MURMUSHIN AJALI COMPPLETE HAUSA NOVELNOVELS

MURMUSHIN AJALI COMPPLETE HAUSA NOVEL

NIGERIAShabiyu na rana tayi anraba yan’sanda takoena ana neman gawar muntari amma ba’a samuva’ yan’uwa da abokan arziki anshiga tashin hankali sosai ‘ inda mahaifiyar muntari ke kuka tana cewa ataimaka akawo mata gawar d’anta tagani da kanta ‘taimasa addu’ah ,amma shiru kakeji babu gawar muntari babu alamun sa ‘dan kaf cikin unguwar nan saida yan sanda suka bincika amma basu ganiva”

Har la’asar ana abu daya’ danhaka tsoho yatara dukka family d’insa a farfajiyar gdn sa”’ nan akaita jajantawa yan’uwa abinda yafaru ‘daga bisani tsoho yace , shifah wannan al’amarin yana d’aure masa kai da tunani’ yaza’ai ace gawa ta 6ata ba’a ganta va’ ga dukkan alamu akwai wani abu dake 6oye wanda mu bamu saniva ‘ saidai ina umartar kowanne daga cikinku daku tsananta bincike akan wannan al’amarin ,domin agano bakin zaren’Sannan ina ganin wannan zaman makokin da akeyi bashida amfani tunda bamu da tabbacin mutuwar tasa ‘musamman idan mukayi la’akari da 6atan gawarsa” da haka aka watse kowa da abinda yake sak’awa acikin ransa”

Miemie da salma zaune cikin daki ‘kowacce tayi tagum tagum” salma tadubi miemie tace ynxu ina gawar muntari zata shiga ?,wayaxo yadauke shi? Kodai ma ba mutuwa yayi va?
Miemie tace oho ni inazan sani ‘ke bakima ji dadi ba koba kome aizaki huta da tijarar dayake maki” girgiza kai salma tayi tace ko kad’an bana murna sbd kome muntari zaimin dan’uwana ne baranyi fatar wani mugun abu yasame shi va””

Shiru miemie tayi tace hakane amma tabbas abaki kike fadan wannan maganar amma a zuciyarki bahaka bane” kuma idan kin musa zan iya fada maki abinda zuciyarki ke ayyanawa ” ido waje salma ke kallon miemie domin tabbas abinda miemie tafada gsky ne saidai ya akai tasan abinda ke xuciyarta?

Lallai gara tayi shiru kar miemie ta tona asirin zuciyarta”””’ bata sake magana va ”miemie tace salma ynxu saiki saki jikinki domin babu muntari balle yatakira maki’ yanacan lantsandan ‘kema inkina bukata kina iya binshi”’????

washe gari da safe haka kowa yatashi da tsammanin ganin gawar muntari amma shiru kakaji kamar an aiki bawa garinsu”” inda hankalin mahaifiyarsa yakai matuka wajen tashi ‘gaba dai tafita hayyacinta ‘ sai rok’o takeyi akawo mata gawar d’anta tagani”

Mahmud kam yakasa koda bud’e motarsa domin koda daddare dazasu wuce gida cewa hafsa yayi taxo su shiga adaidaita danshi bare iya shiga motarsa va” sbd gani yake kamar muntarin na ciki ko kuma gawar zata dawo’haka suka koma gd amma basuyi bacci va ,mahmud yakasa bacci wanda dalilin hakan yasa hafsa itama bata iya barcin va”

Sultan kwance a dakinsa yana hutawa shida ameer ‘kamar antsikare shi yamike yadau wayarshi yashiga kiran numbern mommansu ‘saidai har wayar takare ruri ba’a d’auka va” nan yasake kira still ba’a dauka va’ abun yabashi mamaki saiya sake kiran na abbansu ‘shima harya kare ruri ba’a dauka va”’duban ameer yayi yace ameer ji wani abun mamaki tundazu sai trying numbern mommah da abba nakeyi amma basu d’auka va komeyasa ? Ameer yace toh kabari xuwa anjima saika sake kira mana mayb dey re busy ne””

Kan dole sultan ya hkr ‘suka cigaba da fira’ ji sukai ana buga masu k’ofa nan ameer yatashi yaje yabud’e ”wanda yai sallamar yabashi hannu suka gaisa ‘suka shigo d’akin tare ”
Ganin wanda suka shigo tare yasa sultan saurin mik’ewa fuskarsa da murmushi yace a’ah dama baku tafi va? Shima murmushi yayi yace eh wlh oga yace saigobe zamu tafi shiyasa nace bara naxo mui fira da d’an uwana kamin natafj” nan sultan yacika da murna ‘ duk suka zauna suna fira cikin annashuwa””

