BABBAN YARO BOOK 2 COMPLETE NOVEL

BABBAN YARO BOOK 2 COMPLETE NOVEL

Ranshi babu dad’i yace.” Matar aure tuntuni na zab’e ta Kawu Asma’u ita na zab’a Insha Allahu ina fatan ta zama Uwar ‘yayana.” Kamar yanda Kawu yayi tsammanin haka daga gareshi hakane ya tabbata hamdala yayi a fili yace.” Insha Allahu baza kayi nadamar auran d’iyar mu ba Allah ya sanya alkairi..” Ameen suma ameen Yanzu dole kaje ka Sanar da Umma halin da ake ciki na janye auran Mimi tunda bai hallasta ba.” Kawu yace.” Yanzu kuwa zan bar kasuwa inje in Sanar da ita, kuma maganar d’aurin aure tanan jibi insha Allahu.” Sallama suka yi da juna, Amjad ya kashe wayar zuciyar sa na sak’a masa abubuwa da dama jikinshi na bashi kamar akwai wani Gagarimin al’amari da zai faru nan gaba.

Kai tsaye gidan Granny ya wuce domin ko ya koma gida yanzu yasan mutane baza su bar shi ya huta ba, to zancan kenan itama Granny fad’a tayi ta yi tana fadin dama Ashe basu da Asali yaran haka kawai zai jawo wa kansa zuvewar mutum ci to itama ba ta yadda da wannan auran ba, yana kwance cikin kujera yana jinta bai ce mata komai ba, duk abun duniya ya dame shi, daga zarar ya tuni Asma’u sai yaji faduwar gaba, abunda bai ta faruwa dashi ba.


Innalilhi wa inna ilahi raji’un shine abunda Umma take nanatawa lokacin da ta gama sauraron maganar da Kawu Yunusa yake tafe da ita, tashin hankalin ta sai ya ninka na da tana fargar bar Mimi taji wannan mummunan labari tsakanin ta da Amjadu babu aure tunda dai ya zab’i Asma’u a cikin su, ga jikinta ya rikice tun d’azu take kuka an kasa shawo kanta. Cikin yanayin damuwa da tashin hankali Tace.” Kawu wannan k’addara Allah ya ije mana ita naso yaron nan ya zab’i Mimi domin ceto ranta, rai shine abun dubawa Mimi marainiya ce kuma tana dauke da ciwo mai mutukar hadari kuma kaga ta dalilin sa ta Sam……… Bata k’arasa ba Kawu Yunusa yayo kanta da bala’i yace.” Baki Isa ba Mariya wallahi tallahi baki Isa ba!!! Arziki yana neman mu kina korarsa awwo!! Bakin ciki kike mana? Ko kuma bakin halin ki zaki nuna mana wanda kika saba, ‘yarinya dai ‘yarmu ce muna da ikon mu aura mata duk Wanda muke so ke!! Baki Isa ki hana mu ba ‘yar bakin ciki kawai.” Tsakanin Kawu da Umma dama ba a shiri tun Asali, basa jituwa a cewar sa itace take zuga Babanmu lokacin in ya dauki albashi baya taimaka wa mahaifiyar su lokacin tana Raye.Umma ta fusata! Ranta ya b’aci sosai wato har Yunusa yana da bakin magana akan ‘yayan ta, mutanan da suka wofin tar da ita bayan mutuwar mijinta suka watsar da zuri’ar shi, wahalar duniya babu wacce bata sha ba, akan ‘yayan ta, sai yanzu da suka ga sun zama mutane shine zasu yi wata magana har da gadara cewar ‘yayan su saboda kwadayin abun duniya to har indai itace ta haifi Asma’u zata nuna masa iko a kanta. Ranta a mutukar bace tace.” Yunusa ni kake d’agawa murya har kana kokarin kai min duka akan ‘yaya na, Yanzu kai kana da bakin magana akan Asma’u wacce baka San cin ta ba baka San shan ta ba, sutturarta karatun ta duk baka San wannan ba, sai yanzu daka ga ta zama mutum sannan zaka yi wata magana akanta.”? Ta k’arashe maganar cike da mamaki, Kawu Yunusa ya mike tsaye a fusace! Yana a matsayin wan mijinta take kiran sunan sa kai tsaye, ransa ya b’aci sosai yace.” An fad’a miki nace na fad’a miki magana Mariya kiyi abunda zakiyi dama ai baki da kunya nasan halin ki d’an uwana yayi hakuri zama dake, kina maganar suttura da sauran su, ki fad’i kud’in wahalar da kikayi sai a biya ki, wacce bata gaji arziki ba, mu bama haihuwar ‘yayan banza d’an uwana ya iya haihuwa koma komai abunki sai anyi wannan auran.”!!!

Umma ta fashe da kuka Wanda yasa na futo wuf!! Daga cikin dakinmu Allah yasa na samu Mimi tayi bacci duk irin tujarar da Kawu yake wa Umma a kunne na kuma duk naji zancen da suke yi, rai na a b’ace na futo INA kallon Kawu dake tsaye kan Umma yana ta surfa mata masifa! “Ita yarinyar da kike so ya aura yace. Ba yaso saboda rashin galihu ya fi son ‘yar Asali me cikkakiyar nasaba, bayan wannan kuma sun sha nono d’aya babu yadda za’ayi ya aure su duk su biyun, in banda kidahumanci irin naki Mariya ‘yar ki zata auri mai kudi Wanda duniya ta San dashi ke kanki kin bar kangin talauci ki nuna ba kya so Allah yayi wadaran ki Mariya.”! Ya k’arashe maganar sa a harzuke.

