ABIN DUHU COMPLETE NOVEL

Daga group na:-
???? HAUSA NOVELS????
☎ 08034691340
???? ABIN DUHU????
????????????
Na
FAUZIYYA D SULAIMAN
PAGE
2⃣2⃣
ta kara riqe hannun husna hawaye hawaye mai ciwo naci gaba da wanke idon tana magana . husna dazan iya da bazan gaya miki ba dazan daure da bazan gayama kowa ba amman bazan iyaba wlh ko ganin abdul ban qaunar yi bana buqatarsa nayi dana sanin kallon fuskarsa da saninsa ki taimakamini kiyi mini abinda ko dana rabu dashi daddy ya yarda ya amince ya karbeni ba tare da tashin hankaliba yar uwata yaddah take magana cikin haqiqancewa ke qara tada hankalin husna tafi kowa sanin wa ece hasana tanada naci da qoqari akan duk wani abu data sanya a gabanta amman a qasan ranta tunanine fal akan meyene ya sameta anya bayan abunda suke tsanmani babu abinda ke damun hasna tace ki gaya mini menen dalilin abinda ya sanya bakison zama da dakta a yanxu hasna banajin zan iya taimaka miki da komai ba tare da nasan menene dalilinkiba ko kinason duniya ta zagemune husna ce ke fadin hakan domin sake tabbatar da abinda ranta ke zargi babu wanda zai zargemu daman ni nace ina soshi yanxu kuma nace bana sonshi meye laifi a ciki ni bai mini komaiba kawai dai bana sonshi…ki taimaka mini don allah saita fashe da kuka hankalin husna ya sake dukunzuma tayaya mutum zai aikata abinda babu dalili koda zata yaddah ta goyama yar uwarta baya to sai ya zamto akwai hujja ? ta kula babu wani abinda abdul yai mata kamar dai yaddah ya fadanne wataqila gamon tayi saidai ta yaya zata tabbatar da hakan shine abu mai wuya amman bari ta gwadata ta gyara zama taci gaba da magana jiya waye ya daukoki a wurin aikinki? tambayar tazoma hasna a bazata amman saita daure fuska kwarai da gaske tana fadin maiya sanya kikace haka?motar haya na hawo mana amman kamar naji ance motar offis dinku ne ta kawoki gida wai baki da lfy ko husna ta. wurga mata tambayar cikin gaggawa tace eeh hakane na mantane wlh direban offis dinmne ya kawoni har kofar gida…tana maganar. cikin inda inda hisna ta tsareta da ido uhmm bayan nan kuma sai meya faru ki gaya mini wataqila zamu iya gano dalilin rabuwar takune ta haka cikin fargaba tace babu abinda ya faru kawai naji na tsaneshine….ki daina mini wani kallo idan ba zaki taimaka mini ba kawai ki gaya mini banasonshi banason zama dashi husna tace wata qila bakyayin addu,a lokacin fitarki da sauran abubuwanki ne ko, ya kamata ki miqa lamuranki ga allah hasna amman tabbas wani abu ya faru dake a daren jia inaji a jikina ko kinyi gamo da wani abu cikin daren… babu abinda na hadu dashi wai kinanufin na sami matsala ko aljani ya shafeni to karki sanya wannan cikin ranki komai bai sameniba babu komai wlh cikin sauri da tashin hankali take maganar husna ta miqe tsaye tanaci gaba da kallonta ni zan tafi don babu abinda zan iya miki a halin yanxu banda addu,a amman tabbas akwai matsala a tattare dake saidai ki sani bazan goyi bayan ki kashe aurenki ki rabu da mijinkiba abu na qarshe da zan fada miki shine kiyi wani tunanin amman ba wannan ba domin ki sani daddy ya sanar dake ya amince ki auri abdull amman babu ke babu rabuwa dashi ko sanar da wani cikin ahalinsa wani mugun lbr game da auren ku kokin manta a hakanne ganin ta kasayin maganane yasa husna ta gyara lullubinta tana fadin ni zan tafi amman don allah kiyi haquri kici gaba da addu,a akan komai sannan ki baima mijinki irin kulawar da kika saba bashi hasna ta kauda kai gefe tana magana batason hada udo da yar uwar tata na gaya miki bazan sake zama a gidannan ba yaya kuma zaki dinga fadamin wannan maganar tunda kin sanar dani mafita ki tafi kawai abinki yanayin yaddah take maganar shi yafi baima husna mamaki ba abinda take fadinba ta kura mata ido amman ba ta waigo ta kalleta ba husna ta kada kai tayi hanyar fita har takai bakin kofa bata qara cewa komai ba sannan bata waigo ta kalleta ba abin ya qara girmama a wajen husna duk sanda taxo gidan yar uwar tata idan zata tafi har bakin mota take kaita kamar karsu rabu da juna amman yau ta kasa tashi ta rakata koda bakin kofane sanna ko kallonta taqiyi ta isa ta tsaya a bakin kofar ta waigo ta kalli hasna tananan a cikin halin data barta saita girgiza kai kawai ta fice daga cikin dakin hasna tayi zaune hawaye yaci gaba da wanke mata idanu shin wani mataki ya kamata ta dauka yanxu………………
Daga group na:-
???? HAUSA NOVELS????
