RAUDHA 1-END

RAUDHA Page 1 to 10

.

_More Comments more post._

[11/13/2020, 3:00 PM] نفيسة أم طاهرة: ????????????????????????????????????????

????????????????????

????????????????????

  *RAUDHA*

????????????????????

????????????????????

????????????????????????????????????????

*MALLAKAR*✍️

              _Nafisat Isma’il Lawal Goma_

*بسم الله الرحمن الرحيم*

 

*FEENAH WRITER’S ASSO????*

“`®Ɗaya tamkar da Dubu????✓“`

*JIKAR LAWALI CE*✍️ ~What’sapp Number 07065334256~

*Wattpad: UmmuDahirah*????

         *F.W.A????/*

.

  *NOT EDITED* ___________________________????

        *SEASON FOUR*

_______????Ƙarfe 90:30pm. Na dare RAUDHA tagama shirin ta cikin ƙananan kaya kamar yanda tasaba, Black Jeans da yellow ɗin riga me hannun vest tasaka, gaban rigan anyi zanen heart❤️ da stune masu ƙyalƙyali, sai tagyara gashinta tasaka Ribom baƙi tafeshe jikin ta da turare masu ƙamshi da ɗaukan hankali, Hill shoes tasaka me igiya shima baƙi sannan taɗau Wizy back ɗin ta da car keeys tafice, tana shiga motan tabata wuta tayi bakin Gate, nan da nan Gate man yawangale mata ƙofa tafice

Cikin tuƙin ta na ganganci ta’isa ƙofar gidan su Ramcy acikin ɗan mintunan da basu gaza 8 ba, tana tsai da motan tasoma danna hon kamar zata tashi garin sabida ƙara, da gudu Ramcy tafito tashige motan taja sukayi gaba, yau kam sun ɗan taɓa hira ba kamar ko yaushe ba, don ita RAUDHA ba kasafai tafiye son surutu ba

Suna isa Club ɗin da suka saba zuwa suka fito sukayi ciki, dama ɗabi’ar RAUDHA kenan duk idan tazo club sai ta tiƙa rawa son ranta sannan ne zata nemi wajen zama, haka ma takasance yau tana shiga tafaɗa cikin masu rawa tasoma girgiza jiki, rawa take yi na ban sha’awa da burgewa, sosai taƙware a rawa wanda ko gasan rawan akaje ita zata cinye, ko wani irin waƙa irin rawan sa take yi

Acan gefe kuwa wani matashin saurayi ne zaune yana faman kurɓan Whiskey Yana kallon ta, murmushi kawai yake zubawa sabida tsananin burgeshin da tayi, har yana tunanin yanda zai je wajen  yarinyan tashigo hannun sa, yana nan zaune yana faman kallon ta har yagama kurɓe na cikin Cup ɗin hannun sa kafin yatashi yadoshi wajen, babu zato babu tsammani RAUDHA tana cikin tiƙan rawan ta tana ihun murna taji hannu a kwankwason ta abinda be taɓa faruwa da ita ba, dasauri tajuyo tana kallon saurayin dake gabanta yana faman doka mata murmushi, kafin tasake wani motsi ya riƙo mata hannaye yana faɗin

“Wow Babe you look so cute, kin matuƙar burge Ni fa”.

Saurin janye hannun  ta tayi tana me buga masa wani banzan kallo batare da tace uffan ba taci gaba da rawan ta, shi kuma memakon yaƙyale ta sai zuwa yayi yasake riƙo ta tare da janyo ta jikin sa gaba ɗaya yana cewa

“Common Baby muyi tare mana”.

Wannan karon ma ƙwace jikin ta tayi but batayi wata-wata ba tatsinka masa mari, dasauri yariƙe kuncin sa yana kallon ta da tsananin mamaki, ita ma ɗin kallon sa take yi da kyawawan idanuwan ta fuskarta aɗaure, kaɗa masa hannu kawai tayi alaman gargaɗi sannan taci gaba da rawan ta batare da tasake bi takan sa ba, shi kuwa cikin haushi yake kallon mutanen wajen duk da basu lura da abinda ke faruwa ba, azuciye yanufe ta yadanƙo gashin ta zai wanka mata mari Abokin sa da yake ganin komi yayi saurin damƙe hannun, kallon abokin nasa yayi shi kuma yagirgiza masa kai alamun kar ya’aikata, ita kuwa RAUDHA zafin riƙe mata kan da yayi ne yasanya ta sake taska masa mari cike da tsananin jin haushi

“Whattt..” yafaɗa da ƙarfi idanuwan sa kamar zasu faɗo ƙasa yana ƙoƙarin fizge hannun sa cikin tsawa yace

“Please Deeni kasake Ni in kakkarya yarinyan nan kana ganin abinda tayi min”.

