NAFEESAT RETURN COMPLETE HAUSA NOVEL

Ad
_____
[5/21, 9:53 PM] Oummu Ζahirah: ππππππππππ
FAMILY DOCTORS
π©Ί
ππππππππππ
π±π±π±π±π±π±π±
NAFEESAT RETURN
π±π±π±π±π±π±π±
MALLAKAR:
NAFISAT ISMA’IL LAWAL
SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT π§π»β
Ψ¨Ψ³Ω Ψ§ΩΩΩ Ψ§ΩΨ±ΨΩ Ω Ψ§ΩΨ±ΨΩΩ
PERFECT WRITER’S ASSOCIATIONπ
( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS πͺ)
/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/
*P.W.AβοΈ*
JIKAR LAWALI CEβοΈ
Wattpad: UmmuDahirahπ
Thanks be May God bless everyone, peace and blessings be upon our leader Prophet Muhammad Sallallahu Alaihi Wasallam, may God bless you and grant me the ability to write this book, may God grant me the ability to write what will benefit the nation ameen.
SADAUKARWA
Na sadaukar ga Family na gaba Ιaya. GOMA’S FAMILY.
LITTAFAN MARUBUCIYAR
NAFEESAT.
BARRISTER IBRAHIM KHALIL.
LABARIN DEEBIZAH.
MALAMA LADI.
JARUMAI
LUBABATU (Ζ΄ar Ζwallon Ζafa).
EPISODE One
Doctor '' Al'ameen Abubakar Khabeer Cindo ''and his wife ''Prof. Nafeesa (Baby) Isma'il Audu, '' as you know in the story of *NAFEESAT* They live in Kaduna, and they still live in the city, owned by their five children.
*1_ DOCTOR NOOR (LAWAL AL'AMEEN ~YARON UMMEE NAFEESA~)* Wanda a yanzu ake kiran sa Big Dady, matar sa Ιaya *Hajiya Asiya (Hajiya) Ζ΄a ga Muhsina,* yaran su uku, Doctor Usman, sai Doctor Zainab ~yanzu haka tayi aure,~ sai kuma Yusra.
2_ HAJIYA RABI’ATU AL’AMEEN (IKRAM) ~WANDA A YANZU TANA AURE A GARIN KATSINA~ tana zaune da iyalan ta acan.
3_ DOCTOR ABUBAKAR AL’AMEEN ~WANDA YANZU AKE KIRAN SA DA ABBA~ matar sa Ιaya Doctor Fatima (Hajja Fatu) ~Ζ΄a ga Abokin Doc. Al’ameen wato Haidar da Ζanwar sa Ihsan,~ yaran su Biyu, Doctor Al’ameen (Baffa), sai Ζanwar sa Shakira.
4_ DOCTOR AL’AMEEN AL’AMEEN (ABBU) Matan sa biyu, ~Bilkisu (Umma) Ζ΄a ga Baseera,~ yaran ta uku Doctor Zulaiha ~tayi aure,~ sai Fadila da autan su Fadil. Sai matar sa ta biyu A’ISHA (AUNTY AMARYA) yarinyan ta Ιaya ”’NAFEESAT”’ suna kiran ta da Ζahira.
5_ HAJIYA LAILA AL’AMEEN yanzu haka tana aure a Kano, ta auri babban Yaron WALID. Suna zaune da iyalan su can.
WaΙannan familyn yanzu haka suna zaune ne a gida Ιaya kowa da part Ιin shi, sai dai akwai Babban parlour'n da ya haΙa su, yanzu haka Doc. Al'ameen Wanda a yanzu suke kiran sa da *KAKA* ya kai shekaru 89years. Tuni ya ajiye aikin sa sakamakon yana fama da ciwon Ζafa wanda a halin yanzu yana zaune ne a wheel chair, matar sa Prof. Nafeesa (Baby) Shekaru uku kenan da Allah ya amshi abin sa.
Za kuyi mamaki idan nace muku duk ka familyn Doc. Al’ameen gaba Ιayan su DOCTORS ne, wannan shine burin sa kuma Allah ya cika masa.
Babban asibitin da ya gina ya Ζara haΙΙaka shi wanda a halin yanzu Five Block ne, kuma sosai asibitin me suna *(AL'AMEEN FAMILY HOSPITAL)* tayi fice a Ζasar Nigeria, gaba Ιaya familyn suna aiki ne a Hospital Ιin.
