INAYAH COMPLETE HAUSA NOVELINAYAH COMPLETE HAUSA NOVEL

INAYAH 1-10

Wani qaqqarfan Nishi ne yafara zuwar Mata Idanuwanta sukai jajir gumin na sake jiqota tako Ina…

Cikin dauriya da azaba tafara Addua sbd sanin adduar mace Mai naquda karbabbiyace inshallah.

“Ya Allah kaine masanin gaskiyata nida abinda zan Haifa,

Ya Allah ka albarki rayuwarsa ko rayuwarta Idan mace ce,

Allah ka tallafi rayuwar abinda zan Haifa ka datar dashi kyakkawar rayuwar kwanciyar hankali da nutsuwa.

Mahaifiyarta da ‘danta Abdul take kokarin yiwa Addua Amma Ina mamar kawai tasamu damar rokarwa Allah sauki jariri ya kunno Kai Kuma adaidai lokacin mama Allah yabata ikon riqe hannunta kyau Dan sassauta Mata radadin datake ciki na kutsowar ‘da ya fito ta jikinka.

Gabaki daya jaririn ya fado tareda sake lafiyayyan kukan jarirai ba kakkautawa.

Wani irin numfashi take saukewa da a wahalce tana Kai hannu inda jaririn yake ta dauko ta Dora jikinta.

Daqyar ta bude idonta dakyau ta Dan daga kafar jaririn taga ‘ya mace ce
Take wasu hawayen suka gangaro Mata masu dumi,

Duk da hakan ta godewa Allah daya Bata abinda ta haifar Amma taso namijine sbd zaifi samun qwarin zuciyar fuskantar zunde da qalubalan maganar da zaa ringa binsa dasu na Kalmar ‘da Mara uba.

Kukan jaririyar ne ya karade gida tako Ina
A gigice Inna ta taso ta fado dakin tana Kiran sunan hadiza.

Da mamaki da tausayi take kallon hadizar tana cewa”

Hadiza ke kadai Kika haihu acikin wannan halin?

Komawa tayi da hanzari ta dauko sabuwar Reza a dakinta tazo ta yanke cibin jaririyar tana kallon fuskar Yar da fitilar hannunta.

Bata iya cewa komaiba sbd batasan Mai zata fada ba,
Rayuwarsu cikin Rana daya Allah ya juya musu akalarta inda yaso dan haka take fatar Allah yabasu ikon cinye Wannan jarabawar.

Ruwan zafi ta Dora acikin tsakar dare tazo ta karba karba Yar ta wanke tas
Ta juyewa hadizar sauran ruwan itama ta lallaba taje tayo wanka tadawo.

Sauran tafasasshen ruwan hadiza ta karba Tasha sosai sbd babu abinci babu komai.

Komawa sukayi suka zauna jigum jigum babu Mai cewa qala.

Hadizar zaune take bakin shimfidar mama Idanuwanta dake kumbure ta zubawa jaririyar tana kallo duk da acikin duhune Bata ganin komai.

Hannu mahaifiyarta taji akan kafadarta
Ta juyo ahankali idanuwanta na Mata nauyi da radadi ta kalla maman cikin duhu ta bude Baki jikinta matuqar sanyaye muryarta a shaqe tace”

Mama ‘ya mace ce na Haifa.

Wani sanyayyan numfashin da Baya fita sosai maman tasaki tareda janye hannunta kan hadizar ta bude Baki daqyar cikin yanayi na majinyaci Mai tsananin Jin jiki ta Kira sunan Hadizar.

MAMUH

ZAFAFABIYAR

LOVE

ROMANCE

INAYA A MAJEED

AYSHATOUH

[10/13, 11:57 AM] +234 703 121 9749: INAYAH
Mamuhgee
Arewabooks@Mamuhgee

5
Daqyar ta iya furta

“Hadiza Allah zai zama gatanki,
Allah zai raya Miki ‘yarki cikin Aminci inshallah.

Allah ya Raya zuriarki ya sanyawa zuriarki albarka kinji¿

Hakama halima ki kula da ita tamkar uwar data dauki cikinki ta haifeki sbd dagani harku har abada bamuda abinda zamu saka Mata dashi akan halacci da kaunarta garemu,
Batada kowa saiku ku sauke nauyin uwa mahaifiya akanta kinji hadiza.

kasa kuka tayi sbd yanda zuciyarta taso tsayawa cak daga bugawa da sanyin kalaman mahaifiyarta,

Tunda mutuwa ta dauki mijinta Bata taba samun kyakkawar kalamiba daya taba zuciyarta sai yau da mahaifiyarta ta furta matasu adaidai lokacinda duniya da kowa ya juya Mata baya ana gudunta akan abinda daya sameta.

Cikin rawar murya dake son bayyanarda kukan dake kokarin yiwa kansa iso tace”

Mama kin yarda da bazan taba aikata abinda ake zargina dashiba???

