ABBAN SOJOJI BOOK 1 COMPLETE

Tana cikin zuƙunno nan wani ƙaton kyankyaso mai fiffike yayi tsalle sai saman kanta, cikin firgici ta tashi a razane nan take wayar dake hannunta ta sulale daga hannunta ta faɗa cikin ramin masan Subhannallah,
Can ance a turo account number nan kuma wayar da suke da ita kwalli kwal ta faɗa cikin masai,
Zaro ido tayi tare da buɗe baki saboda tsoro, taji haushin kyankyasan nan har taji cewa bazata kyalesa ba dole ya mutu,
Nan suka shiga sintiri ita dashi shidai wings ke gare sa, ita kuma da ƙafa take binsa sai faman tashi sama yake yake yi tana binsa da gudu, hada ɗauko takalmi tana kokarin kwaɗesa,
Baki a washe jahad ta shigo ta samo account number ɗin yarinyar ta rubuta mata a farar paper,
ɗakinsu ta shiga tana neman waya, sama ko ƙasa babu ita ta shiga lalube ko’ina babu, tashiga mamakin ina aka kai wayar bayan babu,
tunawa tayi da cewa tabar husanna a kwance tana bacci tabbas tana wurinta , fita tayi cikin saurin tsakar gidan
Adai dai lokacin Husanna tafito tana sauke ajiyar zuciya tace”wash Allah da ace ban kashe shi ba dana binne kaina,’
“Husanna ina wayar nan take”?
jahad ta jefa mata tambaya ita bama ta lura da ita ba sai da tayi magana, nan fa tashiga wurga ido na mara gaskiya shiru tayi tana kallon ƙasa,
hakan ba ƙaramin tayarwa jahad da hankali yayi ba, saboda akwai abunda ko ba’a faɗa maka ba zaka fahimta ne ta yanayin mutun,????????ABBAN SOJOJI????
writer HAFSAT BATURE
~Boss Lady~
page 39 to 40 ????
jiki na rawa ta ƙarasa gabanta cike da tsoro tace” husanna ina waya ?
Shiru tayi tana mazurai, hannu jahad tasa ta shaƙo wuyan rigar dake jikinta cikin matsanancin tashin hankali ta sake cewa “tell me where did you kept it ?
muryar na rawa husanna tace” wani kyankyaso ne ya hau mun saman kaine shineee…sai wayr ta faɗa cikin….’
“Cikin Uban me !? jahad ta tambaya cikin daka mata tsawa,
duk tabi ta gama firgita tata cikin takura tace “cikin ramin”
Aikuwa rai a tsananin bace jahad ta shiga kai mata bugu ta ko’ina, nan suka shiga dambe, faɗa ya katse me a tsakaninsu kai kace basu son junansu,
A ƙarshe jahad tasake ta cikin tsananin ƙunar rai tace”shikenan kinyi farin ciki ko? kada kiyi tunanin ina bakin ciki ne don kin jefa waya, ina bakin ciki ne saboda kinyi mana babbar asara, taimakon da zamu samu na kuɗi a siya miki magani mun rasa, sannan ƴar uwarmu ma mun rasa ta ! saboda daga ni har ke ba wanda ya riƙe numbar da take kira, sannan ita inta kira zata ji waya a kashe kinga shikenan tamu ta ƙare…..’
Zuƙunnawa tayi tare da fashe wa da matsanancin kuka, itama husannar koma tayi ta tsaya jikin bango tana shesshekar kuka jin jahad tace sun rasa ƴar uwarsu SEHRISH
A cikin wannan yanayin mara daɗi tsohuwa ta same su, shigowa tayi hannunta ɗauke da bakar leda wadda fura ce aciki ta samo musu don su sha tun safe rabonsu da abinci har izuwa yanzu da ake ta faman kiran sallar isha’e
hankali a tashe ta ƙarasa inda jahad take tana faɗin”lafiya meya faru ƴa’ƴan ne me kke wa kuka? Nasan yunwa ce ku kwantar da hankalinku gashi nan na samo mana ƴar fura musha,’
Jin wannan maganartata yasa jahad ƙara sautin kukan nata, tana kuka tana magana “ba wannan zararriyar bace nasamu sehrish tace mu tura mata acct number, nashiga gidan makwabtan mu wurin mamee nace taban nata acct number ɗin, sai da na anso ina shigo wa nasamu husanna wai ta jefa wayar cikin masai,”
Jin wannan maganar yasa tsohuwa sakin ledar furar dake hannunta, tashiga tafa hannu tana faɗin “Innalallahi wa’inna ilaihirraji’un shikenan ae kun gama dani shekara 10 kenan wayarnan da ita nake lallabawa ashe kune ajalinta, kun kyauta,’
tana faɗin hakanan ta shige cikin ƙuƙuƙun ɗakin nata ta rufo kopa, tunda suka ga hakan yatabbatar masu da cewa ran tsohuwa ya bace, saboda bata taba yi musu haka ba,
Gashi ɗaki ɗayane a gidan ɗayan ɗakin ya rushe sakamakon ruwan sama da akayi,
ga wani irin sanyi a wajen nan da nan jikin husanna ya soma kakarwa, hankali a tashe jahad ta tashi daga zukunnawar da tayi ta tunkare ta,
“zo muje mu lallashe ta tabuɗe mana ɗakin mu kwanta waje sanyi,”
Haka suka je bakin kopan ɗakin sukai ta kwankwasa wa amma tsohuwa tayi shiru babu alamar zata buɗe,
A ƙarshe sai dai suka rungume junansu suka ƙanƙame juna saboda sanyin dake akwai, wannan abun ya tuna musu da wani lokaci daya shuɗe a rayuwarsu mara daɗin ji ????
