BABBAN YARO BOOK 2 COMPLETE NOVEL

BABBAN YARO BOOK 2 COMPLETE NOVEL

Jikina nake dubawa babu Riga sai brez itama da ita gwara babu tunda duk ga breast dina nan a waje, siket dina duk ya tattare cinyoyina a waje.
Zuciyata nayi min wani irin zafi na mike zaune hade da d’aukar rigata ina sanyawa.
Naji yace.” Yanzu ni dake waye d’an iska? Kawai daga tab’a ki kin wani lanjare har kina rungume ni kina kara bude min jikin ki ummmm!. Ki bani amsa ta.”
Fad’ar halin bakin cikin da nake ciki a bata lokaci ne, rigar ta na sanya na dauki dankwalina na d’aura hade da gyara siket dina na soma kokarin bude kofar motar
Wani guri naga ya danna jikin kujerar sai ta mike zaune dani na zauna kusa dashi.
Har yanzu da murmushi a fuskarsa yace.” Kinyi shiru baki bani amsa ba.”

Muryata na rawa nace”Bude min kofa in futa Allah zai saka min.”
Dariya yasa yana nuna ni da hannunsa yace.” Allah zai saka miki kika ce.? Hummmm Asma’u manya mata.”
Shiru nayi masa ina dauke Kaina.
Yace.” Ki Bari lokaci nan zuwa da zan tsotse ki na shanye ki tasss!!!!! Lokacin da ya fad’i maganar wani irin fleenges ne ya zo min lumshe idona nayi gabana na fad’uwa Yace.” Muje ki rakani in duba Momyna in wuce ina da gurin zuwa yanzu. “
Kallonsa na danyi nayi saurin kauda kaina zuciyata na raya min kila zai tafi gurin karuwarsa ne ya biyawa kansa bukata.

Rai a bace nace”Kaji tsoron Allah a duk inda kake.”
Babu yabo babu fallasa Yace.” Tom Malama ta nagode da wa’azi.” Kofar motar ya bude na futa, shima ya futo Idonsa sakaye da glass mai duhu, naji yana fadin”Wannan unguwar taku banda dalilin Ku ban tab’a shigowa cikin ta ba.”
Banza nayi dashi na tsallaka titi ya biyo bayana Cikin yanayin tafiyarshi ta jarumai yazo ya wuce ni

Da sauri na bi bayansa domin kar ya wuce gidan.
Tsayuwa nayi kofar gidanmu har ya k’araso ya tsaya muna kallon junanmu nace”Sai ka Bari in Sanar da Masu gidan.”
“Owk” yace yana bin gidan da kallo, shiga nayi na barshi tsaye a gurin.
Mamaki yake sosai yanzu dama acikin wannan gidan Asma’u take rayuwa? Duka girman gidan bai kai b’angaran mai gadin gidan shi girma ba, gyada kansa yake yana duba ‘yan gujub-gujub din gidajen dake layin namu a cikin zuciyarsa yake fadin talaka na ganin rayuwa me zai hana baza’ayi zazzab’in maleria ba kwataci duk sun bi hanya sauro da kudaje da bola ko ina.

Tsaye na ganshi jikin bango hannunsa nan nade a k’irjinsa nace”Shigo to”
Gaba nayi yana bina a baya

Umma na zaune gefen sabuwar tabarmar da ta shimfid’a masa tana sanye da farin hijab fuska a sake take amsa sallamarsa.
Cikin ladabi naga ya tsaya bakin kofar ya cire hadd’adan takalimsa karfashi sanye da wata lafiyayyar safa ya karasa kan tabarmar .

