ABBAN SOJOJI BOOK 1 COMPLETE

ABBAN SOJOJI BOOK 1 COMPLETE

Dakyar sound din ke fita , hakan ya tambatar masu da cewa so take tayi ma Sehrish magana amma takasa , matsawa sehrish tayi kusa da ita tare da sa hannu tana shafa mata gefen fuskarta cikin kuka tace “pls husanna kiyi hkr kinji Allah zai baki lafiya , nasan mai kike ji a zuciyarki, zanyi kokari koda zan rasa raina ne wurin ganin kin samu lfy , wlh sai inda karfina ya kare , ina sonki sosai my sister,” gaba dayansu kuka sukeyi , mayar mata da roban oxygen din Husanna tayi , bin ta su kayi da kallo ganin tana kokari kakaro murmushi a fuskarta , wani sabon kukan suka sake fashe wa dashi.

“Yar’uwata kada ki tafi kibarni ni nafiso na mutu a gabanku dan Allah kada ki tafi ,” lokacin da sehrish ta tuna da wannan kalami na Husanna sai jikinta ya kara mutuwa lukus , kamar ba kasusuwa a jikinta, zamewa tayi ta zauna kasan tiles din tare da jingina kanta gefen gadon , wasu abubuwa ta dinga tunawa arayuwarsu wanda in har taci gaba da tuna su to tabbas zuciyata zata buga ne! komai ya dawo masu sabo fal , komawa Jahad tayi ta zauna tana shesshekar kuka hada majina a hancinta ,
Hannun husanna taji cikin nata , dayake ta aza hannun nata a saman bed din, ta rike shi gam cikin nata , dagowa sehrish tayi da fuskanta wadda tayi jawur , ga idonta sun kada , fuskarta tayi kwaba kwaba cikin kasalalliyar murya tace “Husanna ki daina zubar da hwayenki nasani abun da ciwo , zafinsa yakai kunar wuta amma ki daure pls , ba irin whalar da bansha ba wurin ganin nasamu kudi an miki aikin nan ke da jahad especially ke , kai karshe ma an kokarin bada kaina nayi amma dana tuna abunda mama ta fada saina gaza , duk da haka ban hkr ba na soma kokarin samun wanda zai siye ni yabani kudi kawai na kawo muku ni natafi amma saina tuna cewa in na tafi wazai kula daku ? duk da nasan akwai Allah shine gatan kowane bawansa …’ muryarta ce tashaqe ta gaza idasa maganartata saboda kululun bakin ciki daya tokare mata makoshinta .

Jahad da ke sauraron maganar yar uwarta su sai taji wani sabon kukan ya balle mata, domin duk wannan gwagwarmayar da Sehrish tayi sam basu sani ba a boye tayi kayanta.

Sun sha kuka kamar ba gobe nima na tayasu kukan duk da bansan takaimaiman tarihin rayuwarsu ba da kuma dalilin kukan nasu.

A haka goggo da hajjaju suka same su gwanin ban tausayi , wayar hajjaju dake cikin yar purse dinta sai ringing take yi don haka tace ma serish ta taso su tafi , cikin kuka ta tashi a hankali take tafiya tana waiwayansu , goggo tace ” kada ki damu rishi hajjaju ta biya mana kudin gadon kuma tace zata samu koda bashi ne a fara biyan kudin aikin inyaso daga baya kin fara aikin kin samu sai ki biya,”
Ba karamin dadi sehrish taji ba , haka jahad ma godiya suka shiga yi mata , a karshe tayi masu sallama suka tafi ,
Har a cikin motan kuka takeyi dakyar hajjaju ta lallashe ta tayi shiru….

Time din da suka dawo , larai na kitchen ita da y’an matan kauyen nan tana koya masu wasu abubuwan daya kamata su sani.

A falon suka zauna gaba daya jikinsu a sanyaye, sehrish na zaune kasan carpet jingine da 2 seater , tana sauraron abunda hajjaju zata ce ,
magana ta soma mata “Sehrish ni yanzu bansan ya zanyi dake ba, game da aikin nan m, gashi ni already ina da y’ar aiki kuma gsky ko da ace ban da ita, ba zan iya daukarki sbd kina bukatar kudi masu yawa ni kuma iya salary din da nake biyan larai 10k ne.”
•·•·•·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·••·•·•·•·•·•·•·•·•·•
LAFAZI WRITERS ASSOCIATION ® ✍️
───────────────────────
Hafsat Bature
~(Boss Lady)~

Page 5-6

Jin wannan bayanin daga bakin hajajju yasa jikin Sehrish yin sanyi , bata ce mata komai ba sai ma ta ci gaba da wasa da yatsun hannunta. Ci gaba da magana hajajju tayi “abunda za’ae tunda dai naga sisters din naki kuma munyi magana da gwaggo da take kula daku , ynx ki koma ki ci gaba da kula dasu saboda suna bukatarki kafin Allah yasa asamu aikin ,”
Kamar an dasa ta haka tazauna idonta suka ciko da kwalla, kiris take jira ta fashe da kuka , dama bata jima da gama wancan kukan ba
Wayar dake hannun hajajju ce ta soma ringing , picking tayi tare da karawa a kunnan ta tana fadin ” Manyan manyan gari ! Abban sojoji ashe kana nan ba’a neman mu , koda yake dama ku hamshakan masu kudinnan ganin ku sai an cike file.”