Rashin gata baiyi ba a duniya
Story by (Hafsat Bature)
Rashin kwanciyar hankali yasa ko kwakkwaran bacci bata samu ba a daren jiya, tunaninta meyasa samu wayar tsohuwa ba’a samu tayi tarying amma swich off, hakan na matuƙar tayar mata da hankali tsoronta kar ace wani abu ya same su su duka,
Jiki a sanyaye ta kammala shiryawa ta wuce kitchen wurin azmi,
“Good morning aunty azmi”
ta faɗa tana kallonta, azmi dake faman gyare gyare a kitchen ɗin tace “morning baturiya hope u slept well”
yar dariya sehrish tayi ta shiga daga ciki tana faɗin “dame zamu fara ne?
Azmi tace “yau fa akwai manyan baki da zasu zo,”
dafe ƙirji sehrish tayi kamar wadda taji mugun abu tace”suwa!”?
dariya axmi tayi ganin yadda ta ɗan raxana,
“suna da yawa wasu yau zasu zo wasu sai gobe, daga ciki akwai chief of army staff wato Abban su junaid wanda zai dawo daga ƙasar chaina, amma shi gobe ne zai zo yau dai wasu daga cikin manyan ƴa’ƴansa dake other states ɗin zasu zo domin tarbarsa,
Da buɗan bakin sehrish sai cewa tayi “Babban yaya fa shi bazai zo ba,”?
girgiza kai azmi tayi tace”oh shirt! ni wannan babban yayan da kike ta faman zumuɗin gani bansan dalili ba,’
“Aunty azmi it’s just a question ba wani abu ba, naji kince manyan ƴa’ƴansa shiyasa na tambaya,’ ta ƙara maganar tana wasa da yatsun hannunta,
Kafin azmi tace wani abu junaid ya shigo da sallama, nan fa sehrish ta hau satar kallonsa yayi fes abunsa yayi dressing cikin suit black colour
A cikin zuciyarta tace “wai madarar kyau”
“Morning azmi how was everthing” ya faɗa shima yana ɗan satar kallon sehrish,
Azmi tace “barka dai komai lafiya kana buƙatar wani abu ne”_?
sam baiji me tace ba domin idonsa nakan sehrish wadda ita ma shi take kallo,
Sai da ta maimaita da cewa”junaid ina magana”?
a ɗan firgice ya mayar da kwayar idonsa kan azmi da ɗan murmushi yace” am dama nazo na sanar miki da cewa sai gobe jirginsu abba zai sauka, sannan jibi babban yaya tare da marshall Omar da Captain suma zasu taso, “
Saboda tsananin zumuɗi sehrish tasa hannu a baki irin mamakin nan ga wani farin ciki daya baibayeta kai kace tasan shi ne,
Junaid ya ci gaba da cewa “kada kusha wahalar yin aiki, akwai ma’aikata da zasu zo daga company zasu tsara komai ku hutu kawai,’
yagama faɗan hakan tare da juyawa ya fice,
Ita kanta azmi murmushi kawai take yi ba don komai ba sai don ta ƙosa sehrish taga wanene wannan babban yayan da take ta zumuɗi a kansa, tayi tunanin ganinsa abune mai sauƙi , mutumin da saboda tsabagen zafin rai ko magana bayayi saboda abu kaɗan ke 6ata masa rai,
“Yanzu hankalin ki zai kwanta tunda kinji cewa babban yaya zai dawo ko “?
murmushi sehrish tayi ita kanta tana mamakin wannan zumuɗin nasan ganinsa
tunda aka sanar da su cewa Babban yayansu zai dawo next tomorrow saboda kiɗima ranar ko breakfast basu ci ba, ba inda suka je kowa zullumi yake yi ba don komai ba sai don tsoransa,
a bangaren su twins kuwa suna a bedroom ɗinsu sai faman safa da marya suke yi yau ba harka, duk hankalisu ya tashi su sunsan mezai faru a zuwan Babban yayansu,
cike da damuwa Ayaan yace”gsky jahan am gonna cut my hairs today if not babban yaya will accuse something about us am afraid of him seriously,”
Ya faɗi hakan tare da zama a side bed ɗin yana kallon Jahan wanda ke faman zarya frm well to well yana haɗe hands ɗinsa yana naushin su atare,
“just feels like to cry wlh, Ayaan i dont wanna see him, am really scared of his eyes, mutumin da ko haɗa ido kukayi dashi sai gaban ka ya faɗi, we must find the solution,
cikin damuwa ayaan yace “what is the solution now ? do u ave any plan?
wuri jahan ya samu ya zauna gefensa tare da cewa “yanke gashi da kace zaka yi is not the solution, sbd shima yana tara doguwar suma ,ayaan kasan bama iya rayuwa even one hour without having sex , and if he finds out about it we are already doomed,”
Zugum su kayi kowa na tunanin yadda zasu 6ullowa lamarin,
Can Jahan yace “me zai hana mu kama room a hotel ? when ever we are horny we can go there hakan yayi ?
