ABBAN SOJOJI BOOK 1 COMPLETE

nan sehrish ta shiga jero mata abunda ya faru hada labarin aljanin daren nan da kuma maganar jini da taga yana bleeding daga under ɗinta,
bayan ta kammala bayanin ta shiga Nuna mata kayan da aljanin ya kawo mata sannan tace “Aunty azmi dama akwai aljani me mutunci irin haka ?
data shoulder dinta azmo tayi tare da cewa ” dukkan abun da kika gani jiya ba gaskiya bane ! you’re just dreaming cos you were scared but am the one that brought all these stuffs to u, kuma ni ce na kawo ki dakin ki, bansan dai mai ya faru ba amma nafito around 10 na ganki while u were fainted on the floor
sai nayi deciding na dauko ki na kawo ki bedroom dinki shine naga blood na zuba a jikin ki, dama already Ina da pad da panties shine na kawo miki wannan shine gaskiyan abunda ya faru,’
Azmi ta karasa maganar tana kallon sehrish wadda tasaki baki galala don mamaki gashi azmi ta rikita ta ta canza mata tunanin ta,
Azmi ta lura da yanayin da sehrish ta shiga sai taji tsoran karfa yarinyar ta rikice don haka ta kara da cewa “Nima na taba yin irin wannan mafarki just like u did, ba wani Abu bane, then maganar menstruation wato blood din da kika gani ba na cuta bane ko ciwo sakamakon punishing dinki da fawan yayi , wannan Jini ne na al’ada Wanda ko wace mace take yi shin baki taba sani ba kuma dama baki taba yi ba am just doubt abt it,
Ta ƙare maganan tana kallon ,
ɗan shiru tayi tana nazari ita dai tasan kamar ta ta6a ji game dashi sai ynx take ɗan tuna wani abin husanna da jahad sun riga ta farawa tasan game dashi rashin kwanciyar hankali da rashin natsuwa yasa ta gaza fahimtar cewa na al’ada ne tabbas tsohuwa ta ta6a koya musu wannan ,
” nasani mantawa nayi amma aunty azmi wai dagske ba wani aljanin da yazo min ? kina nufi is not true amma fa har abu aka samin a pant na sanya kuma ni banga kowa nd i didnt see u a time ɗin ,’
ganin ta fara ƙoƙarin gane ƙarya take mata ne yasa ta ce “pls forget about the past ! we’ll talk about It later ,
Daganan azmi ta ƙara wayar mata da kai game da yadda zata tsarkake jikinta da sauran muhimman abubuwan,
Duk ranar batayi aiki ba azmi ce tayi komai kuma har room ɗinta takai mata breakfast lafiyaye hada kayan marmari , sannan ta tunatar da ita akan tasha maganin da ta bata,
Junaid yayi kewar ganin ta, ya kasa fita ko ball ya buga saboda tunanin ta , sai faman sintiri yake yi yaga ko zata fito amma shiru babu ita ji yake kamar yaje bedroom ɗin nata yayi mata magana,
Gaza jurewa yayi cikin sauri ya sauko down jikinsa sanye da jeans da tshirt
A kopar ɗakin ya tsaya tare da yin knocking ,
lokacin har tayi wanka ta shirya tsaf shigar da ta saba yi ta maza, ta canza kuma pad ɗin data sa,
har ynx batayi tunanin wasu abubuwan ba kamar hankicif da taga an naɗe mata gashin bakinta da na jagirar ta duk ba tayi tunanin wani abu ba, sai ta sawa aranta cewa duk azmi ce tayi wannan,
ta gyara komai daƙar tayi fixing ɗin gashin bakin saboda gam ɗinsa ya ɗan saki saboda jikinsa yayi wetting sakamakon kukan da tasha,
Jin knockinga yasa ta yin gaggawar idasa kifa hular akanta, sannan ta ƙarasa gaban kofan ta buɗe,
Lokacin da ya yi arba da kyakkyawar fuskar nan tata sai yaji natsuwa da kwanciyar hankali sun zo masa
“am tukur dama nazo naji meke faruwa ne yau banganka ba,’;
ɗan murmushi tayi jin yadda ya damu da ita tace” Zazza6i nayi amma ynx da sauƙi Alhmdllh,’
ta ƙarasa maganar tana sunnar da kai, aransa ya ce “mai ƙarya ɗan wuta, amma a zahiri sai ya ce “Allah ƙaro sauƙi,
“Ameen ngde” ta faɗa tana ƙara gyara tsayuwanta,
Shiru su kayi na ɗan wani lokaci wani irin kallo yake binta dashi confidence ɗinta na bashi mamaki ????????ABBAN SOJOJI????
