ABIN DUHU COMPLETE NOVEL

Daga group na:-
???? HAUSA NOVELS????
☎ 08034691340
???? ABIN DUHU????
????????????
Na
FAUZIYYA D SULAIMAN
PAGE
2⃣4⃣
wannan ne ya qara tasar masa da hankali abin ya zame masa biyu ga matsalar hasna gata mahaifiyarsa amman yafi damuwa dason sanin inda hasna taje yanxu domin bata cikin hayyacinta bai kamata a ace tayi driven ba ya fara daddana wayarsa ya kara a kunne wayar ta fara qara amman abin mamaki sai yaga wayar tata akan kujerar falon hankalinsa ya qara tashi saiya kara kiran daya layin nata kasancewar wayoyin biyune da ita itta kuma wannan a kashe take mai ya kamata yayi yanxu shine abinda zuciyarsa ke sanar dashi a tinaninsa hasna bata cikin hayyacinta komai zai iya faruwa da ita ya nufi dakinsa cikin gaggawa ya dauko makullin mota ya fita hasna kuwa kai tsaye asibiti ta nufa wurin likitansu tayi sa,a babu layi don mitum biyu ne suka shiga ta zama ta uku dakta buba wanda ya kasance likitansu yana zaune akan kujerarsa tana shiga suka gaisa ya fara tsokanarta da yar jarida iyayen sharri sai tayi yaqe kawai ta zauna hakanne ya tabbatar masa da bata da lfy saiya zamto serious ya gyra zaman medicated glass dinsa yana fadin yaya dai hajia hasna me yake damunki? cikin takaici ta fara magana likita. cikine dani na kuma gano hakanne a daren jia bayan nayi pregnant text likita ya gyada kai cikin damuwa sannan ya fara tambayarta amman bayan gwajin da kikai akwai wasu alamu da suka tabbatar miki da hakan ne? eh yanayin jikina ya sauya sannan ina yawaita jin tashin zuciya amman ban kawo kamai akaiba sai jia zaki kwanta yanxu ayi scanning domin tabbatarwa hasna ta mike cikin gaggawa tamkar jira take ta kwanta akan gadon dakta buba ya dauko na,urar da ake daurawa akan mara ya daura sannan ya fara mata scanning hankalin hasna da idonta yana kan dan allon computar tana kallon abinda ke fita daga cikinta bazata iya ganekomai ba domin halittar bata rigada ta zama mutum ba amman akwai alamun ciki a tattare da ita hakan ya qara tasar mata da hankali ya gama yo mata gwajin gamoda bata damar ta sauka ya fitar da sakamako sanna ya fararubutu akan takarda harya kammala idonta na kasa sanna ya miqa mata hasna ta amshi takardar tana ci gaba da kallon likitan ya qara gyara gilas dinsa sannan ya soma yi mata bayani ga sakamakon daya fitanan ya nuna akwai ciki na sati goma sha shida a jikinki hasna ta tsorata gamida waro ido tace wata hudu fa kenan dakta dakta buba ya gyada kai gamida dan murmushi bakiyi tsammanin hakanba ko hasna ta daga kai har ilokacin cikin tsoro da fargaba take banyi tsammaniba likita banma tsinkayi lamarinba sai,a daren jia likita ka taimakamin ta yaya zan rabu da cikinnan bana buqatarshi kwata kwata mamaki ya fito qarara kan fuskar dakta buba domin baiyi tsammanin jin wadannan kalaman daga bakin hasna ba shine tai mata awon cikinta na fari a asibitinsama ta haihuyasan irin yanayin da suka shiga na farin ciki dajin dadin a wancan lokacin koda yaushe tare da mijinta suke zuwa asibitin tunda yake baima taba ganinta taxo asibiti ita daya ba duk sanda zataxo tare da mijinta take zuwa yanA tarairayarta gamida bata kulawa na musamman ganin baice komai ba ya sany ta qara maimaita abindata fada a baya likita ko bakaji abinda nace bane bana buqatar cikinnan cikin kakkausar murya tayi maganar tundata shigo ya fuskanci da akwai matsala a tattare da ita to don haka ya zama dole yai amfani da matsayinsa na likita domin kwantar mata da hankali don haka cikin rarrashi ya fara magana .hasna kamar yaddah kika sani nan asibitin kudine amman muna iya kokarinmu wajen bin dokokin qasa da kuma tsarin da addininmu ya shimfida mana don haka idan har ciki baya zamto akwai matsala ba bama kokarin zubar dashi musamman daya kasance ke daya kika buqaci hakan ba tare da mijinki ba, abinda scaning ya nunamin ya nuna dan cikin naki yananan cikin koshin lfy bai kamata kiyi wani abu dazai taba lfyarsa ba idanma wani abune ya bata miki rai kiyi haquri kibar cikinnan kamar yaddah kika wayi gari kika tsincesa a jikinki namasan matsalar bazata wuce na tsoron karkiyi konika ba hakan ba wani matsala bane tunda kin yaye yaronki kuma kedashi da abinda ke cikin naki duk kuna cikin koshin lfy hasna ta bata fuska wannan lokacin don bata fahimci komai akan wannan lallashhin da ban bakin da dakta ke mata ba abinda ke ranta kawai shi take buqatar ayi mata don haka ta fara kokarin miqewa ba tar data qara cewa komai ba a cikin ranta tana data sanin zuwanta gurinsa sai a lokacinma taga matuqar wautar data aikata ya kula da abinda take shirinyi don haka ya dakatar da ita cikin gaggawa yana fadin haj hasna kiyi haquri na fihinci da akwai wani abu cikin ranki amman karkiyi amfani da bacin rai wurin daukar fansa akan abinda baiji bai ganiba bazata iya masa bAyanin halin da take cikib kuma tasan bazata iya gamsar dashi da duk bayanin da zatai masa ba don haka. yin shiru da barinsa a hakan yafi sauqi amman tayi qoqarin fadin na gode likita ta fice daga ofis din cikin gaggawa………………
Daga group na:-
???? HAUSA NOVELS????