Umma fad’i take”Sannu da zuwa yaron arziki Mara ba lale.
Zama yayi kanshi a kasa yace.” Barka da yamma Umma na same Ku Lafiya.”?
Umma tace”Lafiya Lou Alhmdullahi ya kokarin ka da fama da jama’a. “?
Yace.” Alhmdullahi wallahi ya me jiki kuma.”?.Tace” Jiki yayi sauk’i ai bs wani tsanani Yayi ba Asma’u ta ta soka.” Murmushi yayi tare da fadin”Dama yau nayi niyar in shigo mu gaisa sai kuma take fadamin Momyna babu lafiya.”
Umma tace”Wallahi kuwa tari take amma da sauk’i dai tunda Aminu ya siyo mata magani Tasha ta samu tayi bacci.”
Yace.” Tou Alhamdullahi Allah ya kara sauk’i. “
Yanda suke hira da Umma sai abun ya bani mamaki kamar Wanda suka shekara da sanin juna Umma sai shi masa albarka take da fadin”Muna ganin taimakon talakawa da kake yi a garinan muna jin dad’i Ubangiji Allah ya tsare ka ya kare ka daga sharrin masu sharri. ” yaji dadin adduoin da Umma take masa ga yanayin yanda yake amsawa

Mimi dake kwance a daki tana bacci kamar a mafarkin taji muryar shi firgigt ta tashi ta zauna k’irjinta yayi mata nauyi sosai rarrafowa tayi ta futo tsakar gida tana dafa bango
Nice na fara ganinta ganin kamar tana kokarin fad’uwa ya sanya naje da sauri na rike ta muka karasa kusa dasu Umma
Tace.” Yauwa ai gata nan ma ta tashi sannu Mimi.”
Zaunar da ita nayi kusa da shi, na matsa gefe
Amjad mamaki ramar Mimi yake duk da yake dare ne kuma tsakar gidan babu wadataccan haske sai da ya fahimci tana jin jiki.
A hankali yace.” Momyna ya jikin ki? Ashe haka Abu yayi tsanani. “
Cikin sanyayyr murya tace.” Jiki da sauk’i .” gyada kansa yayi tare da kallon Umma yace.” Kunje asibiti da ita kuwa.”?
Kafin Umma tace Wani Abu Yaya Aminu ya shigo gidan.
Gabansa ne ya fad’i ganin Mutumin dake zaune ga gidan jininsa Mimi kenan a zaune a kusa dashi, lokaci guda ya b’ata fuskarsa hade da yin kicin-kicin da ita sama-sama suka gaisa dashi Yana mamakin me ya kawo shi, zama yayi gefen rijiya yana sauraran maganar da suke yi da Umma.

Umma tace.” Ba muje asibiti ba amma dai gobe in Allah ya kaimu za muje a duba ta sosai.”
Gyada kansa yayi shiru na minti biyu yace.” Gobe idan Allah ya kaimu zan turo dravar sai a kaita asibtin malam Aminu a duba ba ta sosai.”

Umma tace”Allah yayi albarka ai da ka bari ma, sai muje asibitin Murtala .” Hannu ya zura aljihu ya futo da kudi masu yawa ya zube gaban Umma ya mike tare da fadin” Zan wuce Allah ya bata Lafiya .”
Umma tace”Harda wahala kuma ai da ka barshi.”
Shiru yayi ya mik’awa Aminu hannu suyi sallama.
Rai babu dad’i Aminu ya mik’a masa nasa hannun sukayi musabaha.
Takalmin shi ya sanya Umma sai godiya take masa futa yayi cikin sauri Umma ta kalleni tare da fadin” Kije ki raka shi mana kinye tsaye.”
Bayansa nabi da sauri..
Yayi nisa sosai don Haka sai da na k’ara sauri.
Na tadda shi.
Yana kokarin bude mota na same shi
Yace.” Amma nayi mamakin ramar Mimi,Abunda kika fada gaskiya ne.”?
‘K’warai kuwa Mimi na sonka sosai kai kuma kana yaudarar ta.”
Shiru yayi yana tunani tabbas abunda Asma’u ta fada gaskiya ne baya jin dai-dai da kwayar zarrah na son Mimi a zuciyar sa, yana yi mata so ne kawai irin na musulunci sai kuma sunan mahaifiyar sa da take dashi.