Mamar Bata iya mgna ba saidai gyara kanta tayi ahankali tana rufe Idanuwanta dake lumshewa da kansu…

Kalmar shahada take kokarin furtawa a kakkarye
Hadizar naji ta tabbatarwa da kanta rasuwa mamar zatayi
Cikin sanyi da qarfin zuciya ta Bata sauran Kalmar shahadar
Cikin saa maman ta karba ta qarasa daqyar sbd Rai dayazo gangar fita.

Wata masifar a rayuwa fin karfin wata masifar take,

Idanuwanta da zuciyarta ne suka bushe Mata alokaci daya
Saidai wani irin gagarumin nauyi daya tokale zuciyarta ya tsaya a maqoshinta.

Hannnunta na cikin na mahaifiyarta ta cika,
Rintse idanuwanta tayi ahankali tana Jin nauyin Kirjin nata na tsananta
Ta miqe tsaye ahankali tareda aje jaririyarta a gefe ta matsa gurin inna dake qudundune gefe tana Nishin azababben zazzabi takai hannu ta tada ita tareda Kiran sunanta ahankali cikin sanyi tace”

Inna ki tashi Allah ya karbi ran mama…

Wani mugun yunquri Inna tayi tana tashi zaune idanuwanta a waje ta kalli inda mamar take tana qara hasken fitilarta tace”

Aishatu ta rasu kikace hadiza?

Yanzu nabarta akwance fa tana numfashi.

Miqewa tsaye tayi ta nufi maman hankali tashe tana cewa”

Ya akai kikasan ta rasu ne tunda ba ganewa zakiyiba.

Gaban gawar maman ta tsaya tana Kiran sunanta muryarta na rawa cikin firgici.

Data tabbatarda Aishatun ta rasu ficewa tayi daga dakin ta zauna tsakar gida tana rusa wani irin kuka Mai rauni.

Tun tanada shekara goma Sha uku Malam ya aurota daga qauyensu kasancewarta marainiya itada qanwarta Indo yazo ya kawosu Mama lokacin itama batafi shekara goma Sha biyarba ya hadasu suka zauna lafiya harya aurar da Indo itama.

Lafiya kalau sukai rayuwa da mama tamkar yaya da qanwa haka suka zauna harsukai wayo mamar ta hayayyafa su kabiru har manyanci da tsufa yakamasu suna zaune lafiya,

Basu qara kaunar juna na mutunta junaba saida malam ya rasu ya barsu
Ita Inna Batada kowa sai mama da ‘yayan mamar da itace tayi renon kowannensu harya girma.

Yau aishatu ta tafi tabarta da tsananin kewa da kadaici adaidai lokacinda ‘yayanta suke tsaka da rikicin da zai rabasu har abada Idan ba Allah ne ya kawo dauki ba.

Koda aka fito sallar asuba tuni su Yaya Umar da malam kabiru suka iso sbd Inna ta buga musu da ‘yar qaramar wayarsu da hadiza ta siya musu tun kafin zuwanta Lagos wadda da ita take waya dasu.

Hadiza na zaune gefe cikin dakin da jaririyarta a dunqule suka shigo babu Wanda ya kalla inda take sukaiwa gawar mahaifiyarsu Addua suka fice Dan fara shirye shiryen jana’izarta da sauransu.

Jaririyarta data Kira da sunan AYSHATUH daidai bayan rasuwar mahaifiyarta sai baccinta takeyi sanyeda kayan sanyi farare tas data zakulo daga kayanta data Bari Nan gida tun kafin tafiyarta,
Kayan tun na Abdul ne Dan haka sun Mata yawa sosai amma tunda babu wani kayan haka ta Sanya Mata su.

Jamaar anguwa da koina sunji labarin rasuwar Mama Dan haka mutane sukaita shigowa cikeda alhini.

Tana dakin itadai Bata fitoba da jaririyarta sbd mutane zasu iya zunde duk da rasuwar da akai mata tasani

Dan haka ta kame kanta a daki Bata fitoba har akaiwa mamar wanka da sitira ta matso tayi Mata Addua aka
Dauketa aka tafi da ita.

Duk yanda taso kuka takasa zuciyarta ta bushe ta kafe da tsagwaron qunci da baqin ciki.

Saida Yan gaisuwa suka rage tana daki tafito taje tayi wanka da tafasasshen ruwan da Inna ta Dora Mata tana gurin wankan jaririyarta tayita kuka
Nan take Yan zaman gaisuwar suka fara yi da ita.

Haka tafito bandaki Takoma daki Bata Kuma fitowaba,
Wankanba itace tayiwa jaririyar da kanta sbd inna na cikin Yan gaisuwa.

Har dare Bata fitoba tana daki
Saidai taci abinci data fidda kudi tabawa innar aka siyo musu sukaci da daddare.

Washe gari take anguwa da jamaa suka dauka cewar haihuwar cikin shegen datai shine ya kashe mama da baqin ciki
Dan haka Take masifar gidan takuma tashi da daddare harta kwanta su malam kabiru suka shiga shida Yaya Umar sukace wlh saita bar gidan da ‘yarta bazata rena ‘yar datai sanadin mutuwar mahaifiyarsuba adakin mahaifiyar tasu.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button