ABBAN SOJOJI BOOK 1 COMPLETE

“Junaid menene haka wai”? Abbansu ne ke yi masa magana da bacci a idonsa, junaid dake saman chair ɗin dake gaban mirror sai faman zabga murmushi yake ya juyo ya kalli abban nasu dake kwance saman gadonsu yace “Abba u will not understand it, Abba kasan yadda so ke shiga ? Yayi tambayar yana kallon Abban nasu,
Cike da takaici yace “Junaid taso kazo ka kwanta kayi bacci tunkan raina ya 6aci,’
“Hmmmm dad kenan ka ta6a ganin inda Romeo yayi bacci ayayin da yake tunanin Juliet ɗinsa,”
shiru Abban yayi yana kallon ikon Allah lamarin junaid ya fara bashi tsoro, shi burin shi ya taso su kwanta amma junaid ya ƙiya, gashi in baiyi bacci da wuri ba daker ake tashin shi bacci wurin sallar asuba,
Hannu Abban yasa ya daki katifar gadon da ƙarfi yace” Zaka taso ko bazaka taso ba”
Fari junaid yayi wa Abban nasu da ido, irin farin da mata keyi na ido yace” Daddy kaima kayi tunanin mommy mana, Nima nayi tunanin juliet ɗita,
BossLady ???? in kinaso ki saka mun kawai kimun share na novel ɗina ???????????? sannan In zakuyimun comment pls ba thanks nakeso naji mutun yace mun ba, kawai kimun comment da abunda ya burgeki ko wanda ya baki haushi, komai dae ????????????????????ABBAN SOJOJI????????????
????the father Soldiers????
mallakin
????Hafsat Bature Moh’d????
Episode 85-86-87
◻ “To rasa kunya 6eran tanka zaka fara mun tsokanar taka ko,”?
◻ junaid yace “ae gaskiya na faɗa Abba, kallon ka kawai nake yi kai ta shan ƙamshi kamar baka son momynmu alhalin ko rannan kana bacci cikin mafarki naji kana cewa bana ji bana gani ni makaho ne agame da sonki Momyn junaid in bake ba sai rijiya in na rasa ki zan rungumi transformer akanki zan iya tunkararrrr
◻ bai idasa ba saboda jin saukar pillow din da abban nasu ya wurgo mashi, tabbas junaid ya bawa abban nasu dariya sosai
◻ “Kai ko? Yaushe akai hakan junaid Ƙaraya kke mun,” ya faɗi yana kara janyo Wani pillow ya wurga masa, hannu junaid yasanya ya ca6e pillow ɗin da Abban nasu ya wurgo masa a ƙinjinsa ya rungumesa yana faɗin “thank u Abbana dole na gode maka domin gashi da hannunka ka miƙo mun juliet ɗita,” ya faɗi hakan yana shafa filon dake ƙirjinsa yayin da yake kallon fuskarshi cikin madubin gabansa,
◻ Jin shiru Abban nasu bai sake cewa komai ba, yasanya junaid juyowa da kallonsa, samun sa yayi zaune tsakiyar gadon kansa na kallon ƙasa Allamar da damuwa a fuskarshi,
◻ tasowa junaid yayi jiki asanyayye ya haye saman gadon in da abban nasu yake yace “Abbana meya faru naga kashiga wani yanayi na damuwa,”?
◻ ɗagowa Abban yayi ya kallesa cikin sanyin murya yace “Junaid momynku ! kasan bana 6oye maka komai kaine abokin sirrina, babu wanda ke fahimtar zuciyata kamar kai,” ya dakata da maganar yana dan jinjina kai,
◻ “Dad pls tell me may be i ave the solution of it,”
◻ “Junaid mom ɗinku ta azabtar dani da soyayyarta, junaid ita tace tana so na tun kafin na fara sonta, amma kalli ynx ta kama hanya da aure na akanta ta koma australlia da zama, junaid ya zanyi?
