ABBAN SOJOJI BOOK 1 COMPLETE

ABBAN SOJOJI BOOK 1 COMPLETE

Ansha wahala sosai kafin alexandra ta kar6i musulunci, a inda sunanta ya canza daga Alexandra zuwa FATIMA, kowa yayi tunanin cewa tayi imani da Allah ne, ashe ita bada son rantaba takar6i addinin,
Takurawar abbace,

dalilin barin alexandra nigeria tsakaninta da mahaifiyarmu ne basu shiri, hajiyarmu ta tsane ta ba don komai ba sai don yadda take wahalar mata da ɗanta,

Duk in tazo abuja gidan abba sai sunyi cece ku ce, tun daga ranar da hajiyarmu ta buɗe baki tace ma Alexandra musuluncin ta ba kar6a66e bane, ta musulunta a banza domin kota mutu wuta zata shiga,

Ran Fatima ya 6aci sosai jin wannan maganar hakan yasa, ta koma addininta kai tsaye,
shiyasa ba a so in mutun ya shiryu arinƙa ƙyamatarsa ko kuma ana goranta masa, sbd gudun irin hakan ynx gashi ta koma yar gidan jiya, a ƙarshe da hajiyarmu ta Tsananta mata da baƙaƙen maganganu, ranta ya 6aci sosai

Wannan shine silar da fatima ta koma ƙasar Australlia da zama wurin danganin mahaifiyarta can sydney, babban tashin hankalin ma tabar masa jinjirin yaro batare da idasa shayar dashi ba,

Junaid yaga rayuwa, naso na ɗauke shi,amma azmee ta nuna cewa tana so ta shayar dashi, shiyasa nabarmata sbd nima ina shayar da talal da mahaifiyarsa ta bari,

Rafayet ya musulunta ne a sanadin omar, saboda duk ƙarshen wata donald yana kawosa su gaisa da mahaifinsa, a haka ahaka har suka ja ra’ayinsa duk da ansha wuya kafin asamu ya kar6a, abba yaji daɗi sosai a lokacin, shima kuma donald yayiwa abba alƙawarin cewa bazai ta6a takurawa rafayet akan addininsa ba, zai bashi ƙwarin guiwa duk da kasancewar shi mabiyin addinin catholic,

A lokacin abba ya haɗa rafayet da omar tare ya damƙawa donald ba don komai ba, sai don kukan da yake yi mashi akan yana son ya zauna kusa da ɗan uwansa, sun shaƙu sosai, duk in zasu rabu sai sunyi zazza6in rashin junansu,
Sannan kuma haɗa omar da rafayet ba ƙaramin ci gaba muka gani ba , domin shike juya rafayet, ya ja ra’ayinsa sosai akan musulunci yana ƙara nutsar dashi, yana tunasar dashi akan ibadarsa da kuma addininsa, da haka aka samu rafayet har ya sauke al’qur’ani mai girma, A shekarar daya musulunta kowa yayi mamakin hakan, duk da munsan cewa shi na musamman ne lu’u lu’u ne , mr donald yayi bajinta domin har yau muna ƙara jinjina masa kuma muna yi masa addu’ar Allah yasa ya musulunta dashi da yar uwarsa fatima,
Domin shi yayi ɗawainiyar su rafayet da marshal omar har suka kai wannan matsayin da suke a yanzu wanda duniya tasan dasu ,
Kuma shi da kansa yasama musu malamin addini wanda ke koyar dasu littattafan addini tun suna yaransu,

Tun wannan lokacin fatima bata ƙara taka nigeria ba, sai dai duk mai son ganinta yaje inda take,

Wannan shine takaitaccen labarin gidan Abban sojoji, Allah yasa an fahimta,
Jinjina kai aunty babba tayi tare da cewa “Allah ya jiƙan surukata, ya haskaka ƙabarinta,yasa Aljanna ce makomarta, da dukkan waɗanda su ka rasu Allah ya gafarta musu, Alfarmar annabi muhammad (SAW) ❤
gaba ɗayansu suka amsa da amin ,sannan ta ƙara da cewa “sannan muna yi ma fatima addu’ar Allah ya shirye ta, yasa ta gane gaskiya ɗaya ce, ya bata ikon musulunta, da ita da ɗan uwa Donald,’
Jikinsu twins da fawan yayi mugun sanyi, ta shi su kayi cikin wani irin yana yi zasu shige ciki…………………????????ABBAN SOJOJI????

mallakin HAFSAT BATURE????

     *BossLady*????

Subhanallah Walhamdulillah Allahu akhbar ☝️

page 49 to 50 ????