Writer Hafsat Bature
~Boss Lady~
Page 37 to 38
Shiru su kayi na ɗan wani lokaci wani irin kallo yake binta dashi confidence ɗinta na basa mamaki ita ala dole namiji ce,
“Can u make a choculate cake for me,’?
Ya tambaya yana kallonta
ɗan zaro ido tayi hakan ba ƙaramin kyau tayi masa ba,
Cikin en ina tace” choculate cake kuma ranka shi daɗe banda lafiya,’ ta faɗi hakan tana ɗan dafe waist ɗinta alamar akwai ciwo wurin,.
yar dariya yayi kafin ya ce “naso ace zaka iya haɗamin da nayi ko browsing ne a wayata sai na baka ka ga yarda akeyi saboda ina buƙatar cin…..’
tun kan ya idasa ta katsesa “zan iya tsaf in ka ban wayr zan ga yadda ake yi sai nayi….
abun yaso yasa shi darawa dama dagangan yayi mata haka saboda ya gane cewa ita ce ke satar masa waya tana kiran yan uwanta, yayi hakan ne don ya haɗa ta da ƴan uwanta dake nemanta,
tayi tunanin ita ce tayi masa wayau batasan cewa shine yayi mata wayau ba domin yasa recording da za’rar ta fara wayar recording ɗin zai soma yana so ya ji meke damun ƴan uwan nata,
Bayan ya bata wayar ya fi ce daga gidan, jikinta har rawa yake yi ta samu nama,6oyewa tayi a wani corner ta danna wa su husanna kira,
A lokacin jahad bata kusa sun fita amsar wani tallafi da ake rarrabawa a gidan wani ɗan majalissa ita da tsohuwa sun bar wayr a gida,
wayau su kayi ma husanna don ta zauna suka bata wayar tayi game sannan suka datse ta a ɗaki da key gudun kar ta fita kar kuma wani ya shigo ya cutar da ita tun da ba kofa a gidan buhu ne kamar labule,
da tagama buga game ɗin taji shiru gidan ba kowa ta kwakkwala masu kira kawai sai ta kama rera kuka tayi mai isarta ta koma ta kama bacci,
Ringing ɗin wayar ne ya tayar da ita har sai da ta tsorata saboda ta ajiye wayar a saitin kunnan ta,
Cikin sauri tasa hannu ta ɗaga wayar tana sauraran jin muryar wanene,
Sehrish ta gyara murya tare da cewa”assalamu alaikum yar uwa ni ce pls kiyi mgna da sauri ya jikin naku ya husanna taji sauƙi ko har ynx da haukan nan akanta ?
ta tambaya tana jiran amsa
Sautin kuka taji tunda taji hakan ya tabbatar mata da cewa husanna ce ta ɗauki wayr saboda ta tsani ace mata tana hauka ita bata yarda ba har yau !
“Subhanallahi kash ! husanna ke ce..? ta tambaya kamar tana a gabanta,
Cikin muryar kuka tace “ni ce! shine kika tafi ki ka barmu ko ? cikin wahala da bakin talauci kullum ba abinci sai mu jera kwana 5 muna cin ɗumamen tuwa….’