Yanzu haka a halin yanzu an shirya yin babban Walima don taya Doc. Ζahira(Nafeesa) Al’ameen Al’ameen, Doc. Shakira Abubakar Al’ameen, Doc. Yusra Noor Al’ameen, da Doc. Fadila Al’ameen Al’ameen. Murnan kammala karatun su na likitanci, wanda za su soma aiki ne a ranan da a kayi musu waliman tare da sabbin ma’aikata da za’a Ιiba a ranan.
KU BIYO NI DON JIN LABARIN WAΖANNAN FAMILYN
Zaune suke su HuΙu a Babban katafaren parlour'n gidan da ya'amsa sunan sa a haΙuwa da Ζayatarwa, da shigowan ka parlour'n Babban Hoton Prof. Nafeesa (Baby) zaka soma cin karo dashi, wanda tayi sa ne lokacin da ta zama Professor, tana sanye da baΖar abaya me tsananin kyawu da burgewa, wanda duk da kasancewar ta baΖa ba Ζaramin kyau yayi mata ba, sai tayane kanta da Milk Colour Ιin Veil, kyakykyawar fuskarta yalwace take da murmushin da ya Ζara fito da tsantsan kyawun ta tare da Dimpul Ιin ta, a tsaye take ta riΖe Ζugu da hannu biyu tare da Ιan Ιage kanta, da alamun sanda akayi hoton bata san ma za'a yi sa ba. kusa da hoton kuma wani tanΖamemen hoton ne da a cikin sa Al'ameen ne tare da ita Babyn, suna zaune manne da juna sun saka ankon shadda me ruwan powder, gefe da gefen su kuma Noor ne tare da Ikram jingine da jikin su, duk kan su dariya suke yi time Ιin da aka Ιauki hoton, sai gefe kuma sauran hotunan Ζ΄an gidan ne kowa da iyalan sa, sannan sai aka Ιau guda Ιaya wanda su kayi gaba Ιaya familyn, shi wannan ba'a daΙe da yin sa ba, don gab da rasuwan Prof. Baby akayi sa, gaba Ιaya idan ka kalle su sosai suke kamanceceniya da juna, sai dai banbancin launi da ya raba su.
Doc. Al’ameen wato KAKA tare da yaran sa maza su uku zaune cikin parlour’n suna tattauna yanda za su gudanar da Waliman yaran su kamar yanda suka saba a duk sanda yaran gidan suka gama karatun su na likitanci.
“Kai takwara yaushe matarka zasu dawo ne? Kasan jibi ne walima, ya kamata su dawo don itama Matata (yana nufin Ζahira kenan) ta sami damar shiryawa yanda Ya kamata”. Kaka dake zaune saman wheel chair yake wannan maganan
ABBU yace, “insha Allahu Dady zasu dawo zan sake tuntuΙan su inji, sabida mahaifin A’isha (matar sa Aunty Amarya) jikin ta yayi tsanani ne shiyasaka suka jin kirta”.
Kaka yace, “to shikenan Allah ya dawo da su lafiya”.
Gaba Ιaya suka amsa da “ameeen”.
Sannan ya kalli Big Dady yace, “Kai kuma da yaushe ne Usman yace “zai dawo?”
Big Dady yace, “Allah ya taimaki Dadyna! na yi masa magana amma yace “in ba ka haΖuri ba zai samu daman zuwa ba sabida aiki sun yi masa yawa”.
Cikin nuna alamun fushi Kaka yace, “wai yaushe Usman yabzama me taurin kai ne? Ko don yana tunanin na ba shi dama ya zauna acan yayi aiki shine yake son Ιata min rai? To, ka gaggauta kiran sa ka faΙa masa umarni nake ba sa; dole ne ya zo wannan taron Waliman da za’a yi, ko me yake yi ya’ajiye sa ya halarci taron nan”.
Gaba Ιayan su su kace “Allah ya huci zuciyar ka Baba”.
“Insha Allahu zan sanar masa Dady kuma zai zo”. Cewar Big Dady kenan
GyaΙa kansa Kaka yayi kana yace, “za ku iya tafiya na sallame ku, Allah yayi muku Albarka”.
Gaba Ιayan su suka amsa da “ameen” kana suka tashi suka fice.
Shi kuma Kaka janyo Remote yayi ya sauya tasha zuwa African t.v yana sauraron wa’azi
Da sallama Fadil ya shigo parlour’n, wanda ya kasance shine Ζaramin gidan don shekarun sa baza su wuce 14yrs ba. zama yayi kan kujeran da ke kusa da na Kaka ya saka hannu ya ja gemun Kakan da ya kasance fari fat, yana dariya yace, “Kakus kana hutawa ne?”
