INAYAH COMPLETE HAUSA NOVELINAYAH COMPLETE HAUSA NOVEL

INAYAH 1-10

Tunda mama ta rasu zuciyarta ta kafe Dan haka ta tashi ta hau tattara kayanta.

Kallonta Inna tayi tana cewa

“Ina Zaki ki barni hadiza?

Wasu siraren hawayen tsananin tausayin Inna ne suka gangaro Mata.

Inna abar tausayice tako Ina sbd barinta tamkar watsar da itane ga duniya Dan kuwa su Yaya Umar Basu tallafi mahaifiyarsu data kawosu duniyaba tanada Rai tayaya zasu iya tallafar rayuwar Inna da batada kowa batada komai…

To Amma ya zatai tunda ankoreta ita kanta,
Kuma ita kanta zataso tafiyar sbd yanda ake zundenta da qyamatarta da yarta tareda jifanta da alkaba’i daban daban akan itace tayi sanadin mutuwar mahaifiyarta.

Tana kuka ta tattara kayanta tabar gidan cikeda baqin ciki da quncin Rashin ganinta Abdul daya koma hannun hajiyarsu Salisu sbd jinyar da mama keyi Inna Batada lokacin kulawa dashi.

Inna kam itama kukanta daukewa yayi bayan tafiyar hadizar da sunaji suna gani su malam Umar ana gaman zaman gaisuwa ya Roshe dakin mama ya hade da wanda yafara ginawa cikin gidan ya fake da sunan zai kawowa Inna abokiyar zamane sbd kadaici.

Barin Hadiza gida ya rusa rayuwar Inna da ita kanta hadizar wadda batasan Ina ta nufaba.
ALLAH YA ZAMA GATAN MARAYA A DUK INDA YAKE..AMIN


March 2002
7:26am

Kokarin saka Mata pink safa a qananun qafafunta yakeyi Yana dan sake waiwayawa yana kallon wajen dakin nasu dan duba yanayin garin dakeda hadari sosai Wanda tun bayan sallar asuba yaketa haduwa.

Ganin yanda duk tabi ta lafe masa tamkar Mara lfy yasashi dagowa ya kalli kyakkawar qaramar fuskarta dake kallonsa da idanuwanta dako yaushe zai kaita makarantar raino sai tayi wannna qyuyar wadda tun batai wayo hakaba takeda ita.

Batasan kowaba bayan mahaifin nata da a duniya batada kowa bayanshi Kuma Bata yarda da kowa sai shi din  sai uwar renonta yagana wadda take kira da Ummey.

Cikin idanuwanta dasuka Dan Yi Kaman zatai hawaye ya kalla ya saki ajiyar zuciya ahankali Yana janyota jikinsa cikin lallausan muryarsa me zallan nutsuwa ya furta

“INAYA..

Hawayene suka fara gangaro Mata ta girgiza kai ahankali cikin Rashin budewar harshenta sosai tace”

ABBI…

cikin kulawa ya hanata fadar abinda yasan rigimace kawai zatayi sbd batason zuwa
Kuma ya saba da hakan tunda yafara kaita kullum saitai masa wannna rigimar.

Share Mata hawayenta yayi tareda miqewa tsaye ya dauki Yar jakar takardar dayake saka Mata robar ruwan pure daya dayake juye Mata a empty robar Coke sai fanke da kosan matar kofar gidansu daake soyawa na siyarwa.

Daukarta yayi ya riqe jakar a dayan hannunsa suka fito ya janyo kofar dakin tareda Sanya padlock dinsa ya rufe kofar dakin nasa ya juya ya nufi hanyar kofar ficewa.

Dukkanin jamaar gidan hayar dasuke gidan kusan kowa yafito Yana hada hadarsa a qatoton tsakar.

Da damarsu dasukaci karo da fitowarsa da mugun kallo suka bisa
Wasu Kuma dai tabe Baki sukai suka dauke Kai Suma.

Maman habiba ce dai da Bata gajiya da cusa kai tana ganinsa ta taso tana washe baki da cewa”

Aa su INAYAN Abbinta ce anfito zaa tafi makaranta?
Zo mu gaisa kinji?

Hannu ta miqa Dan karbanta
Inayar ta sake maqalewa Mahaifinta tana lafewa tareda rintse ido batamason kallon maman habiba din.

Yar dariya tasake tana cewa

“Inaya haryanzu dai qyuya ko?
To adawo lfy.

Amin kawai ya iya bude bakinsa ya furta ahankali kafin ya ra6a maman habiban ya wuce tana bin bayansa da kallo.

