YAN ABUJA HAUSA NOVEL

YAN ABUJA HAUSA NOVEL

   BY HAERMEEBRAERH

This page is for u our missing Sawwama Qawwama, i and all ur fans ,tum hari yaad aa rahi hoo, we wish u will be back soon dear????❤

Darene yanzu a cikin garin Abuja, a wani hotel da su Alh Salihu suka maqale wa, tare da ‘yan matan su da bazan iya tantancewa arna ne ko musulmai ba, wata naji an kira da ‘yar Gwal, daga nan na gane hausawa ne, amsawa tai ta juya, dayar ta mata nuni da ido, murmushi naga sun sakamr ma juna, ” mene ne naga kuna wani dariya kamar wasu wadan da suka cinci damin kudi a qasa?” Inji Alhj Kallah kenan da ya ga sanda sukai hakan,” ‘Yar gwal ce ta hau cinyar Alhj Salihu tana wani karairaya tana shafa shi” Alhaji na kudi muke so, gaba daya qawayen mu sun wucemu a komai, bayan muna tare da ku, gaskiya zai zama abin kunya ace ko motar hawa bamu da ita” tana magana tana kai bakin ta jikin nashi, wani irin nunfashi Alh ya fitar da bai san yana ruqe da shi ba,” Haba ‘Yar gwal yanzu dan wannan shine kuke wani abu kamar baqi, ai in kuna son abu kamar umarni zaku bamu kuga an cika, dan haka,….. kan ya qarasa kamar jira suke suji zaa biya masu biqatar su, suka miqe tsaye suka ja su daga clube din dake cikin hotel din zuwa dakunan hotel din , tin a hanya suke romancing din su, naje leqawa sukai slamming qofar a fuskata???? haka nai baya na koma gidan Suwaiba naga wainar tmda take toyawa.