☎ 08034691340
???? ABIN DUHU????
????????????
Na
FAUZIYYA D SULAIMAN
PAGE
2⃣5⃣
dazu Dakta Buba ya kira ni ya sanar da ni wai ta je asibitinsa akan tana son zubar da cikin da ke jikin ta, ya ya zan yi abokina gaya mini? Gaba daya ilimina da basirata sun toshe, na rasa abin da ya kamata nayi.” ‘ Murtala ya kalleshi cikin damuwa, kishin Hasna ya fara shigarsa, shine abokin Abdul na farko, shine mutumin da ya taimaka masa gurin neman rufin asirinsa tun farko, amman mai ya sanya a yanzu yake Kokarin nuna duk duniya babu wanda ya ke so kamar Hasna ne, ya kasa cewa komai>sai kallonsa kawai da yake yi. Kamar Abdul ya karanci abin da ke ransa sai ya fara roqonsa da magiya “Murtala ka sanni, ban saba alaka da mutane ba, shi ya sanya idan na shiga damuwa babu wanda na ke gayawa ya warware mini sai kai, k0 kuma mahaifiyata, a yanzu bana bukatar mahaifiyata ta ji komai game da abin da ke faruwa, hankalinta zai tashi fiye da nawa, zaman lafiyar iyalina shine nawa, ina son kasancewa cikin kwanciyar hankali kamar kai, bana son abin da zai shiga tsakanin aure na da rayuwata, ka taimaka mini don Allah Murtala.” Yanda ya ke maganar ya. sanya tausayinsa cika zuciyar Murtala har ya sare ya fara Magana. “Kace mini kasanar da yayarta,kuma da ta zo babu abin da ya ragu sai ma lalacewa da abin ya Kara yi k0? “Haka ne.” ya bashi amsa cikin gaggawa, Murtala ya dafa kafadarsa cikin lallashi yana fadin “Dole iyayanta su san labarin nan, dole ne, ka je ka sanar da su halin da take ciki, kada lamura su lalace abin yafi karfinka, ina ganin hakan ne kawai mafita.” Abdul yayi dan jim cikin Kokarin yadda da abin da Murtalan ya fada, yana kuma tinanin ta yanda ya kamata ya sanar da iyayan na ta. “Ka zo mu wuce cikin motata na kai ka gidan nasu.” Murtala ya fadi abin da ya warware masa damuwarsa. A Bangaran Hasna bayan ta shiga cikin gida ta fice daga cikin mota k0 tsayawa rufewa ba ta iya yi ba ta yi cikin gida a guje tana kuka, ta shiga dakinta na shiga uku, shine abin da ta ke fada a fili da zuciyarta, kai tsaye dakin baccin ta ta shiga ta fada bisa gado ta kara fashewa da kuka. Yanzu haka zata yi ta mu’amalar aure da Abdul bayan yana yi da Murtala, ashe dukkan Kaunar da sukewa juna ta haka ce, wannan wacce irin masifa ce komai ta ke yi su kawai ta ke gani cikin kwayar idonta, ta tashi tsaye ta dora hannu bisa kanta ta fara zagaya dakin, tana jin kamar ta kwala ihu k0 ta ji dadi, abin da ke bata mata rai a yanzu da yawa. Daga asibitin gidan su har asibitin Abdul sunqi yadda su zubar mata da cikin jikinta, bayan nan ba san ina za tatae ba, domin ba ta da wayewa akan iririn wadannan abubuwana nan abubuwan, yaya za ta yi da cikin jikinta, ta kai ta kawo har lokacin hannunta yana bisa kanta, sai zuciyarta ta fara tashi kamar yanda ta faro, kafin ta iya yin wani abu amai ya taho mata, ta nufi bandaki da gudu ta fara kelayawa. Babu komai cikin aman sai majina da dan ruwan da ta sha domin bata sanya komai cikin ta ba, kanta ya fara juyawa ta gaji da wahalar nan, juwa ta fara dibarta, amman bata yadda zuciyarta ta gaji ba, tinanin hanyar rabuwa da cikin jikinta ne kawai a ranta, tana nan zaune cikin bandakin wani tanani ya fado mata, sai ta fita cikin gagagawa daga bandakin ta nufi hanyar fita. Wayarta da ke kara tun dazu da ta kunna ta gagabaadaara, ta gane me kiran nanaa Husna cecedomin ta sanya mata kiranta daban, amman tatai dadagaawayariciagabaadaururina daawayarekeyiayasaa dadagaun fara Magana Husna ta fara rarrashinta da lallaBata, da kalaman nata tayi kokarin nuna mata kamar ta kamu da ciwon hauka, har ta furta mata kalmomin da suke tabbatar da hakan, wannan shine dalilin da ya sanya ta kashe wayar, domin da ta yi Kokarin fahimtar da ita lafiyarta Kalau sai ta nunaba ~ haka bane ba don haka ba ta ga amfanin amsa kiranta ba,tun da tana mata kallon mahaukaciya, bayan kiran Husna kira kala-kala yayi ta shigo mata wayarta, amman babu wanda ta dauka sai kiran da aka yi mata daga OfiS din su domin rashin ganinta, ta bayar da uzurin bata da laflya tun jiya. Kai tsaye kicin ta nufa ta fara neman abin da ta ke nema, amman sai ba ta gani ba, ta nufi kofar fita cikin gaggawa tana kwalawa mai aikinta kira…………