Our website is made possible by displaying online advertisements to our visitors. Please consider supporting us by whitelisting our website.
NAFEESAT RETURN COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

NAFEESAT RETURN COMPLETE HAUSA NOVEL

Ad

_____

[5/21, 9:53 PM] Oummu Ɗahirah: πŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’Ž
FAMILY DOCTORS
🩺
πŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’ŽπŸ’Ž

🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱
NAFEESAT RETURN
🌱🌱🌱🌱🌱🌱🌱

MALLAKAR:
NAFISAT ISMA’IL LAWAL

SARAUNIYAR TSOKANAR PERFECT πŸ§πŸ»β€

Ψ¨Ψ³Ω… Ψ§Ω„Ω„Ω‡ Ψ§Ω„Ψ±Ψ­Ω…Ω† Ψ§Ω„Ψ±Ψ­ΩŠΩ…

PERFECT WRITER’S ASSOCIATION🌞

( WE AIN'T PERFECT BUT WE'RE ALWAYS, TRYING OUR BEST TO MOTIVATE AND ENTERTAIN OUR READERS πŸ’ͺ)

/https://www.facebook.com/Perfect-writers-association-100452275039839/

           *P.W.A✍️*

JIKAR LAWALI CE✍️

Wattpad: UmmuDahirahπŸ‘ˆ

Thanks be May God bless everyone, peace and blessings be upon our leader Prophet Muhammad Sallallahu Alaihi Wasallam, may God bless you and grant me the ability to write this book, may God grant me the ability to write what will benefit the nation ameen.

SADAUKARWA
Na sadaukar ga Family na gaba Ι—aya. GOMA’S FAMILY.

LITTAFAN MARUBUCIYAR
NAFEESAT.
BARRISTER IBRAHIM KHALIL.
LABARIN DEEBIZAH.
MALAMA LADI.
JARUMAI
LUBABATU (Ζ΄ar Ζ™wallon Ζ™afa).

EPISODE One

    Doctor '' Al'ameen Abubakar Khabeer Cindo ''and his wife ''Prof. Nafeesa (Baby) Isma'il Audu, '' as you know in the story of  *NAFEESAT* They live in Kaduna, and they still live in the city, owned by their five children.



    *1_ DOCTOR NOOR (LAWAL AL'AMEEN ~YARON UMMEE NAFEESA~)* Wanda a yanzu ake kiran sa Big Dady, matar sa Ι—aya *Hajiya Asiya (Hajiya) Ζ΄a ga Muhsina,* yaran su uku, Doctor Usman, sai Doctor Zainab ~yanzu haka tayi aure,~ sai kuma Yusra.

2_ HAJIYA RABI’ATU AL’AMEEN (IKRAM) ~WANDA A YANZU TANA AURE A GARIN KATSINA~ tana zaune da iyalan ta acan.

3_ DOCTOR ABUBAKAR AL’AMEEN ~WANDA YANZU AKE KIRAN SA DA ABBA~ matar sa Ι—aya Doctor Fatima (Hajja Fatu) ~Ζ΄a ga Abokin Doc. Al’ameen wato Haidar da Ζ™anwar sa Ihsan,~ yaran su Biyu, Doctor Al’ameen (Baffa), sai Ζ™anwar sa Shakira.

4_ DOCTOR AL’AMEEN AL’AMEEN (ABBU) Matan sa biyu, ~Bilkisu (Umma) Ζ΄a ga Baseera,~ yaran ta uku Doctor Zulaiha ~tayi aure,~ sai Fadila da autan su Fadil. Sai matar sa ta biyu A’ISHA (AUNTY AMARYA) yarinyan ta Ι—aya ”’NAFEESAT”’ suna kiran ta da Ɗahira.

5_ HAJIYA LAILA AL’AMEEN yanzu haka tana aure a Kano, ta auri babban Yaron WALID. Suna zaune da iyalan su can.

   WaΙ—annan familyn yanzu haka suna zaune ne a gida Ι—aya kowa da part Ι—in shi, sai dai akwai Babban parlour'n da ya haΙ—a su, yanzu haka Doc. Al'ameen Wanda a yanzu suke kiran sa da *KAKA* ya kai shekaru 89years. Tuni ya ajiye aikin sa sakamakon yana fama da ciwon Ζ™afa wanda a halin yanzu yana zaune ne a wheel chair, matar sa Prof. Nafeesa (Baby) Shekaru uku kenan da Allah ya amshi abin sa.

Za kuyi mamaki idan nace muku duk ka familyn Doc. Al’ameen gaba Ι—ayan su DOCTORS ne, wannan shine burin sa kuma Allah ya cika masa.

