ABIN DUHU COMPLETE NOVEL

Daga group na:-
???? HAUSA NOVELS????
☎ 08034691340
???? ABIN DUHU????
????????????
PAGE
0⃣2⃣
saita dake batace komai ba. Husna ta zauna a kusa da ita tana murmushi tace “Don Allah na tambaye ki sister. me kika mora daga satfiya zuwa yanxu. bayan tsawon lokacin da ki ka Bata kina kwalliya?” Ta hade rai Kwarai da gaske “Ban gane me kike nufi ba, ki min gwari-gwari”. Husna ta sake yin murmushi, tace. “Tun asubar fari da ki ka‘yi sallar asuba ‘ki ‘ka kasa komawa bacci, kina ta tananin irin kwalliyar da ya dace kiyi, har shirin naki ya kai safiya wanda ya ja mana yin lattii ya kuma sanya ki ka rasa lacca mai muhinmanci. shi nake tambayarki, me ki ka cinma? Hasna taja tsaki. ta kau da kanta gefe “Ke kika sani don ban san amsar wannan doguwar tambayar taki ba”. “Idan ba ki sani ba bari na sanar dake. Hasna ta kalleta da sauri kamar za ta yi magana. sai kuma ta fasa ta yi shiru. Husna ta ci gaba da “Ni ‘yar uwarki ce da muka rayu ciki daya, muka kuma fito duniya rana daya, ya kamata na fahimci dukkan halin DA kike ciki kin jima kinason DR Abduljabbar falmata Amman kin Gaza sanar Dani hasna ta kauda Kai DA sauri idanunta ya sake cikowa DA kwalla tace injiwa niba haka baneba husnah tai murmushi ta tashi ta durqusa a gaban hasna tana kallon fuskarta data kauda gefe tace wallahi hakane kinji na rantse abinda baki saniba har a cikin barcinki sunansa kike Kira na barkine na gani KO zaki sanar Dani halin DA kike ciki Amman zuwa yanxu na gane bani DA wannan matsayin hasna ta goge fuskarta dake xubda hawaye ta Fara magana cikin rawar murya kada Ki Kara daukan haka yar uwata duk duniya bani DA kamarki tare muka rayu tun a cikin ummanmu muka fito duniya mukaci gaba DA rayuwa tare saidai Ina ganin kamar abin kunyane a gareni furtawa wani cewa inason wani DA namijin dabai damu daniba buyan akwai mazan dake sona kamar suyi hauka. Wannan ke sanya ni kasa gaya miki ba komai ba”. Husna ta girgiza kai,”Na gamsu da bayaninki, amma ina son ki sanya a ranki Dr. Abduljabbar ba kowa bane da za ki kasa samunsa ba, duk da mata da yawa na sonshi a makarantar nan, amma ke son da ki ke masa na daban ne sai dai ba zan so ki bayyana kanki gare shi da sunan soyayya ba, ki kama kanki, ki riKi masu sonki k0 da Dr. Abduljabbar ya soki ma son ba shi da wani amfani a gare ki, k0 kin manta kina gab da zama’matar Abba ne‘?” Ta daga ido ta kalli Husna gabanta ya yanke ya fadi Sam ta manta da wani Abba, son Abduljabbar-ya makantar da idanunta har tana ganin shi ne kadai namiji a duniya. Husna ta Ci ‘ gaba da DR “Abduljabbar ba kowa ba ne ki tuna, Abba yaf1 shi komai daga kyau har gata har nasaba, k0 ba kiji sunanshi bane Abduljabbar Falmata Hakan yana nuna ba shi da uba, shi ‘ya sanya ya ke amfani da sunan mamarsa hasna ta rage murya har lokacin idanunta bai daina zubda hawayeba tace husna KO wanene Abduljabbar inasonshi inhar zai yarda ya soni koda dariyarsace ta wadatar husna tace mata DA yawa na fatan hakan saidai daria abace Mai tsada DA wahala a garesa bandama so bahaguwace me zai hada zuciyarki data Abduljabbar mutuminda baya daria baya Fara,a baya mu,amala DA Kowa hatta a cikin Yan uwansa malamai ya fita daban ga shegen girman kan tsiya Ki barshi haka don Allah Ki masa uzuri sister hasna ta fadi DA sauri husna ta gyada Kai shikenan Ki tashi mu koma dan muna dabda shiga political comunication kin sani hasna ta miqe jikinta babu kwari ji take kamar tabi bayan DR Abduljabbar haka hasna ta wuni sukuku batajin