Jinjina kai Ayaan yayi ganin jahan ya kawo shawara ruƙo hannunsa yayi tare da cewa “thats why i love u so much cos you’re very smart hakan yayi,’
murmushi jahan yayi yana kallon cikin idonsa ya ce “since i found the solution ynx sai muje mu ci abinci ko? ko ba kajin yunwa?
Ayaan ya ce “Am starving too let’s go nd ave something to eat”
A tare suka fito
Tabbas jin zuwan baban yayan nasu ba ƙaramin kashe musu jiki yayi ba domin duk wanda yasan yana aikata ba dai dai ba neman takansa yake yi,
cleaners ɗin da aka ɗauko daga company sun hallara kuma sun fara gudanar da aikinsu, wasu parts aka buɗe wanda ita kanta sehrish batasan da zaman su a katafaren gidan gidan ba ,
ta dai san akwai wuraren dake a rufe bata taba ganinsa a buɗe ba, kamar other parlours ɗin dake a gidan amma yau ko’ina buɗe sa ake yi muraren saboda gyara,
Bayan sun kammala aiki ta shiga neman junaid saboda ta damu da rashin su husanna tana damuwa sosai,
ganin sai faman zarya take yi daga upstair zuwa down ga ma’aikata sai fama aikace aikace suke,
“Zonan sehrish” azmi ta kira ta alokacin itama ta shigo babban parlourn ita kuma sehrish tana saukowa down ƙarasawa tayi gaban ta tana faɗin “gani aunty azmi”
Azmi tace”lafiya kike ta faman yawa ce yawace baki ganin ma’aikata na aiki ne”? ta tambaya tana kallonta,
“Junaid nake nema ne” ta bata amsa, azmi tace i don’t think yana kusa ki koma ɗakin ki idan ya dawo i will inform you,’
Amsawa tayi da toh sannan ta wuce izuwa room ɗinta, kasa zama tayi sai faman safa da marwa take burinta taji wani hali su husanna suke ta damu da son jin hakan,
tana cikin wannan zagayen ta dinga jin jiniyar shigowar motoci kamar hauka, har sai da gabanta ya faɗi rass, cikin sauri ta ƙarasa gaban window ɗinta ta janye curtain ɗin jiki ta zuge glass ɗin tana leƙen abunda ke wakana a waje,
motoci ne na sojoji ke ta faman antayowa ciki, sanye cikin uniform ɗinsu, kowanne hannunsa sanƙame da jibga jibgan bindigu, wani irin miyau ta shiga haɗiye wa saboda tsananin tsoro, kamar mara gasky kamar ita suka zo kamawa,
Sakin labulen tayi ta koma ciki ta ci gaba da zagayen tana zare ido, abubuwa dayawa suna zuwa mata aranta damuwarta shine yaya zatayi idan suka gane cewa ita mace ce? tana tsoran waɗanda zasu zo musamman abbansu chief of army staffs da kuma surgeon general rafayet ga marshall Omer tare da Captain Adams da zasu zo daga outside country , gashi taji hada sauran ƴa’ƴansa waɗan da batasani ba, wasu ma anan garin suke wasu kuma na other states,
Yinin ranar cikin fargaba tayi shi, ga tunanin wani hali su husanna ke ciki ga kuma tunanin zuwansu Abban sojoji,
A bangaren junaid kuwa ya jira yaga ko zasu turo masa account number yaji shiru ba text message a time ɗin yayi niyar ya tura masu 300k duk da baisan ko su wanene ba, amma yana ji aransa cewa siblings ɗin Sehrish ne,
Jahad & Husanna
Abunda ya faru daren jiya A waje suka kwana, cikin dare jikin husanna yayi tsanani sosai saboda weather din akwai sanyi and she’s athmatic, haka ta rinƙa tari jikinta har jijjiga ya ke yi, hankalin Jahad ba ƙaramin tashi yayi ba, tana rungume a jikinta, wani irin ajiyar zuciya taji husanna na saki wanda bata ta6a jin irin hakan ba, a hankali ta kira sunanta “Husanna!”_.
Cikin wata irin galabaitacciyar murya tace”mutuwa zanyi baki ji yadda ni ke ji ba, dan Allah idan kin haɗu da sehrish ki ce mata ta yafe min ke ma ki yafe min nasan najima ina 6ata maku rai…….’