☎ 08034691340
???? ABIN DUHU????
????????????
Na
FAUZIYYA D SULAIMAN
PAGE
2⃣3⃣
abdull ya zauna yai tagumi yaga fitowar husna ya miqe da sauri ya nufeta tai masa alama da su fita daga waje saida suka nufi harabar gidan sannan suka tsaya cikin damuwa ta fara magana dakta babu wani abu daya taba zuciyar hasna kuwa? maganar taxo masa a bazata har ta sanya shakku da damuwa a cikin ransa amman saiya dake yace ta gaya miki wani abu ne?ta kada kai gamida fadin a,a bata fadamin komai ba don nama lura kamar bata da abin fadi kawai dai akwai wani abu daya tabata kamar yaddah kace dinne na tambayekane domin tabbatar da babu komai din. tayi shiru cikin damuwa ta kasa qarisa abinda tai niyyar fadi ya fuskanci akwai wani abu da bata fada masaba cikin irin dabara ta mai ilmi yacci gaba dayi mata magana husna ko akwai wani abu da baki fadamin bane ? don allah ki sanar dani komai karki boye min husna tai ajiyar zuciya sannan taci gaba da magana kalmomin da take fadane sunyi zafi da yawa rokona take akan na taimaka mata ta rabu dakai …hankalinsa ya qara tashi cikin damuwa ya e rabuwA?hasna ce ta fadi haka da bakinta?ta daga kai alamar eh haka ta tayi shiru yanayinta,yadan canja cikin damuwa sannan taci gaba da magana zan tafi ni amman zan fara biyawa ta gida na sanar da mommy abinda ake ciki cikin sauri ya katseta yana fadin a,a karki aikata haka husna banason kowa yasan da wannan matsalarr kema dan babu yaddah zanyine kawai na sanar dake amman in allah ya yardda zan shawo kan matsalar da kaina shikenan zan wuceni zan tabaka a waya tayi hanyar fita cikin gaggawa abdull ya bita da kallo harta fice sannan ya maida hankalinsa kan hanyar dakin hasna daga cikin anguwarsu aka fara kiraye kirayen sallar la,asar ba yaddah ya iya dole yaje yai sallar don haka ya nufi dakinsa domin dauro alwala kamar jira take ya fita masallacin kawai ta hau shiri ba wata shararriyar kwalliya tayiba dovuwar riga kawai ta saka da gyalenta ta dauki makullin mota ta fice dukda tanajin yinwa da tashin zuciya amman hakan bai hanata fitan ba koda mai gadi ya hangota saida yayi dan dumm domin tayi kama da wacce tai shekaru tana jinya mai gadi na mata magana amman ko kulashi batai ba kai tsaye asibitinsu ta nufa dakta ya dawo gidan kamar wanda akace ya kalli gurin kai tsaye inda motar hasna ke ajiye ya kalla sai yaga babu motar sai ya kalli bangaren mai gadi ya fara kwala masa kira mai gadi ya fito cikin sauri a gigice yana amsawa ina hasna ta tafi shine tambayar daya farama mai gadin wacce ta bashi mamaki gamida rikitashi ta yaya shi zaisan inda hasna ta tafi amman cikin kokari yace ranka ya dade wallahi. bansan inda ta tafi ba naga dai ta fita kamar mara lfy sai a sannan ya tina a inda yai tambayar ba muhallinta bane don haka cikin sauri yace ok babu damuwa sai yayi hanyar cikin gidan cikin gaggawa mai gadi ya bishi da kallo tabbas daga daren jia zuwa yau ya fahimci akwai abinda ke faruwa a gidan amman dai abinda babu ruwanka akace dadin kallo garesa abdull kai tsaye yana shiga wayarsa ya dauka ya fara qoqarin kiran hasna kiran hajiyarsa data shigo wayarce ta sanya ya fasa kiran layin hasnar yai ajiyar zuciya cikin damuwa sai a sannan ya tuna yau kwata kwata bai kira taba tunda yake bai taba kwana ya tashi ba tare da yayi kiran wayar mahaifiyarsa sama da sau biyar,ba gidanta kuwa qa,idane dole sai yaje kullum kafin ya tafi makaranta da sanda zai dawo amman yau gaba daya bai aikata ko daya ba dole hankalinta ya tashi saida ya bari har saida kiran ta yanke sannan ya kirata domin a qa,idarsa bai taba amsa kirantaba yafison ace shine ya kirata da kansa don baison ya cinye mata kudin wayar tata sai dayayi kokarin tattaro dakiya da dauriya ya sanya a ransa sannan ya fara yin mata magana cikin daria tuba nake hajia ta yau ban kirakiba ko? daga bangarenta ta bata fuska tace kaxo inason ganinka magana ta waya bazai gamsar daniba gabansa ya yanke ya fadi. cikin ransa fadi yake na shiga uku amman a fili saiya dake yace mata shikenan ganinan zuwa kafin yakaiga qarayin magana ta kashe wayar tata………………