Jin wannan maganar yasa kwalla ta taru a idon sehrish ci gaba da sauraronta tayi
“ni nagaji dan Allah ki dawo ko kizo ki dauke ni wlh bana jin daɗi, ko isasshen bacci bana samu ga sauro ga yunwa ko kayan sawa babu kullum wasu tsummo karai tsohuwa take bamu muna sawa ni nagaji gsky,’
Sehrish batasan lokacin da kuka ya 6arke mata ba, sam tagaza magana tuni jikinta ya soma jijjiga kamar wadda sanyi ya buga
“Kinyi shiru baki ce komai ba ? kin manta oumman mu tace duk runtsi duk wuya karmu rabu da juna amma kika tafi ko ? baki sona ko ? So kike na mutu ko, to shikenan zan je na kashe kai….’
tsawa sehrish ta daka mata wanda hakan ya dakatar da ita daga magana ” ya isa ! Ya isa! ya kike so nayi? saboda ku nake zaune a nan husanna, bashi ne na dubu ɗari tara akaina how can i pay it ? i dont ave anything dole na tsaya nayi musu aiki na tsawon shekara ɗaya da rabi,saboda ku !
daker ta ƙarasa maganar tana share kwalla,
Jin yadda sehrish ke faman shesshekar kuka yasa jikin husanna yin sanyi ta ce “kiyi hakuri in na 6ata miki rai bansan ran ki zai 6ace ba,’
dakyar sehrish ta tsaida hawayen ta gyara wayar a kunnanta tace” rai na be baci ba ina kuka ne saboda ku halin da kuke ciki, amma karki damu kinji ƙanwa ta in na samu kuɗi zan tura muku insha Allah ki tayani da addu’a,’
cikin sanyin murya husanna tace” ina miki addu’a kullum bana mantawa,’
Murmushi sehrish tasaki kamar suna kusa da juna tace”I love u so much shashasha,’
tana jiyo muryar husanna ta cikin wayar tana tiƙar dariyar saboda ta tuna mata da wani abu,
daga nan sehrish tace “zan ajiye waya send my regards to jahad & tsohuwa,’
husanna tace”insha Allah zasu ji”
daga nan ta katse wayar ranta fal saboda taji muryar husanna, cikin koshin lafiya,
nan fa ta soma tunanin yadda zata haɗa masa chocolate cake ita hasalima a suna kawai tasan cake ɗin,
Wuri ta samu saman ta zuƙunna ta shiga lalubar masa waya instead taje tayi aikin daya sata,
Gallery ɗinsa ta shiga madaddalar hotuna, na fa ta fara ganin haɗaɗɗunan pictures ɗin samarin familƴ ɗinsu hada waɗanda su kayi a ƙasashen waje,
A nan ne taga hotonan wannan haɗaɗɗen matashin saurayin mai shegen kyan nan, shi da junaid su kayi hoton a cikin jirgi da alama privet jet ne mallakinsu saboda su biyu ne acikinsa, sunyi hugging ɗin junansu fuskarsu ɗauke da murmushi,
wuce wa gaba tayi next picture nan fa ta ƙara ganin hotonsa cikin dandazon sojoji suna sara masa,
Ƙasa tayi ta shiga videos nan fa ta gane wa kanta zahiri,
Videos ɗinsa tagani kamar hauka da alama junaid na yinsa sosai,
ran ta yana bata cewa wannan ba kowa bane face BABBAN YAYA wato surgeon general RAFAYET,
ta jinjina wa matsayinsa ganin kowane video zakaga dubban sojoji ne turawa kewaye da shi suna taka masa baya, ko suna sara masa ,
tana cikin wannan laluban wayar ta soma ringing bin hoton da ya bayyana a calling ɗin tayi ,
zaro ido waje tayi tare da buɗe baki alamar mamaki, mutumin da take bibiya ynx haka shine ke kiransa a waya,
