi miki, hakan bazai sake faruwa ba”.

Gajeren tsaki RAUDHA taja tana miƙe wa zaune taja jakan ta dake hannun Ramcy ɗin, taciro ƙwayoyin ta ta’afa a bakin ta don jin kanta ya soma ciwo sakamakon hayaniyan mutane

Can kamar baza ta sake cewa komi ba sai kuma tatashi tana ajiye Facing Cap ɗin ta saman gadon takalli Ramcy tace “tashi muje”.

Dasauri Ramcy tatashi tana murmusawa suka nufi ƙofa suka fice, Ramcy ɗin tarufe ƙofan suka sauka ƙasa, inda suka ajiye motan su suka nufa suka shiga RAUDHA tafiga motan suka bar haraban wajen.

[11/16/2020, 10:49 AM] نفيسة أم طاهرة: ????????????????????????????????????????

????????????????????

????????????????????

  *RAUDHA*

????????????????????

????????????????????

????????????????????????????????????????

*MALLAKAR*✍️

              _Nafisat Isma’il Lawal Goma_

*بسم الله الرحمن الرحيم*

 

*FEENAH WRITER’S ASSO????*

“`®Ɗaya tamkar da Dubu????✓“`

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*????

         *F.W.A????/*

.

  *NOT EDITED* ___________________________????

        *SEASON TWELVE*

_______????A Hotel ???? ɗin da su Shatu suke yin party RAUDHA tatsaya, ɗan ƙaramin hotel ne me kyau da tsada, gaba ɗaya haraban wajen motoci ne manya-manya jibge, da gani kasan harkan da manyan mutane ake yi

Dama shi Mijin Shatu ɗin me kuɗi ne, don haka abokan sa duk yaran masu hannu da shuni ne kuma duk sun hallara wajen, partyn dama daga Ƴan mata sai samari ne

Fitowa suka yi cikin motan suka nufi ciki

Tunda suka doso bakin wajen Cool music ɗin da aka saka yaratsa kunnuwan RAUDHA, sosai taji wani sanyi da nishaɗi ya ziyarce ta duk da kuwa bata cikin Mood ɗin ta

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button