MURMUSHIN AJALI COMPPLETE HAUSA NOVELNOVELS

MURMUSHIN AJALI COMPPLETE HAUSA NOVEL

Tsoho yadubi sultan yayi gyaran murya ‘yace sultan wato mairo dakake gani akwai wani babban al’amari atare da ita ‘Wanda iyakar bincike na nakasa gano komeye saidai inafatan yazamtoh alkhairi”’ cikin rashin fahimta sultan yace wani al’amari kenan tsoho?

Jinjina kai tsoho yayi yace abinda nakeson sani kenan amma haryanzu nakasa ‘amma nasan da sannu kome zai bayyana ‘fatana Allah yasa alkhairi ne atare da ita”

Nan suka ta6a fira da tsoho sultan ya shaida masa tafiyarsa jibi in Allah yakaimu”’nan tsoho yaimasa nasiha sosai akan yaji tsoron Allah sannan yamaida hankalinsa akan abinda yaje nema”’

Mikewa sultan yayi yacewa tsoho zai shiga cikin gdn yaiwa su baabaa asabe sallama””’

Yana sa Kansa cikin soron yaci karo da Miemie hannunta yaja yana cewa yauwa zo nan ke nake nema dama””’ cike dajin haushi tace toh mezan maka kuma?

Murmushi yayi yace babu tambaya kawai zan maki””’ tsaki tayi tace inajinka’ shiru yabiyo bayan wasu seconds kamin sultan ‘yadubeta yace’ ”kifadamin gsky pls”’

Gyada kai tayi alamar eh’ yace jiya kindawo gd ne da daddare?, ‘cikin zare ido tace ni? Da yaushe?

Sultan ganin yadda ta razana sai zuciyarsa tabasa cewa ba ita bace”’danhaka yace forget kawai inaga mafarki nakeyi'”

Sakin hannunta yayi yawuce cikin gdn ‘yabarta tsaye cikin soron”’bayansa tabi da kallo sannan takwashe da dariya ”tace am sorry yah sultan I hv no option ,,dole nai pretending ”’

Acikin gd koda sultan yaje yagaida baabaa laure yace mata jibi zaitafi ta6e baki tayi tace Allah kiyaye hanya”’ yana fita tabi bayansa da kallo tana cewa sakaran yaro Mara wayau kawai””

Baabaa asabe kam daya shaida mata cewa tayi haka zaka tafi kabar jikin musa ? Kallonta yayi yace kenan nizan bashi lfy idan natsaya?

Girgiza kai tayi tace a’ah amma dai zaifi kyau katsaya Ku gana ‘domin ba lallai ne kadawo ka taddashi araye ba”domin wannan cutar tashi dakyar inna tashi ne”’

Cikin jin haushi sultan yace dake ran nasa ahannunki yake saiki kashe shi ai”’mtwe, mikewa yayi yafice zuciyarsa cike dajin haushin baabaa asabe”’

Sashin inna amarya yashiga”yana xuwa ya taddata zaune tana cin dambun shinkafa Wanda yaji zogale sai kamshi ke tashi””

Tana ganinshi tace a’ah sultan Kaine tafe ”cikin murmuahi yace eh inna nine ‘Nazo yimaki sallama ne tafiyata jibi shiyasa nazo sallamarku””

Zama yayi kusa daita ‘yasa hannu yajanyo buta yawanke hannunsa sannan yasaka cikin kwanon dambun yafara ci”’

Bayan sun kamallah ne inna amarya tadubeshi ”tace toh sultan gashi zaka tafi wani garin dabaka saba dashiva” zaka had’u da sabbin mutani INA rokonka da karike mutuncinka da martabar addininka ‘abinda yakaika shikadai zakayi karka yarda kayi Hulda da mutanin banza”’ inayi maka fatan alkhairi ”Allah yabaka sa’a yasa asamo abinda akaje nema”””””’cikin farinciki sultan ya amsa da ameen ta karfen” wlh duk kinfi sauran matan ””’dariya tayi tace kardai kaimin dad’in baki” kwantar da kansa yayi bisa cinyarta yana cewa Barin mori cinyar masoyiyata kamin natafi””

Kunnensa tarike tana cewa Allah yakiyaye nazam masoyiyarka saidai kanemi wata ‘amma ni ta Alhaji bukar CE'””

Shigowar Miemie ahargitse shiya dawo dasu daga nishadin da sukeyi””’

Idanunta jazur kamar garwashi”’koba’a tambaya va kasan tasha kuka ne””” da Sauri sultan yamike a cinyar inna yana tambayar Miemie abinda yasameta”’

Guri tasamu tazauna tasaka fuskarta cikin cinyoyinta ”tana wani irin kuka” sultan hankalinsa yatashi sbd tun tasowarshi baita6a ganin Miemie tayi kuka irin hakava saiyau””’

Karasowa yai kusa da ita yana rarrashinta”’janyota yayi jikinsa yana bata hakauri”,
Saida takai kusan Monti shabiyar tana kukan kamin ‘tadago’ tadubi sultan ”’

Tace yah sultan tunda muke rayuwarmu abba yata6a dukana? Girgiza mata kai sultan yayi alamun a’ah” tasake share hawayenta tace mommah fah itama ta ta6a dukana? Nan ma a’ah sultan yace”’

Tadubeshi tace kaifah kata6a dukana ? Girgiza mata kai yayi alamar a’ah”tadubi inna tace inna kefah kinta6a dukana?