◻ gyara zama junaid yayi suna fuskantar juna kamar zaiyi maganar arziki sai cewa “Abba dole sai ita? Ga zankaɗa zankaɗan mata nan ƴan goma shatakwas ƴan shila kyawawan gaske masu neman sugar daddy irinka wlh abba har rububinka zasu yi ka share ta kawai ka auri wata,” in serious matter junaid yake magana,
◻ Takaici ya hana abban magana a tunaninsa junaid zai bashi shawara akan yadda zasuyi mom ɗinsu ta dawo wurinsu da zama, amma sai ga akasin hakan, in banda sangartaccen irin junaid waye zaiso ayiwa uwarsa kishiya”
◻ “Abba u didnt say anything, shawarata batayi bane,?.
◻ “Eh junaid batayi ba, ashe baka da hankali in rasa wa zanyiwa kishiya sae momynku, bakasan halinta bane, duk da bamu tare da ita amma tayimun gargaɗin cewa muddin na ƙara aure sai ta dasa Bomb acikin gidan kowa ma ya rasa,”
◻ Fashewa da dariya junaid yayi, abban nasu yaci gaba da cewa “kuma in banda abunka wani magidanci ne mai ƴa’ƴa irinsu Sgr da Marshal Omar zai kara aure, auren ma ƴar shekara sha takwas ae wlh a ranar da ta sa ƙafarta acikin gidan nan aranar zasu balla ta gutsi gutsi
◻ Dariya kawai junaid yake kwasa wato ta ko’ina ba sauƙi, ita mommy tace zata dasa bomb su kuma su Babban yaya in an kawo ta gidan 6arar gyaɗa zasu yi mata,.
◻ “Enough junaid dariyar ta isa haka, zan baka lokaci daga yau zuwa gobe kayi tunanin shawarar da zaka bani akan yadda zamu shawo kan momynku ta dawo nan da zama,”
◻ “Kana nufin muyi mata wayau abba,”?
◻ ɗan zaro ido abban yayi tare da cewa “kai ! wannan matar mai ɗan banzan wayau kamar dila tab ae banta6a ganin dakakkiyar mata ba irin momynku ae wannan ba wanda ya isa ya yayi mata wayau,
◻ Dariya su kayi gaba ɗayansu sun jima suna fira kafin su kwanta tare Abban yayi musu addu’a yabi ya shafe su duka,
◻ _________________________________
◻ ƙaramar yarinya ce wadda bazata gaza shekara 12 ba ke tafama gudun saman titi sai faman kuka takeyi tana ambaton sunan “Oumma !! Oumma !!! ba tare da ta lura ba wata ƙatuwar motar ƙirar range rover tayi awon gaba da ita, nan take kanta ya fashe jini ya soma kwaranyo wa ta ko’ina
◻ A firgice sehrish ta farka daga mummunan mafarkin da take yi murya na rawa ta furta “Innalallahi wa’ina ilaihirraji’un,” ta faɗi tana cusa hannunta cikin sumar kanta idonta sunyi jawur hawaye na bulbulowa daga cikinsu, tabbas ta tsorata da mafarkin da tayi,
◻ Jiki a mace ta tashi ta wuce toilet saboda lokacin sallama yayi, sai da ta watsa ruwa sannan ta ɗaura alwala ta fito tana ta faman sauke ajiyar zuciya,
◻ Wardrobe ta buɗe ta dauko hijab ɗinta ta shimfiɗa sallaya ta kabbara sallah, bayan ta kammala ta zauna saman sallayar ta ɗaga hannayenta tana addu’o’i,
◻ Bayan ta kammala komawa tayi ta kwanta saman bed batare da ta cire hijab ɗin ba, haƙiƙa mafarkin ɗazu da tayi ya tuna mata wani abu mummuna daya ta6a faruwa makamancinsa,
◻ Ta jima hawaye na gangarowa daga eyes ɗinta kafin wani baccin ya sake ɗauke ta, ba ita ta farka ba har sae wurin ƙarfe tara, jiki na rawa ta shirya kamar kullum ta wuce kitchen,
◻ tsayawa tayi tana zazzare ido ganin har azmee ta kammala breakfast ɗin, wanda zata je ta jera a dining kawai take shiryawa,
◻ “Ina kwana aunty azmee,” tayi maganar tana ƴa kame kame, murmushi azmee tayi tare da cewa “Lafiya lou reesh, fatan kin tashi lpy,”
◻ “Aunty azmee ai mun afwa ban fito da wuri ba,”
◻ “Bakomai sehrish nifa da so samu ne ki koma kawai room ɗinki na kawo miki breakfast ɗinki ki ci acan ba sai kinyi wani aiki ba,”
◻ murmushi sehrish tayi tare da cewa “hakan bazaiyiyu ba auntyna, nima bana so nabar miki aiki dayawa ke kaɗai,
◻ Sehrish tayi maganar tare da ƙarasawa ciki domin ta taya azmee shirya abincin da zasu jera,
◻ Kamar daga sama ya faɗo kitchen ɗin daga shi sai shorts ajikinsa ba riga,
◻ gaba ɗayansu sai da gabansu ya faɗi ganinsa kwatsam haka ba sallama,
◻ daker azmee ta iya cewa “wata sabon gani haroon yaushe ka dawo ne ? Amma dae saukar dare kayi ko,”? Ta tambaya tana kallon shi
◻ idasa shiga yayi yana sakin murmushi yace “Eh jiya da daddare na iso, nayi mamaki da banganki ba auntyna gaskiya i really missed u, nayi kewar delicious ɗinnan naki,
◻ da ƴar dariya a fuska azmee tace” ae yanzu tunda ka dawo sai ka dasa daga inda ka tsaya, halan yanzu ma yunwace ta koro ka,?
