ABBAN SOJOJI BOOK 1 COMPLETE

ABBAN SOJOJI BOOK 1 COMPLETE

Sehrish kuwa kamar matatta haka take kwance idonta luhu luhu, wasu siraran hawaye ne masu xafi ke saukar mata daga eyes ɗinta, haroon ya ƙuntata mata yasa ta tsani jikinta, ko’ina ƙyanƙyaminsa take ji,
Ga wani matsanancin ciwon kai da take fama dashi saboda kukan da tasha, ga zazza6i duk ita ɗaya, duk wannan bai hanata tunanin Sgr ba, shin yaci dinner ɗinsa kuwa, so take ta tashi taje ta dubasa amma tsoran karta haɗuwa da haroon ya hana ta fita,

Aunty azmee itace takai masa dinner ɗinsa a part ɗinsa, har ɗagowa yayi ya kalleta a tunaninsa mai aikin nan ne da akace masa maca ne, wanda yake so yakama hannu dumu dumu,

Wannan ke nan ????

Keeep sharing everywhere, kar a manta da comment ????????????????ABBAN SOJOJI????????????

~????Father Of soldiers????~

Page 92-93

ﻗﺼﺔ ﺣﺐ ﺭﻭﻣﺎﻧﺴﻴﺔ ﺑﻴﻦ ﺳﺤﺮﻳﺶ ﻭ ﺍﻟﺠﺮﺍﺡ ﺍﻟﻌﺎﻡ
ﺭﺍﻓﻴﺖ????????

✨Hafsat Bature
~BossLady~

Na canza days na sanya littafin abban sojoji, Ya koma Monday Tuesday da kuma friday????????

????????????

This novel part 2 will be paid book, a next post zan faɗi nawa ne payment ɗin????


A 6angaren su Hosana kuwa, tun da suka samu su kayi wanka suka yi alwala da sallah, basu yi kuskuren fitowa daga ɗakin ba, tsoransu kar wannan matar ta shigo basu son dame zata fara musu ba,

Yinin ranar cikin fargaba su kayi shi, suna ta faman zagaye zagaye a ɗakin, sallah ce kawai ke tsaida su,

Daga bisa ni bayan sallar Magrib ne bacci ya kwashe su a saman shimfiɗeɗen gadon dake ɗakin, sun sha gajiyar tafiya hakan yasa sukai ta sharar bacci kamar matattu,

A tsiyace Ta shigo da motarta acikin gidan, tayi parking ɗinta a wurin ajiye motocinsu, sannan ta harba murfin motar da ƙafarta don bala’i ta bude sannan ta fito,

Jikinta na sanye da less tsadadden gaske blue colour yasha adon duwatsu, less mai tsada amma an wulakanta shi wurin ɗinkinsa,

Riga da skirt ne rigar ta matse ta ƙam kamar zata tsage, wuyan rigar yayi girma sosai tamkar boob ɗinta zasu fito dukansu,

Skirt ɗin kuwa ya ɗameta over, ga wata uwar tsaga da akayi mashi tun daga guiwarta tsagar ta fara har ƙasan ƙafarta, kuma daga ciki batasa komai ba,

Hannunta na sanye da knuckle rings, mai kyan gaske Hancinta ma nasanye da Nose ring,
tana riƙe da purse A hannunta launin kayanta,

fuskarnan na sanye da Makeup hada eye lashes tasa na kanti tayi fixing,

bakin nan nata yasha uban jan baki red colour Sai faman taunar cingam take yi a tsiyace,

ɗaurin ɗan kwalin kanta kadae ya isa ya tabbatar maka da cewa bata da sauƙi,

Cike da yauƙi tashiga tafiya kwas kwas saboda ƙafarta na sanye da wasu matsiyatan high heels masu tsinin gaske,

Kai tsaye ta wuce bedroom ɗinta, hannu tasa ta turo kopan tana faɗin “am so tired ina buƙatar watsa ruwa naci abinci nayi wan……..’

Bata idasa ba saboda abunda tagani kamar a mafarki Yan mata saman gadonta suna bacci,

Hannunta tasa ta murza idonta donta tabbatarwa kanta abunda take gani aikuwa ta sheda hakan
A fili tace “Bura’ubancan !!! Yau akeyin ta wlh,”
Wurga purse ɗinta tayi saman gadon sannan ta fuce waje a tsiyace take kwalawa Aunty Babba kira
“Mom!! Mom!! Mommyyyyyy !!

A razane aunty babba ta fito daga bedroom ɗinta ta sauko down tana faɗin “Hafsat meya faru haka kke kwalamun kira haka ? yaushe kika shigo ne?

ta tambaya tana kallonta,
Uban tsoki taja tare da cewa “Mom duk ba wannan ba! Suwanene waɗancan yaran isassu dana gani kwance asaman bed ɗina? a faɗace tayi maganar tana riƙe qugu,

Aunty babba ta yatsina fuska tare da cewa “ni wlh sam nama manta dasu, wlh Omar ne ya kawomana tsintattun yara tagwaye wai su zauna tare damu acikin gidan nan na wani lokaci……….’

Zaro ido hafsat tayi tare da cewa “Jakar uban can kayyasa !! sai kika amince ke kuma !?