Inna tace a’ah mezaisa nadokeki ke kuwa”’ hannu tasa tazuge zip d’in rigarta”’rigar tafadi k’asa ”nan farin bayanta da babu ko d’igon baki ya bayyana ”saidai abun mamaki shatoti ne na bulala kwance abayan nata sunyi rud’u rud’u dasu””’
Abunka ga farin mutm duk sunyi jazur ‘ga dukkan alama Wanda yai dukan duk karfinsa yasake yaidukan””

Cikin tashin hankali sultan yace waye yaimaki wannan dukan? Cikin hawaye tace nima bansan shi va” amma dai naga yana shigowa gdn nan sashin su baabaa asabe”’ naji yara suna kiransa da yaya muntari””’

Sultan yace ynxu mekikai masa da yaimaki irin wannan dukan? Wlh saina rama maki”” mikewa yayi cikin hanzari”’ zaifita’

Inna tariko rigarshi tace ahir d’inka sultan kabarshi da Allah domin muntari ba mutunci garesa va ”ynxu haka nasan yanakan hanyarsa xuwa nan””’

Bata gama rufe baki ba ”yashigo”babu ko sallama ”duban inna yayi yace ke inna kijawa wannan banzar jikar taki kunni akan zama datakeyi da tsoho awaje ko wlh saina karya mata k’afa”

Jinjina kai inna tayi alamar taji”sultan cikin jin haushi yafara takawa zai isa kusa dashi ‘inna tarike masa Riga tabaya”’
Miemie kam ranta yariga yagama 6aci ”’danhaka tamatsa kusa dashi ”’
Saida takare masa kallo sannan tace ‘ashema mashayi ne ”

Toh kasani ko’a gdn giya kake kwana karyarka takare wlh wlh wlh sainai ajalinka tunda harkasa hannunka ajikina ‘wannan shine babban kuskurenka aduniya”””

Karubuta ka aje ‘har ubanka saiyayi Dana Sanin haihuwarka ”saikaga yadda rayuwarka zata karke””

Tana gama fadan haka tajuya tafita ””binta yayi shima yana cewa Dan ubanki zoki kasheni shegiya me fuskar agwagwa”””’

Sultan da inna kam daskarewa sukayi awurin sbd Jin furucin Miemie”’ saidai sungodewa Allah babu Wanda yake wurin balle aji ”alan’k’aya mata wata maganar”””

ana tare????
[08/10 8:33 am] Me Kosai✍: ???? ????
???? ????
????????????????????????????
MURMUSHIN AJALI
????????????????????
????????????????????
????????????????????????????
Written by Aysha Wakili
Mrs ahmed

dedicated to friend bee kalbi Miemie

Page2⃣2⃣

Bin bayanta sultan yayi shima” adaidai soro ta tsaya ‘tana share hawaye ‘shikuma muntari yazo yawuce ta yana cewa shegiya mekama da mayu””’ binsa tayi da ido ”’

Yana ficewa sultan na karasowa ”’kallonta yayi yace zomu koma ciki’ sharce hawayen fuskarta tayi tana cewa yah sultan kabarni kawai katafi abunka karka damu dani”’
Cikin damuwa sultan yace taya zanwuce nabarki haka ‘kina kuka” share hawayenta tayi tace shikenan nadena yah sultan d’ina ynxu katafi abinka””’murmushi yayi yace toh kizo mukoma gd kinga jibi zanwuce””

Murmushi tayi tace karda damu zanxo gobe saina kwana ”amma yah sultan kasan zanyi kewarka dayawa koh?

Dariya yayi yace aini ne zanyi kewarki kan’wata mai bani farin ciki”’ yehh yah sultan dama ina baka farinciki shine baka ta6a gayamin ba?
Girgiza kai yayi yace ke dad’ina dake shiririta”’

Jan hannunta yayi xuwa waje””kan wani dakali suka zauna yadubeta ‘yace Miemie,ta amsa da na’am ‘yace ynxu fah sai nai shekara hudu xuwa biyar kamin musake kasancewa tare””’

Dariya ta kwashe dashi tace wlh a’ah nikam ko SAFINA barakayi va zanzo naganka naga enda kasauka” sannnan owani lokaci zanrika kasancewa tare dakai ”. Dubanta yayi yace wazai kawoki?

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button