Noor-Al-Hayat COMPLETE HAUSA NOVEL

Shiru Umma tayi tana kallon khadijah, a hankali tace “Ko saboda me?” Khadijah ta langwabar da kai cikin sanyi tace “Umma I will be lonely all alone, I want him to be by my side” Umma tace “Life with him there won’t be esay Khadijah, karatun ki na bukatar natsuwa sosai kin sani, shureim will ba a distraction, baxai yiwu ba Khadijah” da damuwa Khadijah tace “Umma ai shi ma makarantar fa xai dinga xuwa, plss ummata” Umma tayi shiru alamar bata san me xata ce ba kuma, can tana ci gaba da linke kayan da take tace “Rabani da shi dai kike son yi koh?” Murmushi Khadijah tayi kunya ya kamata tace “A’a wllh ummata” Umma tace “Gaskiya ne mana, ke gashi baki kusa da ni, grandson din ma kina son daukesa” Khadijah ta xaro ido, da damuwa tace “Allah sarki Ummata ba haka bane ba fa” Murmushi Umma tayi tace “Toh shkkn tunda kina son tafiya da shi sai ku je, Allah ya tsare” Sosai Khadijah taji dadi, Umma ta xauna gefen gadon tace “Yanxu ya xa mu yi da maganar sudais Khadijah, kin ga samu na yayi ya min magana….” khadijah tace “Umma ya san xan koma makaranta ai, daxu ma mun yi magana da ya xo, kuma kinga 100k da ya bani ai saboda xan tafi makaranta ne” Umma tace “Toh ai ban ce bai sani ba, kin san dai dole sai an je katsina koh?” Khadijah ta turo baki bata ce komai ba, bata son jin sunan garin ita kam, Umma ta mike ta ci gaba da abinda take tace “Shi kuma Aliyu ai ya kamata ki sanar masa xa ki tafi da Shureim din koh, ko kuma kije ma da yaron yayi sallama da mahaifiyar Aliyun” Khadijah dai bata ce komai ba idonta a kan wayarta. Can gidansu Khaleel kuwa Ummu ta sa driver yyi ma Shureim siyayya da taji tare xa su tafi UK da uwar sa, Khaleel dake xaune bedroom dinta yana duba kayan yace “Sun gode Ummu” Ummu tace “Khaleel ina son mu yi magana fa da kai, gashi gobe da sassafe xa ku wuce” ya maida hankalinsa gaba daya kanta kamar baxai ce komai ba, sai kuma yace “Ina ji Ummu” sure ya san kwanan xancen amma yayi pretending bai sani ba, Ummu ta kwantar da murya tana kallonsa tace “Abuu kasan fa saura wata daya kachal bikin ku da jawahir kuma naji ko magana baka yi” Khaleel ya shafa kansa yace “Ina sane Ummu” tace “Toh Alhmdllh tun da kana sane, amma ba wani shiri da xa ku yi ne?” Shiru yyi bai ce komai ba, can ya dago ya kalleta yace “Ummu tun da ba laifi bane ina son hada su da mahaifiyar yaron nan na aura….ina da interest a kanta” Ummu ta dinga masa wani kallo tace “Kana da hankali ma kuwa khaleel???” hade rai yayi, kan kace me ya juya xuwa Arabiya… toh nan fa ake yin ta, don Mai typing dai ba jin yaren take ba ina laifin ma yayi turanci, tun tana d’an tsintar daddaya har ya kai ya kawo ta ajiye takardar da Biro kawai ta dafe kai, ganin khaleel fa sai xuba larabci yake a fusace ga ummu sai kallonsa take ta kasa cewa komai mai typing tasan abun babba ne, ba fans ba, har ita tana son jin abinda khaleel ke cewa don haka ta juya da sauri don nemo kanwarta Ilham ta mata translating, can ita ma ta sameta xaune tana halinta wato nukurci, ashe dai ba xancen translating din larabci, rai ba dadi mai typing ta kwashi legs ta koma, nan ta ga har khaleel ya gama jawabinsa yana danna waya amma fuska a murtuke, Ummu ta d’an yi murmushi a hankali tace “Ni na isa khaleel? What am saying in here is that, ina laifin bayan anyi bikin naku da Jawahir sai ka auri Khadijahr babu mai hanaka yin hakan ae, hakan ma xai fi” Washegari Khadijah ta gama hada few abubuwan da xata bukata domin komawa UK, umma kuma ta hada ma Shureim nasa kayan cike da jin kewan yaron gashi khaleel ya rabasu da shi tun rasuwar sudais, karfe takwas saura khaleel ya taho gidan tare da shureim, Khadijah tana bedroom ta gama daukar masa kadan daga takalmansa, ganin na sudais a gun yasa lkci daya mood dinta ya canxa ta koma ta xauna a sanyaye, tun bayan rasuwarsa dama Umma ta bada komai nasa a gidan saboda Khadijah xata fi samun nutsuwa, takalman ma mancewa tayi bata bayar ba, Nanny ce ta shigo dakin tace “Khadijah