Babu respect hafsat take magana da mahaifiyarta koda yake dama ance magaji mafiyi,

Yarfa hannu aunty babba tayi tare da cewa “To ya kike so nayi !? Omar fa ne ! Na isa na hana shi yin iko da gidan yayansa ?

Jinjina kai hafsat tayi tare da cewa “aiko zasu ci ubansu wlh ! they’ll regret being here in this home !

“Ae bama sai kin faɗa ba, ynx dai am sorry my daughter nakai miki su bedroom ɗinki, nayi hakan saboda Omar yana nan ne shiyasa nayi musu amma ynx wancan Tsohon Store ɗin zan maidasu da zama ciki,”

Jinjina kai hafsat tayi tare dace “Can yafi dacewa dasu yanzu dae muje a fitar mun dasu daga bedroom ɗina, ni saina ma Canza bedsheet Allah, sannan ina jin yunwa hope kin shiryamin abinci na Mommy,” tayi maganar tana shafa ciki

Aunty babba tace “dolena ne wannan, yanzu muje ɗakin mu fitar dasu, kisamu kiyi wanka na shirya miki abinci kici,

Atare da aunty babba suka shiga cikin ɗakin, su hosana bayin Allah na kwance suna sharar bacci

hafsat tace “Eyyehh !! Banza tasamu an haye mun gadona ana sharar bacci, wlh nasan maganinsu,’

Tana faɗin hakan ta juya ta fita daga ɗakin izuwa parlor in da freezer take,

Murmushi aunty babba tayi don tasan me hafsat zata ɗauko,

Aikuwa sai gata hannunta ɗauke da Cool water har yasoma ice acikinsa cikin ƙatuwar bottle,

Dariya aunty babba ta fashe da ita, tana faɗin “Good my daughter hakan yayimun wlh,”

Cire murfin robar tayi batare da tausayi ba ta zazzaga musu ruwan mai matuƙar sanyi a jikinsu,

A firce jahad da hosana suka farka jin dirar ruwa mai sanyi ajikinsu, jahad na faɗin “innalallahi wa’inna ilahirrajin’un, muryarta tamkar zatayi kuka ita kuwa hosana fashe wa tayi da matsanancin kuka saboda bata son sanyi balle ita mai asthma, jikinta har wani irin kerma yake yi,
Ido luhu luhu yayi jawur daker suke kallon Aunty Babba da hafsat dake tsaye suna kallonsu,.
Hafsat tayi mamakin kamannin su iri ɗaya sak aranta tace “Ashe har ynx ana yin twins masu kama da juna haka, ba laifi suna da kyau,”
A fili kuma ta daka musu tsawa har sai da suka firgita Hosana ta ƙanƙame jahad don batason sauti mai ƙarfi,
“GET UP !!!! Maza a tasarmun daga gado na, ku sauko Mun haka nan ankawo mana mutane tsintattu cikin gida,’ tayi maganar tana yi musu alama da hannu na su sauko,
Jiki na rawa suka miƙe tare da saukowa daga saman gadon jikinsu na rawar ɗari saboda sanyin A.c ne ya haɗu da sanyin ruwan da Hafsat ta watsa musu,
Tsayawa su kayi a tsananin tsorace suna faman shessheƙar kuka,
Tsoki aunty babba tayi tare da cewa “ku biyo ni,”

Bin bayanta su kayi ta fuce dasu daga ɗakin, sunyi mamakin ganin suna ta faman tafiya acikin wata Corner na gidan,

Adai dai ƙopan wani Room ta tsayar dasu, hannu tasa ta riƙe handle ɗin kopar tare da buɗewa tace “To ƴan matan mama ga fa makwancin ku daga yau,’
Hankalin su ba ƙaramin tashi yayi ba domin kuwa, wani tsohon store ne na ajiyar kayan abinci, tarkace ne kamar hauka, jarkoki da galon aciki na manja dana mai da akai amfani dasu awargaje, Sun tsufa sunyi ƙura, ga buhun hunan Shinkafa dana gero dana fulawa duk gasunan, ƙasa kuwa sunkin doyoyoyi ne ajere da dankalin hausa dana turawa, da gunduwa gunduwar Albasa, babban tashin hankalin ɗakin ko fanka babu duk ƙura ga yanar girgizo har jikin bango, ga ƙwari kuma a ƙasan suna shawagi, Ga manyan drawers waɗan da ke a datse jikin bango da alama na ajiyar tarkace ne,’

“Uban me kuka tsaya kuna kallo kushi ga mana! Ko saina shigar daku ne !?
Basu yi mata musu ba jahad ta ruƙe hannun hosana suka shiga cikin store ɗin sannan aunty babba ta ƙara da cewa “daga yanzu nan ne wurin kwanan ku Kuma wurin zamanku, saboda baku da gurbi acikin gidan nan,”
ta faɗi hakan tare da turo kopan kuma tasanya Key ɗin dake ajiki tayi Locking ɗinta, ba damar fita kenan, ko taya mutun zai iya kwakkwaran Numfashi a ɗakin nan !? ????

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74Next page

Leave a Reply

Back to top button