    Babban asibitin da ya gina ya Ζ™ara haΙ“Ι“aka shi wanda a halin yanzu Five Block ne, kuma sosai asibitin me suna *(AL'AMEEN FAMILY HOSPITAL)* tayi fice a Ζ™asar Nigeria, gaba Ι—aya familyn suna aiki ne a Hospital Ι—in.

Yanzu haka a halin yanzu an shirya yin babban Walima don taya Doc. Ɗahira(Nafeesa) Al’ameen Al’ameen, Doc. Shakira Abubakar Al’ameen, Doc. Yusra Noor Al’ameen, da Doc. Fadila Al’ameen Al’ameen. Murnan kammala karatun su na likitanci, wanda za su soma aiki ne a ranan da a kayi musu waliman tare da sabbin ma’aikata da za’a Ι—iba a ranan.

KU BIYO NI DON JIN LABARIN WAƊANNAN FAMILYN

     Zaune suke su HuΙ—u a Babban katafaren parlour'n gidan da ya'amsa sunan sa a haΙ—uwa da Ζ™ayatarwa, da shigowan ka parlour'n Babban Hoton Prof. Nafeesa (Baby) zaka soma cin karo dashi, wanda tayi sa ne lokacin da ta zama Professor, tana sanye da baΖ™ar abaya me tsananin kyawu da burgewa, wanda duk da kasancewar ta baΖ™a ba Ζ™aramin kyau yayi mata ba, sai tayane kanta da Milk Colour Ι—in Veil, kyakykyawar fuskarta yalwace take da murmushin da ya Ζ™ara fito da tsantsan kyawun ta tare da Dimpul Ι—in ta, a tsaye take ta riΖ™e Ζ™ugu da hannu biyu tare da Ι—an Ι—age kanta, da alamun sanda akayi hoton bata san ma za'a yi sa ba. kusa da hoton kuma wani tanΖ™amemen hoton ne da a cikin sa Al'ameen ne tare da ita Babyn, suna zaune manne da juna sun saka ankon shadda me ruwan powder, gefe da gefen su kuma Noor ne tare da Ikram jingine da jikin su, duk kan su dariya suke yi time Ι—in da aka Ι—auki hoton, sai gefe kuma sauran hotunan Ζ΄an gidan ne kowa da iyalan sa, sannan sai aka Ι—au guda Ι—aya wanda su kayi gaba Ι—aya familyn, shi wannan ba'a daΙ—e da yin sa ba, don gab da rasuwan Prof. Baby akayi sa, gaba Ι—aya idan ka kalle su sosai suke kamanceceniya da juna, sai dai banbancin launi da ya raba su. 

Doc. Al’ameen wato KAKA tare da yaran sa maza su uku zaune cikin parlour’n suna tattauna yanda za su gudanar da Waliman yaran su kamar yanda suka saba a duk sanda yaran gidan suka gama karatun su na likitanci.

“Kai takwara yaushe matarka zasu dawo ne? Kasan jibi ne walima, ya kamata su dawo don itama Matata (yana nufin Ɗahira kenan) ta sami damar shiryawa yanda Ya kamata”. Kaka dake zaune saman wheel chair yake wannan maganan

ABBU yace, “insha Allahu Dady zasu dawo zan sake tuntuΙ“an su inji, sabida mahaifin A’isha (matar sa Aunty Amarya) jikin ta yayi tsanani ne shiyasaka suka jin kirta”.

Kaka yace, “to shikenan Allah ya dawo da su lafiya”.

Gaba Ι—aya suka amsa da “ameeen”.

Sannan ya kalli Big Dady yace, “Kai kuma da yaushe ne Usman yace “zai dawo?”

Big Dady yace, “Allah ya taimaki Dadyna! na yi masa magana amma yace “in ba ka haΖ™uri ba zai samu daman zuwa ba sabida aiki sun yi masa yawa”.

Cikin nuna alamun fushi Kaka yace, “wai yaushe Usman yabzama me taurin kai ne? Ko don yana tunanin na ba shi dama ya zauna acan yayi aiki shine yake son Ι“ata min rai? To, ka gaggauta kiran sa ka faΙ—a masa umarni nake ba sa; dole ne ya zo wannan taron Waliman da za’a yi, ko me yake yi ya’ajiye sa ya halarci taron nan”.

Gaba Ι—ayan su su kace “Allah ya huci zuciyar ka Baba”.

“Insha Allahu zan sanar masa Dady kuma zai zo”. Cewar Big Dady kenan

GyaΙ—a kansa Kaka yayi kana yace, “za ku iya tafiya na sallame ku, Allah yayi muku Albarka”.

Gaba Ι—ayan su suka amsa da “ameen” kana suka tashi suka fice.