Mijintane ya qaraso ta bayanta Yana kallon Wanda takebin da kallo yace”

Zuwaira bazaki daina shiga sha’anin Wannan Mai shegen girman kan da miskilanciba ko?
Sam Dan iskan yaro a naqushe cikin talauci Amma baya ganin girman kowa
Baya daraja kowa
a duniyarsa babu abinda yasani sai wannan aljanar ‘yar tasa Mai kama da   ‘yar Rake,

Kullum Yana tafe Yana kame kansa Kaman dan kwalisar daya sauko daga jirgi.,
Ke Kuma sai naci da shishigi kike masa akan yabaki renon Yar tasa kina samun ‘yan kudin da yagana ke samu gurinsa.

Juyowa tayi tana fuskantar mijin nata tace”

Baban habiba laifine Dan na nace masa akan yaban renon Nima naringa samun Yan qananun canjin da yagana ke samu?
Inace Idan nasamu kudin Kai zan rufawa asiri na ringa Dan samun ciyar da yarana tunda Kai zuciyarka ta jima da mutuwa bazaka iya fita kayi ko aikin wahalar dashi yakeyi Dan ya kula da ‘yarsa kasamoba…

Cikin masifa Yana jefanta da mugun kallo yace”

Idan zuciyata mutuwa tayi ke taki konewa tayi ko?
Sbd Naga alamar son abin duniyarki Neman yake ya rufe Miki ido yaro Dan qarami Wanda kikai qani dashi Zaki zauna Yana wulaqantaki tunda ko kallonki bantaba ganin yayiba duk wannna shishigin da kike masa akan ‘yarsa dako qafarta baya barin ta taka tsakar gidan Nan Kamar akansa aka fara haihuwa
mu duka ‘yayanmu ba ‘Yaya bane sai tasa ‘yar ce kawai ‘ya,

Yasan Yana tsananin jinta kamar ransa ubanwa yace ya rabu da uwarta?

Cikin takaici maman habiba tace

“Ina ruwanka da Idan sakin uwarta yayi idanma mutuwa tayi,meye naka?

Bbn habiba ka fita fa idona na rufe kabarni nasamu nacusa kaina a gurin nasa nasamu abinda nakeso.

Inaya dai inshallah sai ka ganni Ina renonta
Ina laifin dari Biyar duk sati?wlh zanyi kokari nasamu tunda Kai din ba nemowa kakeyiba sai shegen gulma da sa ido.

Qaramin tsaki ta sake tana juyawa ta wucewarta tabarsa tsaye Yana binta da hararar mugun rainin datai masa Bata kunyar fada masa magana kowace iri tunda taga ita ke nomowa ta ciyar dashi.

Suna fitowa gida Kai tsaye hanyar titi ya nufa Bai Kuma sauketaba har lokacin sbd karta Bata qafafunta da takarminta da daudar hanya tunda lokacin damuna ne.
Barema koba lokacin damuna bane baya ajeta koyaushe daukarta yakeyi daga cikin gida har inda yake kaita,
Bai cika barin ta fitoba tayi tafiyaba koyaushe daukar ‘yarsa yakeyi shiyasa tayi wani irin mugun sabo da abbin nata Bata yarda da kowa saishi Bata iya zama da kowa sai shi,

Wani irin qawa zucin Mahaifinta Allah ya dasa Mata acikin ranta sbd tunda tafara wayo shine halitta mafi soyuwa a zuciya da idanuwanta,

Yagana farkoma data fara wayo qin yarda takeyi yabarta gurinta yaje gurin nema sai ahankali tadan fara sabawa da ita Amma harya dawo daukanta Bata sakewa duk da qananun shekarunta tasan Mahaifinta ta yanda ko sallamarsa taji daga nesa tana gane shine.

Wata qaramar private school ya nufa da ita Kai tsaye dake anguwar.

Yana Isa dayake maigadin makarantar ya sanshi sosai sbd yanda kullum yake zuwa kawo ‘yarsa tun tana jinjira har tayi shekaru hudu yanzu.

Da sakewar fuskar ya miqe tsaye Yana cewa”

Haji ABDUL-MAJEED baban Inaya sannu da qarasowa,

Inayar ya kalla yana dariya yace”

Inayar Abbi sauko to na kaiki gurin yagana.

Kallon Abbin nata tayi tana sake riqesa idanuwanta na kokarin cikowa da hawaye Kaman yanda tasaba kullum aka kawota.

Wata boyayyar ajiyar zuciya ya sauke yana kallonta cikin kulawa tareda zareta daga jikinsa ya miqawa yagana data iso gurinsu tana Kiran sunanta cikin kulawa da kauna.

A natse da kamilalliyar murya yace”

Barka da safiya yagana,
Mun tashi lfy?

Lfy kalau Baban Inaya,
Ya Inaya?antashi lfy?

Alhmdlh” ya furta a taqaice Yana maida kallonsa kan inayar datake kallonsa ya sakar Mata wani taqaitaccen murmushin da duk duniya ita kadaice yakewa murmushi da tattausan lafazi ya furta

“INAYA”
Karkiyi kuka zandawo da wuri inshallah kinji??

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button