Hango ta nai tana zaune ta baza kaji a gaba da fresh milk a gaba tana diba, hankalin ta kwance, tana danna wayar ta, bayan ta gama taje tai wanka tai brush, ta saka kayan hacci, amma sam bata jin bacci, komawa tai palon ta kunna kallo, tqna kallo tana duba lokaci, wannan rayuwa, ace miji ba zai dawo da wuri ba sai dare ya raba? Tashi tai ta dakko fruit salad data hada ta saka a fridge, ta zauna tana kallo tana sha, bayan ya qare ne, ta aje bowl din a gefe, dai hamma take tana miqa, duk ta gaji da zaman shirun, wayar ta taji tana ringing, miqa hannu tai ta dauka, “Saudat love” shine sunan da ya fito akan wayar, ” Hey sis”
“Hey”
” ya kk, da yayan nawa?”
” muna lfy, Ya Alhjn ki?”
“Muna lfy”
“Dama kiran ki nai naji ko Baby na gidan ku, tsoro nake ji, gidannan ya min girma, duk dare sai naji kamar kirana ake,” ta fafa cike da tsoro,
” Sis kiyi hakuri baya nan, nima zaman jiran mine nake, duk yanda akai suna tare, ki kwantar da hankalin ki ki mori abinda ya kawo ki, tin kan lokaci ya qure maki” amsawa tai da”to” sallama sukai suka kashe wayar Suwaiba ta tashi tai daki, bata jima da kwanciya ba, lokacin qarfe 2:45am ya shigo bakin shi duk warin giya, tsabar kwarewa da sukai ba sa layi, sai dai a gane ta idon su, da saurin fushin su,Suwaiba ce ta miqe ta nufe shi, ” wai wannan wanne irin wulaqanci ne Sweethert, tinda nazo gidan nan i can’t remember d last time we had xxx, amma da nai magana kace lokacin ban da lfy ne, yanzu danaji sauqi ka kasa sauke nauyin dake kan ka, amma kai da dikkan alamu har yanzu kayi auren ma wasu kk bi a waje, ga giyar da kk sha wadda ni ban san kai din dan giya bane, wannan ai iskanci ne” ta fada tana daga murya tana masifa” ni kk kira dan iska? Ni kk kira dan iska ko, ba dai ni kk cewa dan iska ba ? Yau zakiga iskanci ganin idon ki Suwaiba” miqewa yai ya janyo ta ya hau duka kamar an aiko shi, a haka ya cire mata kayan ya wurgar duk ya yaga su, aiki ya fara akan ta full time, and non stop, gaba daya jikin ta yai tsami ga duka , ga xxx din da ba tai niyya ba, kuka take tana” kai hakuri nice yar iskar ba kaiba, ba zan qara ba , ka taimaka min, ka duba auren soyayyar da mukai da kai” kwade bakin ta yai yace ” auren soyayya ko auren kwadayi?auren kudi? Karki zaci ban san kr da uwar ki kwadayayyu bane da yan uwan ki? Ina sane da komai, ni ba qaramin mutum bane” qara wurgata gadon yai da take qoqarin guduwa ya kwanta a jikin ta, nan da nan bacci ya dauke shi, kuka take sosai jikin ta na ciwo, haka ta tashi ta ja jiki da kyar, ta tafi toilet, ruwan zafi ta hada mai zafi sosai, ta shiga, tana shiga tai qara dan azaba, a haka ta gasa jikin ta taji dadi sosai, nan da nan bacci ya fara diban ta a xaune a ruwan, fita tai taje ta saka wasu kayan ta koma daya dakin ta kwanta, ta rufa, nan da nan baccin wuya yai gaba da ita, da asubar fari Saudat ta kira ta a waya tana kuka, Ta sanar da ita irin cin mutuncin da Alhn ya mata itama, sata yai tai ta mai tausa, har wayewar gari, data fara gyangyadi ya zabga mata mari, ta dora daga inda ta tsaya, kuka sukai tayi, ba mai lallashin wani, itama Suwaiba labarin nata ta bata, sannan sukai akan gobe zasu hadu in mazajen sun fita, qoqarin shigowa ake ta danne wayar ta kwanta tai lamo kamar me bacci, qarasa shigowa yai ya zauna kuda da ita, ” Haba my Suwai hakuri zaki, ke ma kin san in rai na y baci bana son a cika tambaya ta musamman maganganu na rainin wayo, auren kudi kikai kuma ga kudin nan, to meye na damuna sai na maki wani abun?” Kuka take ta gefen ido bata ce komai ba, janta yai jikin shi yana shafata, take ta fara saukr ajiyar zuciya tana hamma, don bacci take ji sosai, kiss ya mata ya maida ta ya kwantar yace shi zai fita, daga mai kawai tai ta koma ta lumshe ido, bayan ya fita ne tai baccin awa uku ta tashi tai wanka , ta hada abin karyawa mai rai da motsi da tea mai kauri ta ma manta jibgar da ta sha, taci tai nak abinta, Wayar ta ce tai ringing ta amsa da ” ku barta ta shigo qanwa ta ce” ta kashe, Wajen kamar minti 5 Saudat ta shigo, cikin shiga ta alfarma, ga wata arniyar mota da ta zo da ita driver na tuqata, ta ci gold ko ta ina hannu da qafa da kunne, dan harda sarqar qafa suke daurawa, isa tai itama kusa da sister din ta akan dinning table ta ja plate ta zuba chips da kwai da farfesun naman kan rago, sai tea da ta hada itama mai kauri ta hau sha, sai da ta gama sannan ta yada kai baya ta zame kadan daga kujerar tace” Sis ina cikin tashin hankali wanda da dikkan alama kema haka ne, dan ga jikin ki ya nuna, dubi fuskata” ta fada tana mai nuna mata fuskar ta da tai jawur ta kumbura, sai rufewa tai da mayafi da ta shigo,” ga zaman yunwa da nai dan jiya kwata2 kasa cin komai nai”
” yar uwa bari kiji, ki cire komai a ranki shawarar da zan bamu shine mu cire rai a son sai sun zama mutanen kirki, tin da dai ba halin su bane, mu zauna mu mori dukiyar da muka zo Abuja domin ta, mu xama manyan hajiyoyi,mu bawa maqiyan mu kunya, dan ni kam kin ganni nan, in ba jiya dana sha jibga ba, bana wasa da abin ci ko wani nau’i na jin dadi, sannan kuma da kk ganni nan haqqina na aure in daga yau ya ce ya daina ban ba zan damu ba, domin kuwa akwai hanyoyi da dama da zan iya maganin matsala ta, wanda na san kema kin dan su ba sai na tsaya bayani ba, i hope ba zasui gangancin turamu wannan stage din ba, zasu na daure wa ko once in a while ne suna biya mana buqatun mu, to kinga ba mu da matsala da bin matan su ko kuma wani abu mai kama da shan giya, sun dade ba suyi ba???? dan ba zan qara yarda a taba lafiya ta ba, an gama daga jiya” ” kaiiiii yar uwa wannan shawara tayi wallahi” tafawa sukai suka koma palo duka debo dambun nama da juice suka dawo palo suka kunna kallo, sunayi suna hira qarshe waya suka dauka, suka hau kiran Goggo Sarai, suna waya, a lokacin suna tsakar gida dikkan su, Mama Bilki, Abban su Juwairah, Ammar, da ita kanta Goggon, wanki Mama Bilki keyi na kayan Abban su da na Ammar, ita kuma tana girki, wanda ta dade da dena cin abincin gidan sai dai tai nata, su kuma suci nasu, hakan da tai yada Abban sun ya samu ragi daga dawainiya, shiyasa ma wataran suke samun abinda suke aikawa Juwairah dan Mama ta kula da rayuwar da take ciki a zuwan da tai sau daya, amma da ta tambaye ta, qeqasa qasa tai tace ita lfy lau komai yake tafiya masu, addua tai mata kawai amma tasan akwai wata a qasa, cikin firgici ta daga kai daga tinanin ta sakamakon……

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39Next page

Leave a Reply

Back to top button