Shi kuma Kaka janyo Remote yayi ya sauya tasha zuwa African t.v yana sauraron wa’azi

Da sallama Fadil ya shigo parlour’n, wanda ya kasance shine Ζ™aramin gidan don shekarun sa baza su wuce 14yrs ba. zama yayi kan kujeran da ke kusa da na Kaka ya saka hannu ya ja gemun Kakan da ya kasance fari fat, yana dariya yace, “Kakus kana hutawa ne?”

Kaka bige hannun sa yayi yana faΙ—in, “Ƙaniyar ka Fadil, kai ma ka koyi jan min gemun ne yanda Matata take min?”

Dariya ya tuntsire da shi yace, “to ai hakan ya fi dace wa da kai Kakus, don me baza ka aske gemun ba ka bar abu sai faman lilo yake yi, wlh watarana kana barci zan silalo in cire maka kowa ya huta”.

Dariya shima Kakan yayi yace, “lallai ka raina ni da yawa amma ina da me maganin ka, ka jira ya dawo zan faΙ—a masa duk abinda kake min”.

Zumbur Fadil ya miΖ™e yana waro ido waje yace, “afwan Kakus kaima ka san ba mu haka da kai, wlh yau ne kawai nace bari in Ι—ana Amma baran sake ba, Kar kasanar masa don Allah kaji Kaka na”. YaΖ™arike maganar nasa yana me marairaice fuska kamar zai yi kuka

“ShaΖ™iyin yaro ashe kana da tsoro har haka?”

Waro idanu Fadil Ι—in ya sake yi yace, “iyyee Kaka taya bazan ji tsoro ba bayan kana son ka haΙ—a ni da Zakin gidan mu? Ni dai ka ga tafiya na don tunda ka’ambato shi bazan iya zama anan ba”. Yana Ζ™arisa maganar ya ruga aguje yabi hanyar part Ι—in su

Da dariya Kaka yabraka shi, kana ya girgiza kan sa aran sa yana cewa, “lallai Usman ka koya ma yaran gidan nan tsoron ka, ba ka a cikin gidan ma shekara da shekaru amma har yanzu tsoron ka be bar cikin ran su ba”.

Ci gaba da kallon sa yayi, sai can kuma ya Ι—ago kansa yana kallon hoton matar sa Baby, Wanda take ita kaΙ—ai Ι—in, murmushi da hawaye ne a haΙ—e suka taho mishi tunawa da rayuwan su, kullum ranan duniya sai ya zub da hawaye a kan ta, coz Ko wacce rana sai ya kalli hoton ta sama da ashirin, kuma aduk sanda zai kalla ko yayi kuka ko yayi dariya sabida abinda zai tuna na game da rayuwan su a wannan lokacin, gaba Ι—aya Ι—akin sa idan ka shiga hotunan ta ne birjik, da sanda take tashen ta da sanda ta tsufa, har ta bakin gadon sa inda yake saka kansa akwai hoton ta da ya’ajiye a wajen, mutuwan ta ya bala’in girgiza sa wanda yayi kamar bazai rayu ba, sai daΖ™yar ya dawo hayyacin sa bayan dogon jinyan da yayi, har yanzu har gobe soyayyar ta tana nan daram a zuciyar sa, domin kamar Ζ™addara ne da Allah ya saka masa na tsananin Ζ™aunarta, kullum fatan sa ace ga ranan da zai bi ta, shima ya koma ga mahaliccin sa kamar yanda ta tafi ta bar sa..

Dafa kafaΙ—un sa da akayi shi ya dawo dashi hayyacin sa, Yusra ce tsaye kansa tana kallon sa, idan da sabo yaci ace sun saba da ganin Kakan nasu cikin wannan halin, kuma sun san da cewa ba komi yake saka sa a halin nan ba illa tuna Kakar su.

“Kaka har yanzu dai ka Ζ™i ka dena tuna wannan tsohuwar matar taka, har yaushe ne zaka cire ta arai ne kayi rayuwan ka cikin kwanciyar hankali? Mu nan mun ishe ka rayuwa ba sai ka tuna ta ba, me ake yi da tsohon Zuma bayan ga sabbin zuma? Don Allah ka dena Ι“ata time Ι—in ka a kan ta”.

Hannu ya saka ya share hawayen yana murmushi yace, “Yusra kenan baza ki taΙ“a gane wa ba, amma kowa ya san da cewa tsohon zuma shi ne wanda ke magani, sannan ba’a iya manta shi ko wani hali mutum ya shiga, Ni Matata ta fiye min ku duk kan ku, idan da za’a bani zaΙ“i daku da ita in zaΙ“a, ita zan zaΙ“a in bar ku”.

TaΙ“e baki Yusra tayi tace, “to don baka zaΙ“e mu ba sai me Kaka? Our parents will vote for us because they love us.”

Kaka yace, “to naji ban ce kiyi min rashin kunya ba, said me to my room”.

Ad

_____

1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42Next page

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button