Natsuwa sehrish tayi tana sauraranta , ta lura da yadda hajjaju ke washe baki da alama koma wanene take wayan dashi Babban mutum ne ,
tuna damuwar da take ciki yasa ta daina sauraron wayar tasu ta shiga tunani kala kala a cikin zuciyarta , har hajjajun ta kammala wayar bata sani ba sai da taji tace “Ga samu ga rashi !!” dagowa tayi da idonta tayi tana kallon , hannu hajjaju tasa ta dafe kanta alamar takaici.

Sehrish tace “Hajiya meya faru?” Hajajju tace “Aiki ya samu mai tsoka , jin hka yasa sehrish ta soma murmushi “amma sai dai kash Namiji suke so mai aiki ba mace ce ba !” lokacin da hajajju ta idasa maganar tuni sehrish ta gumtse fuska hankalinta ya tashi.

Hajjaju ta ci gaba da cewa “ina tayaki bakin ciki gsky, sbd kinga mutumin nan daya kira ni ba karamin mai arziki bane , cos they can pay u 50k as your salary after that zasu dauki dukkan responsibilities din ! Ci da shan ki wurin kwana lafiyayye sannan har school zasu iya saka ki ga sutura ya kike gani “?
Takaici ya hana tace komai ga samu ga rashi , ji take kamar ta cire takalmanta ta watsa da gudu saman titi kota rage radadin da take ji a zuciyanta ,
“Sehrish kinyi shiru baki ce komai ba “? ta jima ba tare da ta ce wani abu ba sai da tayi zurfin tunani kafin tace “ZanJe ! Zan yi aikin a matsayin NAMIJIN akan y’an uwana babu abunda bazan iya yi ba don nayi basaja a matsayin namiji wannan abune mai sauki a wurina ,”
In serious matter take mgnan ba tare da jin wani dar a zciyarta ba dagaske take dai , murmushi hajjaju tasaki don ba karamin burgeta tayi ba saboda tana da confidence akan komai da take so , ” hmmm sehrish kenan how can u change ur creator frm a girl to a boy i dont think u can act like a male zasu gane ki ne , “
Matsawa tayi kusa da hajiyar tare da rike kafarta tace “Don Allah hajiya ki taimake ni wlh zan iya , indai za’a samu makeup artist din da zai tsara ni ya mayar dani kamar namiji this is a simple thing , kawai amincewarki nake bukata,”
hannu hajjaju tasa ta cirewa Sehrish hannunta data rike mata leg dinta dashi sannan tace “Babbar magana ! tun da nake bantaba yin wannan kasadar ba , natura house maid mace a matsayin namiji , sannan wannan mutumin da kika ji ina magana akan sa wato Abban Sojoji , y’ay’ansa maza goma sha takwas kuma dukkansu sojoji ne masu rike da manyan mukamai , dalilin dayasa yace namiji suke so a matsayin d’an aiki saboda ba yadda za’ai mace ta iya , bai ma dace ba , balle ma yaransa da kwata kwata basa da sauki , zafin rai ga ji da isa , “
Kamar zata yi kuka ji take in har hajajju bata amince mata ba zata iya rasa ranta , cikin kasalalliyar murya tace “Hajiya ki amince mun kawai ae ni nace zan iya wlh idan baki amince ba shinkafar bera zanci kawai na mutu kowa ya huta don bazansu naga mutuwar y’an uwana ba , ” zaro ido hajajju tayi jin ta anbaci zata je taci shinkafr bera , kuma dagaske take ba alamar wasa a mgnrta ,
ruko hannunta tayi saboda harta mike zumbur zata figi hanya , “Meya yi zafi haka dawo ki zauna kinji , ni bazanso nayi sanadiyar mutuwar wannan innocent face din ba ,” komawa tayi ta zauna tana sauke ajiyar zuciya ,
Shiru suka yi na wani lokaci daga ita har hajajju , jin shirun yayi yawa yasa tace “Hajiya baki ce komai ba am so eargerly to hear frm u ,” ta karasa maganan tana kallon ta ,
Wan nan shirun da hajajju tayi sake sake takeyi a cikin zuciyarta “taya zan kai yarinyar nan gidan soldiers a matsayin namiji ! duk ranar da asiri mun ya tonu daga ni har ita kashin mu ya bushe , maganar da sehrish tayi ce ta dawo da ita , ” Sehrish i dont know what to do am just comfused ina tsoron hakan fa ,”