Wanda aka kira da Deeni sake riƙe sa ƙam yayi yana basa haƙuri har alokacin kuma ya ƙi sakar mata gashi, RAUDHA kuwa azaba ya ishe ta sabida yanda yake ƙara jan mata, tayi saurin saka hannu tana son fizge gashin ta but ta kasa

sai alokacin su Ramcy dake zaune can nesa suka soma lura da abinda ke faruwa, dasauri tataho ganin da RAUDHA ake yi, itama tana zuwa tasoma janye gashin RAUDHAN amma duk sun kasa ƙwacewa, da yawa mutanen wajen duk sun taru a wajen ana basa haƙuri bcoz yawancin su sun san ita ƴar wanene, wannan dalilin ne yasaka ma babu wanda ke kula su idan sun zo suke cin karen su babu babbaka

Jawad fa yaƙi sakin gashin RAUDHA adole sai ya rama marin da tayi masa, sai fitina yake yi yana son ƙwace ɗayan hannun sa da Deeni yariƙe

Cikin tsananin ƙulewa RAUDHA tace “dan ubanka kasakar min gashina idan ba uwarka tashuka min ba”.

Har wani rawa jikin Jawad yake yi sabida tsananin ɓacin rai da irin zagin da tayi masa, wani irin ƙarfi da yazo masa take yahankaɗe Deeni yafuzgo ta yasoma naushin ta, nan da nan matasan wurin suka rufar masa suka riƙe sa ana son ƙwace RAUDHA, a time ɗin har ya farfasa mata hanci da baki sai zuban jini suke yi, hakan ya ɗaga ma RAUDHA hankali sosai tafashe da kuka tana jin wani baƙin ciki na turnuƙe ta, daƙyar aka ƙwace ta a hannun sa Ramcy tayi saurin riƙe ta tana duba inda yafasa mata duk hankalin ta atashe, furzo da jinin bakin ta RAUDHA tayi tana ɗago shanyayyun idanuwan ta da suka gama rinewa sabida tsaban wahala tana kallon Jawad wanda ake ta faman riƙe wa har yanzu be huce ba, bata iya cewa komi ba illa fizge jikin ta da tayi daga riƙon da Ramcy tayi mata tabi hanyan fita da mugun gudu tafice, motan ta tashige ko jiran Ramcy batayi ba tabata wuta tabar haraban Club ɗin, sosai take gudu akan kwalta kamar zata tashi sama sabida tsaban baƙin ciki, tana yi tana share jinin dake zuban mata da bayan hannu, Allah ne kawai yakaita gida da babu abinda zai saka batayi hatsari ba, tana zuwa bakin Gate ɗin tabugi Gate ɗin da motan kamar mara hankali, hon take dannawa akai-akai ɗaya kan ɗaya

shi kuwa Gateman sosai yatsorata da yanda aka bugi Gate ɗin, Bama shi kaɗai ba har ta sauran masu aikin gidan sai da sukayo wajen da gudu don suga meke faruwa, dasauri me gadin yabuɗe ƙaramin ƙofa yana leƙawa don be yi tunanin RAUDHA bace tunda bata taɓa yin hakan ba, ganin motan ta yayi saurin komawa yaja mata gate ɗin, ba don Allah ya tsare sa ba da tuni tataka kansa ta wuce sai yayi wuf yakauce, haka sauran masu aikin ma suka dare da mugun gudu ganin yanda tayi kansu suka bata hanya, ko kashe motan batayi ba bare tayi parcking me kyau tafito tanufi cikin gidan da gudu, Direct ɗakinta tashige tafaɗa kan gado tana kuka, sosai ranta yaɓaci har wani ɗaci-ɗaci take ji a maƙoshinta sabida mugun ɓacin rai, wani irin ƙara tasaki tana miƙewa tasoma wargaza duk abinda ke ɗakin tana yi tana ihu, abunka da taɓararriya abun kuka baya mata kaɗan

Saude da Larai da suka fito daga ɗakin su sukayi cirko-cirko a parlour suna kallon saman suna me jiyo ihun da RAUDHA take yi

Saude tace “yau fa an taɓo Hajiyan mu Allah yasa dai lafiya?”

“Hmm bana tunanin lafiya gaskiya, Yakamata muje mu dubo ta”. Cewar Larai tana kallon Saude

Ita kuma zaro idanu waje tayi tace “ke ki rufa mana asiri, muje tahuce akan mu kenan ko? Kinga gwara mu lallaɓa mukoma ciki muyi gumm hakan shi zai fi mana alkhairi don wlh yau ba ƙalau take ba yarinyan nan”.

Larai tace “maganar ki dutse fa, Ni fa har na soma barci ƙarar buga gate ɗin da tayi yatashe Ni, wlh na tsorata nayi tunanin ɓarayi ne”.

Dariya Saude tasheƙe dashi tana cewa “kai Larai kin cika tsoro wlh”.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button