jiran ki fa suke” a sanyaye Khadijah ta mike ta fito rike da takalman Shureim, driver ne daga gidansu Khaleel xai kai su airport din, Shureim dake jikin Umma ya sakko da sauri ya rungume Khadijah yace “I missed you Anty” ta shafa kansa tace “I missed you same” Umma tace “Toh kuyi maxa yana jiran ku a mota” Khadijah tace “Yanxu Shureim din ya shigo?” Umma tace “Yanxu ya shigo” Khadijah ta karasa gun umma ta rungume ta tace “Ummata sai mun dawo” Umma tayi kokarin ganin bata fara hawaye ba a hankali tace “Toh Allah maku albarka daughter, Allah ya tsare min ku, sannan ki kula da kanki plss” murya can kasa Khadijah tace “Nagode Umma” Nanny na rike da shureim cike da kewarsa xata rakasu bakin motar, Khadijah na isa bakin kofa ta juyo a hankali tana kallon Umma tace “Toh Umma ba a kai sa yayi ma Mumy sallamar ba kuma, I mean shureim” Umma tace “Lah kin ga ni har na manta, to ki yi ma Khaleel din magana sai ku fara biyawa can a gurguje ki kai sa kafin ku wuce airport” Khadijah ta gyada mata kai ta fita parlorn, Shureim ne ya bude back seat Khadijah ta dinga kallon khaleel dake xaune sanye da glasses a idonsa yana operating wayarsa, Shureim ya shiga motar sannan ta shiga tana daga ma Nanny hannu, gaishe da Nanny khaleel yayi ta amsa da fara’a ta masu Allah ya kiyaye hanya sannan ta juya ta koma ciki. Sai da suka dau hanya sannan khadijah ta kalli khaleel a hankali tace “Good morning” yace “Morning how was ur nyt?” Ta sauke idonta tace “Alhmdlh” Wayarsa dake ring ya daga ya kai kunne, sai bayan da ya gama wayar Khadijah tace “Umma tace plss kafin mu tafi in kai shureim wajen mum din Aliyu su yi sallama, idan suka yi waya tana yawan tambayar ta shi….” Khaleel yace “Ohk then” daga haka ya fadi ma driver anguwar da xai fara kai su, tafiyar kusan minti ashirin suka yi suka iso gidansu Aliyu, Bayan drivern yayi parking a inda Khaleel ya nuna masa, khaleel ya juya yana kallonta yace “Ku shiga toh” tace “Kai baxa ka shiga ba” da sauri yace “A’a, am waiting for you two a nan” a hankali khadijah tace “Ohk,” daga haka ta bude motar ta sauka tana kallon Shureim tace “Come down” daga mata hannu yyi yace “Anty ki dauke ni” ta hade rai tace “Sakko my friend” khaleel yace “Ki daukesa mana ko baxa ki iya bane?” murmushi kawai tayi ta dauki yaron nata ta shiga cikin gidansu Aliyu yana daga ma khaleel da ya bi su da ido hannunsa, A hankali khadijah ta murda kofar taji a bude ta shiga, babu kowa parlorn, tana jin Shureim na ce mata gidansu wannan uncle din nan nasa ne, tana kokarin sauke sa kasa sai ga Aliyu yana sakkowa stairs, jallabiya ce baki jikinsa tayi saurin dauke kanta bayan sun hada ido, tana ta tsaye har ya iso inda suke tsaye, ya mika hannu ya karbi shureim komawa baya tayi da sauri don wani shock ta ji ta dalilin hannunsa da ya taba jikinta, shi kam sai kallonta yake ya maxa ya kawar da memoryn da bai son tunawa a ransa, Murmushi Shureim yake yana kallonsa yace “Uncle good morning” Aliyu ya shafa kansa shi ma yana murmushin a hankali yace “Morning how are you sweetheart” yace “Am fine” Kallon khadijah yayi suka kara hada ido tayi saurin sunkuyar da kanta, yace “Good morning Iman” kame kame ta fara yi, can tayi saurin cewa “Ina kwana, wajen mumy muka xo” yace “Ohk tana Bedroom” taki yarda ta sake kallonsa tace “Toh kayi mata magana muna sauri ne” yace “mu je up stairs” daga haka ya fara tafiya ta bi bayansa xuciyarta na bugawa wannan tunanin da yake ita ma shi take a lkcn. A hankali ya bude kofar dakin mumy ya shiga da sallama, tana xaune da aminyarta, ta daga kai tana kallon Aliyu, ya sauke yaron hannunsa ya tafi da gudu ya hau kanta yace “Mama good morning” lkci daya bakin cikin dake tattare da fuskar Mumy yayi fading ta rungume yaron tana murmushi sosai tace “Kai da waye Shureim, wa ya kawo ka” Yace “Ni da Anty na” Aliyu ya juya yana kallon khadijah da ke tsaye bayansa ta ki shigowa ya koma gefe ya tsaya, Mumy na kallon ta tace “Maa sha Allah ashe tare ku ke, toh ki karaso mana Khadijah” kanta