“Nima ina goyon bayan yarinyar nan” larai ce tayi maganar shigowarta kenan taji suna tattauna wa , bin ta su kayi da kallo , wuri ta samu ta zauna kafin taci gaba da magana “Wurin samun biyan bukata rai ba abakin komai ya ke ba , tun da har tace zata iya kawai ki amince mata ! saboda ni na taba kallon wani korean film irin haka actress din ciki ta yi shigar namiji ba tare da wani ya gane ta ba kuma tacimma nasara ,” jinjina kai hajajju tayi tare da watsa hannayen ta tace “Shikenan Finally i agree tunda har larai ta Jefa miki kuri’a kun rinjaye ni ,” dariya sukayi su duka ba karamin dadi sehrish taji ba , ynx hajajju ta yarje mata sauran shirin yarda abun zai kasance ,
Mayar da idon ta kan larai tayi tace “To ynx ta ina zamu fara “? Larai tace “ae magana ta kare kawai mu da muke da Professional makeup artist a hannu ko kin manta da Mariiiya ? murmushi hajajju tasaki tare da cewa ” ae Mareeya karshe ce ! Indai wurin canzawa mutun kamanni ne insha Allah gobe zan yi inviting din ta kuma a gobe za’a kammala komai don ya ce mun Jibi suke son mai aikin ta je ,”
Har larai ta bude baki zatayi magana ta jiyo muryar yaran nan dake cikin Kitchen wadanda take koyama aiki , suna kokoyi muryar d’aya daga cikinsu taji tana cewa “Aunty larai gatanan xata wanke gas cooker da ruwa ,” da sauri ta mike ta nufi hanyar kitchen din tana cewa “Allah ya wadaran naka ya lalace har waning nayi muku kada ku taba komai amma saboda kan kifi gare ku baku gane komai salon kujama mutane ko !?
Hajajju tace “ke ma da laifinki akan me zaki baro min su a kitchen salon suyi mun barna ,” mayar da idon ta tayi kan Sehrish “ki je ki huta time din sallah ma yayi nima bari na tashi ,”
Ta shi tayi ta shiga ciki , wanka tayi ta dauro alwala , ta fito ta shimfida prayer mat tayi sallah , kamar yarda ta sama kullum sai ta daga hannayenta tayi sama da 30mins tana rokon Allah cikin harshen larabci take jero addu’oin ta da bukatanta da damuwarta tana neman Allah ya yaye mata su ,
Bayan tagama ta tube hijabin ta ajiye , sannan ta hau saman bed ta kwanta dama jiya bata samu isasshen bacci ba , don haka lokaci guda bacci ya kwashe ta , tana cikin bacci y’an matan nan suka shigo , sai faman fadin wash Allah suke , koda sukayi arba da ita kwance ta baje gashi ta cire hijabin kan ba head tie, nan fa suka fara santin gashin kanta , ita dae bata son meke wakana ba tadai ji sama sama ana ja mata gashin kai ,
Zama sukayi kamar sun sami television sukai ta kallonta , ba karamin lalata sukayi ma kanta ba duk sun cukuikuye mata gashi yar kalaban nan sun warware mata ita , sun mai da karamar mahaukaciya ,
Nauyin bacci ne ya hana ta farka amma tabbas taji ana shafa mata kai kasa kasa ,
Sai da ana kiran sallan isha sannan ta farka , mika tayi tare da yin hamma , time din sun fita daga cikin bedroom zuciya sauko da legs dinta tayi kasan tiles din tana sauke ajiyar zuciya , kafin ta mike ta shiga toilet , tana cikin yin alwala tayi shafuwan kai ta shafo gashin kan ta mamaki ne ya kamata jin ba kitson dake kanta da sauri ta idasa alwalar ta je gaban mirror ita kanta sai da ta firgita da ganin yadda suka susuce mata gashinta , amma ba wannan bace damuwarta , zullumin kada husanna ta mutu da kuma aikin da zata fara ,
Zama taci gaba da yi a bedroom din , tana tunene tunane , ga yunwa tana ji amma takasa fita ta nema ,
Turo kofan sukayi suka shigo hannunsu dauke da tray abincin aka zuba musu shinkafa da miya ne sun cinye sun rage mata d’an kadan, ajiye mata sukayi suna dariya suka fice , abunda basu sani ba ita kallon Shashashu take masu ,
Bin a bincin tayi da kallon ba don tana jin yunwa ba da bazata ci Ba don sun jagula shi, haka ta zauna ta dinga turawa a baki kamar zatayi kuka , har dare yayi tana zullum abu daya kuma dashi ta kwana,
…………………………………ABBAN SOJOJI
…………………..Story by MrsBature
………………Part 1

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74Next page

Leave a Reply

Back to top button