Sultan yadubi muntari yace yauwa zanbaka sak’o ka kaiwa my lil miemie kace mata inasonta sosai nd ina missing nata tunda ita bata sona”’ nan yamik’e da nufin d’auko sak’on sai muntari yarik’e masa hannu yace dakata kaji” aiba gd zamuyi va daga nan misra zamu tafi kuma ina ganin zamu d’auki lokaci me tsawo kamin mukomo nigeria ‘mezaihana ka aje sak’on agunka dan gudun karnaje na salwantar dashi’?
Jinjina kai sultan yayi yace hakane kuma ” barshima zanbawa abokin abbanmu inzai tafi saiya kai mata”’

Muntari bai bar hostel d’insu sultan ba ‘sai bayan magrib ”wanda ameer dake sauraren firarsu duk yak’osa muntari yatafi sbd Shi amatse yake yafad’awa sultan abinda yabashi tsoro”’

Sultan na dawowa daga rakiyar muntari ameer yatareshi ‘yana cewa sultan anyako wannan muntarin mutm ne?
Cikeda mamaki sultan yace meyafaru ?ko meka gani?
Ameer yace gani nayi gashi nan zaune kan kujera amma kuma bana ganinshi ajikin madubin dake fuskantar kujerar saidai nahango kujerar amma ba mutm akai”

Cikeda zaro ido sultan yace me ????????
Wani irin magana kakeyi ne ameer? Ameer yace wlh gsky nake fada maka kaima dan dai baka lura bane”

Ana tare????
[30/10 4:41 pm] Me Kosai✍: ???? ????
???? ????
????????????????????????????
MURMUSHIN AJALI
????????????????????
????????????????????
????????????????????????????
Written by Aysha wakili
Mrs ahmed

dedicated to friend bee kalbi Miemie

Page3⃣2⃣

Da sauri sultan yaja hannun ameer yana cewa zomuje tunkan yayi nisa mugansa”’ dagudu suka fice a d’akin sukabi hanyar da sultan yaimasa rakiya ‘ sunyi tafiya sosai amma ko kurwansa basu gani va inda ameer harya gaji da gudu”’ wuri suka samu suka zauna suna maida numfashi sultan yadubi ameer yace amma fah baici ace muntari yayi nisan wannan tafiyar damukayi va ‘ sbd awnawa da irin gudun damaukayi”
Ameer yace aikam ‘mu hkr kawai mukoma dan nikam nagaji’
Haka suka juyo zuwa xuwa hostel kowannensu na haki”

Nigeria da safe bayan tagama aikinta tashirya itada yaranta suna jiran mahmud yafito domin xuwa family house ‘ hannu tasa tadau wayarta tana dubawa ganin misscall dayawa yasata mamakin yaushe ma aka kira ‘tana dubawa taga sultan ne nd tunjiya yakira” batare da 6ata lokaci ba tashiga kiransa”’

Ringing biyu yad’auka cikeda farin ciki yace mommah na ina kuka shiga keda abba tunjiya inata kiranku ba wanda yad’auka ‘ ajiyar zuciya tayi tace sultan bamu cikin hayyacinmu shiyasa bamu d’auka ba nd wayarma bata tare damu”
Cikin damu sultan yace meyafaru mommah meya fiddaku cikin hayyacinku?????.

Cikin damuwa hafsa tace wani babban al’amari ne yafaru jiya wanda yatada hankulan dukkan ahalin tsoho”’ cikin k’aguwa sultan yace mommah menene wannan abun pls fad’amin’
Nan hafsa tabashi labarin kome tundaga farko har xuwa mutuwar muntari da 6atar gawarsa””’dayake tunda suka fara wayar a handsfree yake ameer najin duk abinda ake fad’e ””aiko yanajin mutuwar muntari da 6atar gawarsa dagudu yamik’e zaibar d’akin sultan yajanyo shi yadawo da baya ‘ yace wlh saikaji k’arshen labarin ‘ cikin rau rau da ido sultan yace pls kabarni nafita karnai mafarki ”
Ko kallonshi sultan baiyi va yaci gaba da tambayar mommansu ko’anga gawan ynxu ” tace ai hrynxu ba’a gansa va ynxu hakama gdn tsoho zamu tafi muji a ena aka tsaya””
Nan sultan yace ok tafadawa abbansu zaikira shi anjima yad’au wayarshi” nan ta amsa da toh sukai sallama”

Sultan na aje wayar suka k’urawa juna ido shida ameer ‘kana ganin yadda ameer yayi xurum da ido kasan a tsorace yake’ sultan yace kai farar kura ,munhadu da fatalwar muntari ne fah ”inko ba fatalwa bane to aljani ne”
Da sauri ameer yace kaii sultan yi shiru dan annabi nifah ynxu hatta d’akin nan tsoro yake bani ””

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button