dadin komai burinta kawai ta qara gani KO giftawar DR Abduljabbar Amman bata ganiba har suka tashi daga lacca din nasu gaba Daya husna ce ke tuqa motar don ta Lura yar uwar tata tana cikin damuwa bazata Iya aiwatar DA komai ba gabda fitarsu babban gate hasna ta hango motar Abduljabbar daga gefe yana jinkine a jikinta kusa dashi wani mutum ne DA bazai wuce shekarunsaba suna hira cikin nishadi DA daria DA sauri ta taba husna tana sister kalli Abduljabbar yana daria yau yayi daria kin taba ganinsa haka? husna ta kalli inda hasna ta nuna mata mamaki ya cikata don’ bata taba ganinsa yana daria ba Amman batace komaiba ganin yaddah yar uwar tata ta kidime tsaya don Allah tsaya mu kalleshi sosai husna taja birki daga gefe don cika umarnin yar uwarta din Amman badon ranta yasoba Hasna ta yi tsai tana kallonshi kamar zata cinye shi. Daga can inda suke Murtala babban abokinsa ya hango Hasna’da ta zuba masa ido, ya zungure shi yana fadin, “Kai mai‘farin jinin‘ mata, ga wata can ta kafe ka da ido. k0 ita ma tana ciki’ne?“ .. ‘ Abduljabbar’ yakalli inda Murtala ke nuna masa Karaf suka yi ido hudu. da Hasna ya kafeta da idansa, amma ita ta yi’” saurin dauke idonta farinciki fal ranta, ta kalli Husna tana fadin, “Muje sister, na ga suna kallonmu KO maganarmu sukeyi!!! Husna ta ja motar ’da sauri‘ suka “ci gaba’ da tafiya, Hasna ta kasa kara kallon inda Abduljabbar ya ke, don tana ji.a jikinta har lokacin yana kallo inda ta ke Abduljabbar ya yi tsaki, ya juya kansa yana fadin, “Ita ta sani ‘wataqila ma kai take . kallo, ka maido ‘abin kaina. Ni ban santa ba ‘ sam”. Murtala‘ ya fashe da dariya yana fadin “Amma ba ka da mutumci, kai da kake malami a makarantar nan baka santa ba sai ni bako da na kawo maka ziyara kawai k0? Tsayuwarmu a nan mata nawa ne suka kalle ka, har da masu gaishe ka kana basar ‘da‘ su, ka zama sai kace wani dodo, ba ka dariya’ balle murmushi” “Wai me ya kawo ka gurina ne, wa‘azi k0 me?” _ ‘ Murtala ya kuma fashewa da dariya. “Ziyara da kuma, wa’azi, ya kamata ka saki ranka‘ ka yarda mata abokan rayuwa ne _ kamar maza, za ka sami dukkan abin da ka ke bukata a tare da su idanka shirya wa hakan, ko da bai gamsar da. kai‘,,,,,”. . Abduljabbar ya_ kara- hada fuska, ya kamata ka tafi haka, lokacin Ziyarar taka ta cika idan na isa gida za mu yi waya”. Murtala ya bude baki da mamaki Don nace ka saki’….. Abduljabbar ya bude motarsa Yana fadin, “Surutunka ya’yi yawa ban fiye son ka kawo mini ziyara a makarantaba sai anjima”. Ya tada motarsa, Murtala yaja gefe DA sauri yana murmushi don yasan abokin NASA sarai bai san dalilin da ya sanya abokin nasa bai son mata ba sam, k0 da ya ke yana hasashen dalilin. Abduljabbar ya nufi Kofar fita yana huci, don ya cika saboda dariyar da Murtala ke yi masa, Murtala ya nufi motarshi har lokacin yana dariya, duk randa ya kawo wa abokin nasa ziyara a makaranta basa rabuwa ta dadin rai, don sai ya zolaye shi a kan abin da shi kuma bai kamawa sam. ‘ A Bangaren su Hasna, farin ciki ya cika zuciyarta‘ duk damuwarta ta kau yanzu, sai zuba karadi ta ke yi wa ‘yar uwarta wacce ke kada kai kawai tana dariya. Suna isa harabar gidan suka hango Abba zaune a kan motarsa yana waya, amma suna shigowa ya zuba musu ido, nan da nan “fuskar Hasna ta sauya zuwa damuwa taja tsaki, “Kai Abba da naci yake wallahi”. Husna ta yi dariya sanda ta ke qokarin yin fakin, “Ba naci bane soyayya ce, bai kamata ki ga laifinsa ba domin kin‘san“ me ye so k0?” Hasna ta dalla mata harara, bata ce