◻ “Eh auntyna fruits nake so da coffee haka ko tea, pls a shirya mun sannan abawa wannan mai aikin yakawo mun,” yayi magana yana kallon sehrish wadda tunda ya shigo gabanta ke faɗuwa tarasa dalilin hakan,
◻ “Shikenan yanzu zan bashi ya kawo maka,”
◻ Murmushi ya saki tare da juyawa ya fuce daga kitchen ɗin,
◻ “Wanene wannan aunty azmee”? Sehrish ta tambaya domin neman ƙarin bayani akansa,
◻ Azmee tace “Wannan haroon kenan, ki saki jiki dashi bai da wata matsala a iya sani na, shima ɗayane daga cikin matasan gidan nan,”
◻ ɗan ta6e baki sehrish tayi tare da jinjina kai tace ” Allah yasa bai da wata matsala,” aranta kuma tace “sam ni baiyi mun kama da sauran ba, hasalima duk sun fishi kyau da natsuwa,”
◻ Ba da son ranta ba azmee ta shirya mata fruit a tray da cup na coffee takai masa,
◻ sai da tabi kwatancen da azmee tayi mata sannan ta gano room ɗinsa a nan down yake kusa dana kanal yusif,”
◻ a bude tasamu kopan sallama ta kwala masa daga ciki taji ance “Come in,”
◻ Shiga ciki tayi gabanta na faɗuwa rass rass, daga kwance yake saman haɗaɗɗen gadonsa ya taso zaune yana ƙare mata kallo,
◻ Cike da girmamawa sehrish tace “Gm sir,”
◻ bai amsa mata ba har ta ajiye masa fruits ɗin asaman table ɗin dake a front ɗinsa,
◻ Cikin sauri tajuya zata fita muryarsa ta katse ta”na sallame ka ne,”? Jiki a mace ta dawo ta tsaya daga tsaye tare da sunnar dakai tana kallon yatsun hanunta da take wasa dasu,
◻ Jin shiru yasa ta ɗan dago ta kallesa samun shi tayi yana bin jikinta da wani irin matsiyacin kallo tundaga kan yatsun ƙafarta har izuwa ƙirjinta,
◻ Hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba, ita burinta ya sallame ta tawuce taje wurin dining don ta taya aunty azmee ga kuma son sanya Babban yaya da take yi a idonta,
◻ Ganin ya tsayar da idonsa a gaban wandon jikinta yasanya tsigar jikinta tashi,
◻ da buɗar bakinsa sai cewa yayi “ina Ak47 ɗinka take, don ni banga alamarta ba anan,”?
◻ Cike da rashin farintar me yake nufi sehrish tace “bangane me kke nufi ba,”
◻ Wani shu’umin murnushi haroon ya saki tare da kai hannu cikin tray ɗin da takawo masa ya ɗauko damin Banana ya cire guda tare da sa hannu yana 6are bawon ayabar yace “Ina nufin wannan,” yayi nuni da ayabar dake hannunsa,.