????Extraordinary Love????

general ishaq yace “kai ina zuwa? Maza ku dawo ku zauna, ku ka yana magani ne? ynx tsakanin ku da mahaifiyarku addu’ace kawai, that’s the only solution, in Allah yasa fatima zata musulunta ae ba wanda ya isa ya hana hakan,’

Cikin shesshekar kuka fawan yace”idan ta mutu fa ba tare da ta karbi addinin musulunci ba, azabar Allah zata tabbata akanta ne, kuma wuta zata shiga, aduk lokacin dana tuna wannan ina jin ƙunci araina…’
Ayaan ma yace “abba bai kyauta mana ba, kullum cikin zullumin makomar mahaifiyarmu muke,’
Jahan yace “kuma bata son mu, ta kama hanya tayi tafiyarta, ko waiwayan mu bata yi, ita wata irin uwace? cikin rashin tausayi ta tafi ta6ar ƙaninmu shi da bai mallaki hankalinsa ba, da tun farko Abba ya za6a mana uwa tagari munyi rayuwarmu cikin salama, da ynx labarin ba haka zai kasance ba,
“Kada na sake jin wani daga cikinku yayi magana, ku koma ku zauna, koba komai ae kuna da mu, wani irin gatane bamu nuna muku ba, mu fa jini ɗaya ne, babu wani banbanci a tsakanin mu ! ku kun kasance jinin dake yawo ajikinmu, kasancewarku farar fata ba hakan yana nufin kun fita daban acikin mu ba, kuma don mahaifiyarku ta tafi ta barku ba hakan yana nufin kun rasa wani sashe na jin daɗin rayuwarku ba,
Da ran mu da lafiyarmu bazamu ta6a bari hawayen ɗaya daga cikin ku ya zuba ba, Allah ya riga ya haɗa kuma ba wanda ya isa ya raba, nasan cewa abunda Ammy take yi muku bakwa jin daɗinsa, shine abunda yasa ku ke jin kan ku daban, to inaso kusancewa zumunci a tsakaninmu yanzu ya SOMA,

Wannan maganar ta yayansu Ishaq yasa su jin wani sanyi a ransu, har suka samu ƙwarin guiwar koma wa suka samu wuri suka zauna,

Suna cikin wannan zaman motoci suka soma antayowa cikin gidan da gudun gaske da wata irin jiniya, wannan alamu ne dake nuna cewa Salahuddeen hussein ya dawo wato chief of army staffs,
Farin ciki a wurinsu ba’a magana, Abbansu jigon rayuwarsu, backbone ɗinsu ya dawo cikin ƙoshin lafia,
Lokaci guda hayaniya ta kacame agidan manyan mutanen da suka zo tar6arsa ba adadi, sai faman marhaban lale ake yi, gidan ya cika fam da manyan mutane ko’ina ya ɗauka, su azmee da chef ummu da momina sai faman kai komo suke wurin rarraba musu abunsha,
Abban nasu ba ƙaramin daɗi yaji ba lokacin da yaga warriors soldiers ɗinsa cikin ƙoshin lafiya, murna a gunsa ba’a magana, sai dai har yanzu baiga Sanyin idaniyarsa ba, gashi ya matsu daya gansa, duk da ɗumbin mutanen dake kansa hakan bai hanasa ambaton sunan JUNAID ba, ❤

dakyar fa mutune suka lafa har abban yasamu damar shiga haɗaɗɗen bedroom ɗinsa, wanka ya shiga bayan ya fito ya kimtsa cikin jallabiya fara, kallon kansa yayi a cikin dressing mirror murmushi ya sakarwa kansa tare da cewa “ABBAN SOJOJI” a fili ya yi maganar,

Abba mutunne mai matuƙar daraja da cikar kamala, mutunne da kowa yake kwaɗayin haɗa iri dashi ba don komai ba sai don sanin kyawawan ɗabi’unsu, mutun ne dayasan darajar ɗan adam, yana da sauƙin kai sosai, hakan yasa naƙasa dashi ke prouding dashi a matsayinsu na shugabansu ❤

Mutunne mai matukar tausayi, hannunsa a buɗe suke indai wurin taimako ne baya gajiya, irin waɗanɗan mutanen na musamman ne su, domin suna da kishin ƙasarsu, shiyasa suke sadaukarwa kansu ga ƙasarsu, kowa zaiyi burin ya mallaki uba irinsa ????

Kwanciya yayi a saman katafaren king size bed ɗinsa, domin ya samu relief kafin ya wartsake ya gana da ƴa’ƴansa,

A can ciki kuwa kowa ya hallara a saman dining table domin gudanar da ɗa’amin, su azmee sun kammala jera komai, saving ɗinsu kawai suke kowa na faɗin abunda yake son ci, su kuma suna zuba masa,:

Cikin natsuwa kowa ke zubawa cikinsa, suna cikin cin abincin aunty azeema tace “wai ina baby junaid nifa na ƙosa na gansa, i really missed him so much,’ ta idasa maganar tana tura dambun naman da ta dumbuzo a hannunta, sam bata wasa da abinci,
Fawan yace “hmmm indai junaid ne ynx zaku gansa, yunwa ta koro sa, nasan yana cen rungume da pillow kamar jinjiri yana sharar bacci,’
gyaran murya Abbas yayi “idan ana cin abinci ba’a magana,’ ya faɗi cikin zolaya,
Amani tace “amma agida fa muna yi,” dariya su kayi gaba ɗayansu jin abunda tace,

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74Next page

Leave a Reply

Back to top button