komai ba ta bude motar ta fice, Husna ta bude ta fito ita ma. Abba ya duro daga kan motar ya nufe su yana murmushi, “Barkanku da zuwa ‘yan mata wato nazo a daidai ke nan?” Husna ta saci kallon Hasna ta qara hade fuska ta yi murmushi, “Watakila…” Ya kalli Hasna da keta Bata rai, yace “Yammata irin wannan cin maganin fa, ko na yi laifine?” , Ta kada manyan idaaunta dara dara farare sol da take’ruda samari da su, ta ce “Ko daya na dai gaji ne, ‘ bari ‘na wuce na huta don ka san yanzu muka taso, sai mun yi waya’ kawai ‘ Ta wuce ta barsu Abba ya bi ta da kallo da damuwa, sannan ya kalli Husna da ta nuna rashin jin dadin abin da ‘yar uwar tata ta aikata. Ya kada kai da damuwa, “Husna wai me sister dinki ke nufi, gabadaya ta sauya mini, ba na ganin fara’arta sam, cikin kwanakin nan k0 wani abin ne ya faru ban sani ba?” Husna ta kakalo murmushi tana son kwantar masa da hankali, “Sai kace baka san halin ‘yar buyagin taka ba? Gajiya ce kawai a tare da ita, amma da ta warware komai zai zama daidai, mu karasa ciki mana”. Bai musa ba ya bita, domin gidan kamar gidansu yake, kasancewar mahaifinsa qani ne ga Alhaji Abbas uwa daya uba daya. ‘ Tun lokacin da Abba ya bayyana son Hasna kowa ya ji dadi cikin dangin, don abin zai zama tuwona maina, Hasna ba ta da wani zabi a wancan lokacin, don haka ba tace da Abba ba ta sonshi ba, duk da bata taba ce masa tana sonshi ba, shi kadai ya ke sabgarsa. A falo ya ci karo da Hajiya Aysha zaune tana kallo, ta dubesu da mamaki tana fadin, “Abba daman kazo shine baka karaso ba, sai da kaga mutananka k0?” : Ya yi dan murmushi yana shafa qeyarsa da kunya. yace’, “Momy waya na ke yi shi ya sanya ban shigo ba, an wuni lafiya‘?” “Lafiya Kalau”. Hajiya Aysha ta ba shi amsa. . Ya sami guri ya zauna daidai lokacin da ‘ Husna ta wuce ciki, bayan ta yi wa mahaifiyarta sannu da gida. , A daki ta.tadda Hasna, ta fada gado ta. zuba wa silin ido. Ta qarasa ta zauna kusa da ita tana fadin. “Wash Na gaji sister, wallahi”. Hasna ba ta ce da ita komai ba, ta dan kalleta da idanunta tana murmushi kawai. Abba ya damu da yadda ki ka yi masa fa, ; kin san mutumin naki dan shagwaBa ne bai son damuwa sam”. Ta Kara Bata fuska kamar zata fasa ihu, “Yana daga cikin abin da ke ba ni haushi da shi, mutum ya dinga halayya kamar wani Karamin yaro, wai shi dan so, don Allah haka namiji ya dace ya kasance? Husna tana ’dariya da tsokana, ta ce “Ke yarinya, kada kallon hadari ya sanya ki yin~wanka da kashi ki‘ tashi ki sake wanka kawai ki isa ga masoyinki‘na gaskiya” Ta karasa maganar da zolaya. Hasna ta kulu matuqa kamar za ta fashe ta ce, “Wallahi babu inda za ni, ke idan‘ki ka matsa min ma yanzu za mu kwashi ‘yan kallo da ke, mace sai takurar tsiya Husna ta fashe da dariya, gami da miqewa tana fadin, .”Kin ga ba nina kar zomon‘ ba, bari na shiga wanka kada ma ki huce a kaina”. ‘ . Ta shige bandaki da sauri ‘tana Sheqa ‘ dariya, abin da ya Kara kular da~ Hasna ta ja tsaki ta juya ta sake kwanciya. . Tsawon lokaci Abba yana tare ,da Momy suna ta hira’; bai cika damuwa da jiran Hasna . ba, don shi mayentane, ya kanzo sau uku har hudu wani lokacin anan yake wuni .” amman yau kam kallon da ta yi masa da yanayin da ya ganta ya dan tayar da hankalinsa, don haka hankalinsa yana kan hanyar dakinsu, lokaci zuwa lokaci ya kan daga ido ya kalli kofar. Babu Hasnar balle Husnar. Bayan dogon lokaci Husna ta fito sanye da kaya zuwa riga da wando masu‘fadi, da nufin cin abinci. ‘ Ya kalle ta da mamaki, “, yace husna………………