Kaka bige hannun sa yayi yana faΙin, “Ζaniyar ka Fadil, kai ma ka koyi jan min gemun ne yanda Matata take min?”
Dariya ya tuntsire da shi yace, “to ai hakan ya fi dace wa da kai Kakus, don me baza ka aske gemun ba ka bar abu sai faman lilo yake yi, wlh watarana kana barci zan silalo in cire maka kowa ya huta”.
Dariya shima Kakan yayi yace, “lallai ka raina ni da yawa amma ina da me maganin ka, ka jira ya dawo zan faΙa masa duk abinda kake min”.
Zumbur Fadil ya miΖe yana waro ido waje yace, “afwan Kakus kaima ka san ba mu haka da kai, wlh yau ne kawai nace bari in Ιana Amma baran sake ba, Kar kasanar masa don Allah kaji Kaka na”. YaΖarike maganar nasa yana me marairaice fuska kamar zai yi kuka
“ShaΖiyin yaro ashe kana da tsoro har haka?”
Waro idanu Fadil Ιin ya sake yi yace, “iyyee Kaka taya bazan ji tsoro ba bayan kana son ka haΙa ni da Zakin gidan mu? Ni dai ka ga tafiya na don tunda ka’ambato shi bazan iya zama anan ba”. Yana Ζarisa maganar ya ruga aguje yabi hanyar part Ιin su
Da dariya Kaka yabraka shi, kana ya girgiza kan sa aran sa yana cewa, “lallai Usman ka koya ma yaran gidan nan tsoron ka, ba ka a cikin gidan ma shekara da shekaru amma har yanzu tsoron ka be bar cikin ran su ba”.
Ci gaba da kallon sa yayi, sai can kuma ya Ιago kansa yana kallon hoton matar sa Baby, Wanda take ita kaΙai Ιin, murmushi da hawaye ne a haΙe suka taho mishi tunawa da rayuwan su, kullum ranan duniya sai ya zub da hawaye a kan ta, coz Ko wacce rana sai ya kalli hoton ta sama da ashirin, kuma aduk sanda zai kalla ko yayi kuka ko yayi dariya sabida abinda zai tuna na game da rayuwan su a wannan lokacin, gaba Ιaya Ιakin sa idan ka shiga hotunan ta ne birjik, da sanda take tashen ta da sanda ta tsufa, har ta bakin gadon sa inda yake saka kansa akwai hoton ta da ya’ajiye a wajen, mutuwan ta ya bala’in girgiza sa wanda yayi kamar bazai rayu ba, sai daΖyar ya dawo hayyacin sa bayan dogon jinyan da yayi, har yanzu har gobe soyayyar ta tana nan daram a zuciyar sa, domin kamar Ζaddara ne da Allah ya saka masa na tsananin Ζaunarta, kullum fatan sa ace ga ranan da zai bi ta, shima ya koma ga mahaliccin sa kamar yanda ta tafi ta bar sa..
Dafa kafaΙun sa da akayi shi ya dawo dashi hayyacin sa, Yusra ce tsaye kansa tana kallon sa, idan da sabo yaci ace sun saba da ganin Kakan nasu cikin wannan halin, kuma sun san da cewa ba komi yake saka sa a halin nan ba illa tuna Kakar su.
“Kaka har yanzu dai ka Ζi ka dena tuna wannan tsohuwar matar taka, har yaushe ne zaka cire ta arai ne kayi rayuwan ka cikin kwanciyar hankali? Mu nan mun ishe ka rayuwa ba sai ka tuna ta ba, me ake yi da tsohon Zuma bayan ga sabbin zuma? Don Allah ka dena Ιata time Ιin ka a kan ta”.
Hannu ya saka ya share hawayen yana murmushi yace, “Yusra kenan baza ki taΙa gane wa ba, amma kowa ya san da cewa tsohon zuma shi ne wanda ke magani, sannan ba’a iya manta shi ko wani hali mutum ya shiga, Ni Matata ta fiye min ku duk kan ku, idan da za’a bani zaΙi daku da ita in zaΙa, ita zan zaΙa in bar ku”.
TaΙe baki Yusra tayi tace, “to don baka zaΙe mu ba sai me Kaka? Our parents will vote for us because they love us.”
Kaka yace, “to naji ban ce kiyi min rashin kunya ba, said me to my room”.
Ad
_____