Ajiyar zuciya ya sauke tare da fadin”Allah ya bata Lafiya, Nasan ni babu laifina anan gaskiyar magana ko Yanzu aka ce an bani ita zan aure ta darajar son da data ke min.”
[11/10, 8:25 AM] BintuUmarAbbale: BABBAN YARO

Mallakar_BINTA UMAR
LITTAFIN MALLAKI NA NE KUN BIYA KUD’IN KARATU NE KAWAI DUK WACCE TASAN ZATA FUTA DASHI WAJE DON GIRMAN ALLAH TAYI MIN MAGANA NA DAWO MATA DA KUDIN TA.

47

Shiru nayi masa domin na rasa abunda zance dashi ni kaina al’amarin Mimi yana bani tsoro Mota ya bude ya shiga tare da fadin”Ni zan tafi zan kira waya insha Allahu. “
Matsawa nayi daga jikin motar ba tare da nace masa komai ba ya ja ya tafi na lura jikinsa duk yayi sanyi.
Ina koma wa gida na tarar da Ya Aminu ya tasa Umma a gaba sai faman bala’i yake mata
Ina shiga ya hau d’ura min ashar wai me yasa na gayyato Amjadu gida wallahi komai kulafucin sa ba zai bar mishi Mimi ba.
Masifa yake kamar zai dake ni Umma tace”Kar ka sake ka doke ta Aminu Sam Asma’u bata da laifi Kaine dai idonka ya rufe, ka ke ganin da laifin ta anan.”.
Kan Mimi ya dawo cikin hargowa yace.” Wallahi Mimi ko mutuwa zaki baza ki aure shi ba sai dai idan ki Mutu ni dashi mu rasa amma ina ji ina gani bazan bar masa ke ba.”
Yana gama maganar shi ya fuce daga gidan a fusace.!
Mimi ta fashe da kuka tari ya sark’e ta, aikuwa ta dinga yi bubu ji babu gani,
Umma ta jawo ta jikinta ta rungume ta sosai tana danne mata kirjinta hankalinta duk ya tashi
Da sauri tace”Asma’u d’ebo ta murhu a shafa mata ko Allah zai sanya ya Tsaya tari.
Da gudu na nufi kicin na d’ebo toka Umma ta bude rigar Mimi ta shafa mata.
Kamar kara ingizata ake ta cigaba da tari!!! Nace.” Ina maganin a dauko a kara bata.”
Da kyar Umma tace”Dauko a daki.” Dakin na shiga da sauri na dauko maganin, abunda na gani yayi mutukar gigita ni da bani tsoro wani irin jini bak’ikkirin na gani daga bakin Mimi yana zubowa jikin Umma,
Da sauri na jefar da kwalbar maganin nayi kanta INA salati.
Umma kuwa kuka ta fashe dashi tana tare jinin da hannunta.
Baki na rawa nace”Umma jini ne ko.”? Tace.” Asma’u maza duba waje ki gani Aminu nan ki kirashi mu tafi asibiti abun ya zama babba.”
Da gudu na futa ko talkami babu.
Mimi ta galabaita iya galabaita tari take sosai jini na zuba daga bakinta idanunta sunyi jajazur dashi sai daga hannu take.
Ni da Aminu muka shigo gidan hankalumu ya tashe.
Yana ganin Abunda yake faruwa ya gigice tare da fadin”Innalillahi wainnailahi raji’un. ” futa yayi da sauri ya dauko mota.
D’aukar ta yayi kacokan ya futa da ita da saurin
Nida Muka rufa masa baya zuwa yanzu na fara kuka tukuru ganin yanda Nuffashin Mimi yake hawa da sauka.
A dai-dai sahu har kofar gidanmu don haka muna futa muka shiga saboda idanun Jama’a Umma ta rungume Mimi a jikinta hankalinta duk ya tashi mai a dai-dai ya ja mu katafi shi ma hankalinsa ya tashi da ganin abunda yake faruwa ya tausayawa Mimi sosai.
Murya a sanyaye Umma tace” Ka kira aunty Ku a waya ka fada mata halin da ake ciki, sannan ka kira Kawunta wato Babansu Munnu.”
Wayarsa ya futo da ita da sauri.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60Next page

Leave a Reply

Back to top button