Kuka na fashe dashi jin irin cin mutumcin da Kawu yake wa Umma tana kuka ko tausayin ta baya ji, idanuna sun rufe ta inda nake ganin girman shi ya zube a gurina, tunda nasan da me yake wannan tashin hankali, duk dan kudi da soye-soyen rayuwa yau da talaka ne Amjad Kawu bazai tako cikin gidan mun ba ko dan kar ace yayi kayan daki, amma yanzu dubi yadda yake tada hak’arkari da jijiyar wuya.

Ina kuka nace.” Kawu wannan ba dai-dai bane kar ka manta da cewar har gidan ka naje munyi magana dakai cewar mutukar Amjadu bai auri Mimi ba nima bazan aure shi, to yanzu duk naji abunda kuke magana akai ni da Mimi mun sha nono d’aya, Amjadu ya zab’e ni a matsayin matar auran sa ya bar Mimi, Kawu kayi hakuri da hukuncin da na yankewa rayuwa ta, idan shine ya aiko ka ka koma ka fada masa cewa ni Asma’u d’iyar Sulaimanu mai madara, bazan aure shi ba, idan son gaskiya yake min ya karb’i Mimi ‘yar uwata a matsayin matarsa ta sinna domin mu ceto rayuwar ta, daga halaka.”
[11/14, 6:35 PM] .: Cikin tashin hankali da damuwa Kawu yake kallon Asma’u, yace.” Asma’u kina da hankali kuwa kike fad’ar wannan maganar cewar ke baza ki aure shi ba kin barwa wata.”! Gyada kaina nayi rai na a dagule nace”K’warai kuwa Kawu na rantse bazan aure shi ba, sai da ya hak’ura tunda babu halin ya hada mu mu biyu idan kuma da gaske kaunata yake tsakani da Allah to sai yazo yayi abunda nace.” Kawu yace.” Baki Isa ba wato Bakin Ku d’aya da Uwar ki ko.”? Da sauri! Nace”Ko daya Kawu wannan ra’ayi na ne, kuma don Allah ina Neman alfarmar ka daina zagin Umma haka, kayi hakuri kar kace nayi maka rashin kunya, a matsayin ka na babba bai dace ba da abunda ka keyi ka daina don Allah.”

Kawu yayi mamakin abunda yarinyar tace wato suna so suyi musu bakin ciki suga samu suga rashi,babun bad’ulahu kenan abunda bazai yiwu ba wallahi ko gawar Asma’u ce sai an kaita Gidan Amjadu sai dai idan shine yace ya fasa auran.

A fusace ! Yace.” Duk wani iya shege da zakuyi ke da uwarki a tafin hannuna kuke, kuma ku rubuta Ku aje, jibi I war haka kin zama matar Amjadu kin zama Mallakin sa, in dai nine wakilin ki.” Ya futa a fusace. !!

Umma naje na rungume da kyau! Ina kuka ina share mata hawaye nace”Umma ki kwantar da hankalin ki duk yanda kike so haka za’ayi ki zab’a min miji Wanda kike so Amjadu na bar wa Mimi .”

Umma tace.” Asma’u kina jin abunda Kawun Ku yake fada ko akan ki kina jin irin cin mutumcin da yake min ko.? Nace” Umma duk naji kiyi hakuri ki kyalesu dama ba yau suka saba miki cin mutum ci. Ni nasan yanda zanyi insha Allahu Mimi bata da miji sai Amjadu ki kwantar da hankalin ki.”

Hannun d’iyar tata ta rike tare da fad’in”Ubangiji Allah yayi miki albarka Asma’u Yanda kike min biyyaya Allah ya baki ‘yaya masu biyayya kema, yanda kike ceci rai ubangiji Allah yasa Annabi ya cece ki kema.” Wasu zafafan hawaye na hau sharewa lokaci guda tausayin kaina ya kama ni, wani irin hali na shiga a lokacin ta inda naji gwara min mutuwa da rayuwa Allah-Allah nake naga Mimi a gidan Amjadu ko ma samu hankalin mu ya kwanta, Alluma ajirin fi musibati wa aklifni kairan minha itace addu’ar Dana ke ta maimatawa a zuciyata tare da Innalillahi wa inna ilahi raji’un, lokaci guda naji zuciyata tayi sanyi na kalli Umma tare da fadin”Don Allah Umma kar a kara tayar da maganar nan domin I Dan Mimi taji to wani tashin hankalin ne, Umma kija kunnen Ya Aminu a kan hakan.” Umma tace”Nima abun ya soma damuna Asma’u Insha Allah zan ja kunnen sa, ke dai Allah yayi miki albarka insha Allahu yanda kika sanya ni farin ciki kema ‘yayan ki zasu sanya ki.”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60Next page

Leave a Reply

Back to top button