ABBAN SOJOJI BOOK 1 COMPLETE

________________________________ABBAN SOJOJI
Story by Hafsat Bature
BossLady????????????
Around 12 Abban su ya dawo cikin gidan time ɗin duk sunyi bacci, bai wuce ɗakinsa ba sai da ya fara zuwa part ɗin Marshal Omar domin yaga ɗansa kafin ya wuce nasa ɗakin, lokacin daya tura kopan part ɗinsa shima nashi sak irin na Sgr ne, akwai hamshaƙin ƙayataccen palor aciki sai bedroom aciki,
Wuce wa bedroom ɗinsa yayi ya shiga Ciki samun shi yayi saman shimfiɗeɗen gadonsa ya lullu6e da lallausan blanket ɗinsa,
Murmushi Abbansu yayi tare da cewa “Yawwa haka nakeso my son asha bacci lafiya,” juyawa yayi zai fita Muryar Omar ta ratsa shi da cewa “Abbana idona biyu fa, i ave told u that i wll be waiting to ave ur hug, that’s why i stayed awake,’
Omar ne yayi maganar a yayin da yasanya hannunsa yana janye Bargonsa ya miƙe zaune da murmushi a face ɗinsa,”
Ƙarasawa Abban yayi Omar ya tashi tsaye suka rungume juna ssae,
“Nayi missing ɗin Tiger ɗina ssae, ” ya faɗi yana bubbuga bayansa, Omar yace “Abbana nima haka, ina fata nasame ka lpy,”
“Lpy lou Alhamdulillah Omar,” ya yi maganar tare da janye jikinsa daga na Omar yana cewa “Ka koma ka kwanta Omar nima zan wuce ɗaki ynx,”
“Shikenan Abba, Mu tashi lpy,”
Sallama su kayi abban ya fice, kwanciya Omar yayi amma yana jin there’s something missing a heart ɗinsa tabbas akwai wanda baisa a idonsa ba, tun da ya dawo cikin gidan ba kowa bane face “Junaid,” ya bari ne kawai sae gobe ya neme shi su gaisa cos yyi missing ɗinshi,”
Sehrish fa sam ta gaza runtse eyes ɗinta tayi bacci, duk ta takure kanta ta tsani jikin ta, ta6awar da haroon yayi mata ji take tamkar raping ɗinta yayi, tana saman gadon daga kwance ta tashi zaune tsakiyar gadon, ta matse kanta baiwar Allah,
_______________/_/
Time ɗin da Abban su ya shiga ɗakinsa, yayi tunanin zai ga junaid a kwance yana sharar bacci, amma sai yaga wayam daga blanket sai pillow asaman gadon, abun ya ɗaure masa kansa, aransa ya ce “meyasa Junaid bai zo ya kwanta bane wai, ko dae yana a bedroom ɗinsa bara dae na canza kaya naje na duba sa,”
Shaf shaf ya cire kakin dake jikinsa, ya shiga toilet ya watsa ruwa ya fito ya zura jallabiya fara, sannan ya fice daga room ɗinsa izuwa na junaid dake a upstairs,
Yana isa ya tura kopan ɗakinsa abun mamaki babu junaid babu alamarsa, har toilet ɗinsa ya duba babu Shi saboda tsabar ruɗu har cikin Laundry basket ɗinsa ya duba da cikin Wardrobe ɗinsa don yaga ko ya 6uya aciki ????
Amma babu shi, aikuwa hankali atashe abban su ya fito ya wuce part ɗin sgr, ya shiga har ɗakinsa ya bubbuga masa jikin ƙoparsa,
Sgr dake kwance natse saman gadonsa yaji knocing ɗin da abban ke masa,
Janye bargon jikinsa yayi, sannan ya tashi zaune yana kallon Abban nasu daker yake buɗe Eyes ɗinsa saboda bacci,
A sanyaye yace “Abba me ya faru ne? Kai ne da kanka?
“Ina fa lafiya babu junaid fa acikin gidan nan”! Jin hakan yasa sgr yin saurin haurowa ya sauko daga saman gadon, jikinsa na sanye da night dress riga ce dai dai guiwarsa ta tsaya babu dogon wando sai dai shorts acan ciki,
Cikin ruɗu yace “Abba kamarya? How za’ace junaid baya cikin gidan nan!!!? ya tmby yana kallon abban nasu dake a tsaye,
“Nima bansani ba, dawowa ta kenan, gsky akwai matsala,’
Fito wa su kayi atare shida abban suka bi sauran bedrooms ɗin sauran saboda su duba su gani ko ya kwana a ɗakin sauran saboda yana yin haka in rigimarshi ta tashi sai ya za6i inda yake so ya kwana ko ɗakin waye kuma dole abarsa ya kwanta,
Duk wanda akayi wa knocing ya buɗe daga yaji cewa Junaid ake nema sai kaga ya wartsake daga baccin da yake yi, hankalin kowa ya tashi matuƙa,
Gaba ɗayansu duk suka hallara a babban falon in ka cire Marshal saboda basu tashe shi ba tunda shi ranar ya dawo baisan wainar da ake toyawa ba Sai haroon,
Duk sukayi tsaye cirko cirko sai faman hammar bacci suke yi,
“A cikin ku wayasan inda Junaid yaje !!? Abban su ne ya tambaye su,
Kowa sai faman murxa ido yake yana hammar bacci,
Haɗa baki su kayi wurin cewa “Abban bamu San inda yake ba wlh,”
Tsawa sgr ya daka musu har sai da suka ɗan firgita yace “wannan wane irin shashanci ne ace junaid yabar gidan nan batare da kun sani ba har yakai wannan time ɗin a waje baku lura ba,!”?