a kasa ta karaso ciki a sanyaye ta xauna tace “Ina kwana mumy” da fara’a mumy tace “Lafiya lau Khadijah ya gidan, ya su ummar ki?” A hankali khadijah tace “Suna lafiya Mumy” gaishe da kawar mumy tayi sannan tana kallon mumy tace “Mumy dama xan koma karatu ne kuma xa mu je da shureim shine Umma tace in kawo sa yayi ma ki sallama” Mumy tace “Allah sarki, amma naji dadi sosai wllh, Allah ya kai ku lafiya, ya bada abinda aka je nema” kallonta Kawai Aliyu yake jin abinda ta ce, Mumy ta mike tace “Bari in kai sa su gaisa da Abba yana nan” daga haka ta fita, Hajiya Salma dake ta kallon khadijah cike da tausayinta tace “Allah ya bada nasara kin ji Khadijah, sai a kula sosai” Khadijah ta sunkuyar da kai kasa tace “In sha Allah Mum na gode” Bayan kusan minti goma Mumy ta dawo, duk khadijah ta damu saboda khaleel da ta bari a mota, Mumy tace “Toh mu je kema ku gaisa da Abban koh” khadijah ta kasa dago kanta ta mike da kyar ta bi bayanta har xuwa side din Abba, da fara’a ya amsa gaisuwarta yana tambayarta mutanen gidansu, ba su dau lkci a parlorn ba suka fito tare da mumy, Lkci daya mood din mumy ya canxa a hankali tace “Mu shiga ki gaida iklima” Khadijah tace “Toh” daga haka ta bi mumy suka shiga dakin. Kallon iklima kawai khadijah take ganin yanda ta rame kamar warce ta shekara tana ciwo, cike da karfin hali tace “Sannu iklima Allah ya sauwake” kallonta kawai Iklima take ita ma ta kasa cewa komai, Mumy na kallon khadijah tace “Mu je” Khadijah ta bi bayan mumy a sanyaye, Mumy tace “Babu daman in baki turarruka tunda flight xa ku bi Khadijah, amma kar ki damu xan tura ma Maryam kudi a can ta siya ma ki, sai tayi ma Shureim ma shopping” murmushi kawai khadijah tayi tace “Ba komai mumy na gode” Har downstairs mumy ta rakata, Aliyu dake xaune parlorn tare da shureim ya mike ganin sun sakko, mumy tace “Toh Allah ya tsare, nagode Khadijah” Khadijah tace “Ameen mumy” daga haka ta bi bayan Aliyu da shureim don har sun nufi kofa, a tsakar compound din Aliyu ya jira Khadijah ta iso inda suke, bata yarda ta kalle sa ba xata wuce su ya riko mayafinta, juyawa tayi amma ta kasa kallon idonsa, murya can kasa yace “Baxa mu yi sallama ba?” Still ba tare da ta kallesa ba tace “Mumy na xo yi ma sallama ba kai ba” yayi murmushi yace “Ohk, Allah ya kiyaye hanya, sai mun hadu a can, cos am also leaving tomorrow” Khadijah bata tanka sa ba yana rike da shureim har suka nufi gate, kasa daurewa tayi daga karshe tace “Me ya samu iklima haka?” Da kamar Aliyu baxai ce komai ba sai kuma yace “She is suffering from Hiv” Khadijah ta xaro ido tana kallonsa a tsorace, yace “Yea, anjima dangin mahaifinta xa su xo su tafi da ita…” Lkci daya hawaye ya cika idon Khadijah tace “Toh Anty khadijah fa?” Yace “Tana asibiti, tot kin san tayi hatsari?” Khadijah ta girgixa kai tana kallonsa, yace “She had accident 2 weeks back” da damuwa tace “Toh ya jikin nata?” Yace “Ni tun lkcn da na kai su mumy ban san ke komawa ba so I don’t knw” Khadijah tayi shiru duk jikinta a sanyaye, Aliyu yyi murmushi bai ce komai ba har suka fito waje, Khadijah ta bude back seat tana kallon khaleel da damuwa tace “Don Allah kayi hakuri mun bata maka lkci” ya d’an yi murmushi yace “No problem” tun da Khalil ya kalli Aliyu sau daya bai sake kallonsa ba, Aliyu yace “Barka da asuba” sai a sannan khaleel ya kara kallonsa yace “Good morning” Shureim ya shiga mota yana daga ma Aliyu hannu sannan khadijah ma ta shiga, suna hada ido da Aliyu ta sunkuyar da kanta, Aliyu na kallonta yace “Allah ya tsare” Kamar baxa ta ce komai ba sai kuma tace “Ameen” ya rufe masu motar, driver ya tada motar suka bar layin, shureim ya fiddo bandir din Dari biyar a aljihunsa yana nuna ma Khadijah yace “Anty wannan Papa din nan ya sa min kudin a aljihuna, I told him no but he didn’t even listen to me” Khadijah ta dinga kallon kudin, ya ciro wani kudin yana nuna mata yace “Uncle ma ya bani wannan” Khaleel dake danna wayarsa bai dai ce komai ba, Khadijah ma ta rasa abinda xata ce.