tunani ta soma yi ta yi ɗaga ko kar ta ɗaga ? katse wa kiran yayi wani kuma ya sake antayo wa wayr ta ci gaba da ringing,
Cikin tsananin tsoro da jin fargaba ta ɗaga tare da karawa a kunnanta bata ce komai ba, tayi shiru tana sauraronsa
abun da ya ɗaure mata kai shima bai ce komai ba ! hasalima alamu sun nuna cewa ya manta daya danna kiran saboda tajiyo hayaniya mutane ta cikin wayar alamar tattauna wa ake,
katsewa kiran yayi, janye wayar tayi daga kunnan ta ta zuba ma number ido da sunan da aka a jiki “My everything”
ta jima wurin zugudun tana kallo kamar daga sama taji muryar junaid
“An kammala haɗa min cake ɗin”
A firgice ta tashi zaune tana kallonsa tayi wuri wuri da ido tana mazurai,
Murmushi ya saki tare da miƙa mata hannu ya ce “Gimme my phone,”
cikin rawar murya tace”am..umm..dama ynx nake am..:
hannu yasa yayi mata alamar tayi shiru kafin yace its ok ba damu zan sa a kawo min ne kawai,’
ya faɗi hakan tare karban wayar ya shige ciki binsa da kallo tabi shi har ya 6ace wa ganin ta,
A cikin waɗannan kwanakin wata irin shakuwace ta shiga tsakaninta da junaid tarasa dalilin dayasa yake kyautatamata sannan abunda ke ɗaure mata kai ynx baya bari ta shigo ɗakinsa musamman inda ga shi sai shorts (gajeran wando) a jikinsa, abunda bata sani ba shine ya gane cewa ita macece da cen abunda yasa yake sakin jiki bai kunyar yin komai a gabanta saboda a tunaninsa namiji ce, ga shi kullum sai ya bata aron wayarsa ya ce ta buga game, waɗannan abubuwan na matuƙar ɗaure mata head,
Ba ƙaramin daɗin hakan taji ba, kullum sai sunyi waya dasu jahad da husanna, kullum sai tayi mata complain akan ta turo musu kuɗi sun gaji da talauci, tai ta faman basu hakauri akan su bata lokaci,
bata samun matsala da kowa ynx, tana taka tsantsan akan duk wani abu da zai sa a kore ta daga gidan, Mutunci tsakanin ta da azmi sai ƙara habbaka yake abun ba’a magana ta maida ta kamar auntyn ta ita ma haka azmi ta maida ta kamar yar cikinta ko nace ƙanwarta komai na tafiya dai dai,
A 6angaren su husanna kuwa dake cikin mawuyacin halin kamar kansu farau talauci, suna buƙatar agajin gaggawa domin maganungunan da doctor ya ba ta sun ƙare dole sai an samu ƙuɗi an siya mata wani,
don haka jahad ta yanke shawarar turama sehrish saƙo, a lokacin da message ɗin ya shiga wayar na hannun junaid,
Karantawa yayi kamar haka” sister maganin husanna fa sun ƙare akwai matsala tazama wata zararriya ta hana mu sakat pls ki taimaka mana,”
Koda junaid ya karanta message ɗin sai ya tura masu da “Send me your account number,’
ganin wannan saƙon cikin zumuɗi jahad ta zari hijabi don tashiga gidan makwabtansu saboda yarinyar gidan nada account number su nan basu dashi,
kafin ta dawo husanna tafarka daga bacci saboda cikinta daya katsa, ta soma laluben waya saboda toilet ɗin akwai duhu irin na gargajiyar nan ne ginin ƙasa, nan ta samu yar nokia ɗin da jahad ta ajiye a saman jakar kayansu taɗauka ta shiga da ita toilet ɗin, to ka’ida in ta kunna fitilar wayar ta zukunna sai ta fara buga game tana sukuni,