Murya na rawa Su twins suka haɗa baki wurin cewa “Junaid fa baya zuwa ko’ina kowa yasani yana cikin gida kullum sai dae wani abun daban,”
“Nima a iya sani na kenan gsky akwai matsala* acewar fawan
Jabeer da Irfan suka ce “mun fa lura baya cikin gidan nan, amma gaba ɗayanmu munyi tunanin yana ɗakin Abba yana bacci shiyasa mukayi shiru,”
Bin su da kallo kawai sgr yake yi suma kallon shi suke yi suna kora bayani,
“Yakamata ajaraba kiran layinsa mana aji inda yake” acewar Khaleed, cikin sauri kanal yusif ya zaro wayarsa dake cikin aljihun wandon baccinsa,
Contact ya shiga ya dubo numbar junaid wadda yayi saving da Last Born Ya danna masa kira ta soma ringing,
Gaba ɗaya koya ya saurara yana jiran amsa kira daga junaid, 3 times tana ringing junaid bai ɗaga ba,
Hakan yasa kanal yusif yin amfani da wayarsa wurin duba location ɗin Inda wayar take,
Gaba ɗaya kowa na jiran tsammani, kanal yusif yace "kai ! Location ɗin fa ya nuna cewa wayar tana acikin gidan nan that means junaid yana acikin gidan kenan ko yabar wayar tashi a bedroom ɗinsa ne,
cikin hanzari su fawan suka haye upstars shi da su twins domin su duba ɗakin junaid koyana nan,
A tsiyace suka tura ƙopan ɗakin suka shiga cike da tsammanin ganinsa amma sai suka ga wayam, sae wayarsa dake ajiye saman Pillow bisa gadonsa, hakan na nufin gida yabarta,
Duk basu ji daɗin hakan ba, jiki amace suka sauko down ɗin har haɗa baki suke keyi wurin tambayar Su ina junaid ɗin ? Suka amsa musu da cewa basu ganshi ba sai dae wayar shi kawai,
“I know u will not see him cos i ave checked his bedroom already ya Ilahi,” acewar Abbansu ya faɗi cikin tsananin damuwa,
Hankalin kowa fa ya tashi, bazaman lpy ba Romeo ba junaid ba last born, ba shagwa6a boy Ba dole kowa ya rasa natsuwa,
“nasan inda yake ni,”
Atare suka ɗago don suga wanene haroon ne wanda fitowarsa kenan daga shi sai gajeran wando ajikinsa,
Har haɗa baki suke yi wurin cewa “Yana Ina!?
“Abada cin hanci a ɗauko muku shi,” kai kana ganinsa kasan yasha ya bugu idon nan sunyi jawur kamar na mujiya sai tangyaɗi yake yi,
Tsoki suka ja atare,
Abbansu ya daka mishi tsawa “Haroon kadaina mun wannan wasan kasan inda yake ne ko baka Sani ba _”!!!
Haroon yace “Billahil Azeemu na tsarance da rabbus sama’wati wal’ard nasan inda junaid yake, in ku kayi haƙuri kuka sa salama azuciyarku yanzun nan zan ɗauko muku shi,”
gaba ɗaya mamaki ne ya kamasu su kace shikenan “Muna jira,”
Juyawa haroon yayi ya nufi hanyar ɗakinsa yana faɗin "saboda wannan ɗan shilan duk kun bi kun tashe mutane Fil laili..........
Shigewa bedroom ɗinsa yayi yana ƙunƙuni,
Su kuwa zama su kayi suna ta faman jiran haroon ya fito musu da junaid,”
Jimmm kaɗan sai gashi ya fito hannun shi ruƙe da Pillow yana tangal tangal,
Zuba ido su kayi suna kallon ikon Allah, haroon na ƙarasowa ya shiga ƙoƙarin tu6e rigar pillown yana cewa “Yawwwa ynx zaku ga shegen ya faɗo daga cikin pillown ae nan cikin ya 6uya ja’irin,’
Rai a6ace har haɗa hannu suka yi Babban yaya da Abbansu suka sharara mashi zafafan maruka , daga shi har filon kowa yayi ƙasa baje,
Ihu haroon yasaki tare da cewa “Eeeeeeee !!!huuu!!!huuuu !!! waman ƙadarallahu haƙƙa ƙadrihi yanzu abba daga abun arxiki zan nuna muku inda junaid ya 6oye sai kawai naji saukar maruka? Yaron nan fa akan idona ya shige cikin rigar filon nan ya 6uya amma shikenan bakomai,’
Abun haushi abun takaici, banza kowa yayi dashi suka shiga tattauna yarda za’a yi a nemo junaid,
Kanal yusif yace “ina ga bari naje na sanarwa Azmee wata’ƙil tasan inda yake,
“A’a bana tunanin hakan, kwarama wannan mai aikin tukur raina yana bani cewa suna shiri sosai da junaid wata’ƙil shi yasan inda yake tunda kusan shine tsaransa,” acewar Abban su