◻ Jigum sehrish tayi sam tagaza fahimtar me haroon ke nufi, ganin bata da niyar bashi amsa yasa shi cewa “ina nufin abu na maza wannan,” yayi maganar yana ruƙo abunsa dake cikin shorts ɗin jikinsa,.
◻ Zaro ido sehrish tayi gabanta na faɗuwa zuciyarta tayi mugun tashi ganin abunda yake nuna mata sai lokacin ta gane me yake nufi ma,
◻ Shiru tayi idonta na kallon ƙasa gabanta na faɗuwa
◻ “A cire mun wando inaso nagani na shaida,”
◻ Ya faɗi ayayin da yake kai ayabar hannunsaa cikin bakinsa yana gatsa yana ci,
◻ Ji tayi gaba ɗaya komai ya tsaya mata tsak, tabbas ta tsorata da haroon sosae tun da take aiki a gidan bawanda ya ta6a lura da hakan farat ɗaya sai shi,
◻ “Baza a cire ba,!? ya tambaya a fusace
◻ Cikin en ena sehrish tace “kayi hkr dan Allah ! amma baxan iya yin abunda kke so ba……,” kafin ta idasa maganar tuni yasanya hanunshi yaja zariyar wandonta nan take wandon ya tafi suuuuuuuuuu zai sabule jiki na rawa ta cafko shi tayi saurin maidashi ta ɗaure abunta a yayin da zufa ke wanko mata,
◻ Dariya haroon yayi kafin ya tsagaita yace “Ke !!! nifa tun jiya dana ganki nasan cewa Ke maca ce ba namiji ba !!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!!
◻ ɗagowa da ido sehrish tayi a firgice tana kallonsa tamkar a mafarki take jin kalaman haroon .
◻ Ƙara jaddada mata yayi da cewa “Ke maca ce ba namiji ba !! ki faɗamin uban miyasa kikayi shigar namiji kika zo gidannan? Da kwai wata manufa aranki ko !!?
◻ Muryar na rawa sehrish tace “innalallahi wa’inna ilaihirraji’una!! taya akai ka gane cewa Ni maca ce farat ɗaya!?
◻ Dariya haroon yayi tare da cewa “saboda ni Shu’umi ne ! Kuma cikakken ɗan duniya wanda idonsa ya buɗe a harkar barikanci ! ba wani abu da mutun zai 6oye mun batare dana gano sa ba,”
◻ “Shikenan nashiga ukuna !! dan Allah ka rufemun asiri karka ce zaka tona cewa ni maca ce pls!!
◻ Ajiye ayabar dake hannunsa yayi cikin tray ɗin sannan yace “Okey, i won’t expose ur secret but under one condition!!?.
◻ Ya faɗi yana kallonta a raunane sehrish tace “koma meye zanyi nidai karka tona mun asiri,” tuni idonta ya ciko tab da kwalla,
◻ Har wani lumshe ido haroon yake yi yana kallonta ” share hawayenki baby, bani da matsala muddin za’a biyamun buƙatata,’
◻ shiru sehrish tayi tana sauraron shi
◻ “Zamuyi magana anjima yanzu zaki iya tafiya naga kuna cikin aiki ne,”
◻ tunkan ya idasa mgnr sehrish ta fuce tana shasshekar kuka ,
◻ sai da ta dakata bayan ta fita ta tsaya ta share hawayenta tare da dai dai ta natsuwarta sannan ta sauka ƙasa, anan ta samu ma Aunty azmeen tana jera musu breakfast ɗin a dining,
◻ Karasawa tayi suka ji gaba da jerawa atare,
◻ Kallonta azmee tayi tare da cewa “Naga kin jima ! Lapiya dae ko?
◻ “Eh,” ta bata amsa atakaice, ita kaɗae tasan yadda take ji aranta, brain ɗinta ta gama shiga ruɗu tashiga tashin hankali mamakinta taya akai farat ɗaya haroon ya gane cewa ita maca ce !? how many days ta share a gidan amma ba wanda ya ta6a lura in aka cire junaid sai shi wanda jiya jiyan nan yazo da daddare, tabbas abun ya ɗaure mata kai, kuma tasa mishi alamar tambaya, (?) Anya ba Aljani bane