YAN ABUJA HAUSA NOVEL

YAN ABUJA HAUSA NOVEL

Sun isa asibiti bayan layi da suka bi, gwajin farko aka gano tana dauke da cikin wata hudu da sati biyu, zaro idanu take kamar mara gaskiya???? ga murna ga kunya duk sun ishe ta, ta rasa ya zatai, janyo hijab din ta tai ta sunne kan ta a ciki tana dariya qasa qasa, Jabeer ta gani ya tashi yai sujjadar godewa Allah yana kwallar murna, itama a cikin ranta take maimaita” Alhamdu lilLAAHi ala kulli halin, hamdan katherran ya rahman, murna take sosai taji hannun shi ya janyo ta jikin shi, hada fuskar su yai waje daya suna shaqar nunfashi junan su,” Juwaireren mama kin ga ikon Allah akan mu ko, ya mana kyauta mai dadi da sanya farin ciki ko?” Daga masa kai kawai take tana murmushi, Doc. ne ya ce” to Lovey-Dovey sai a tsaya a saurare ni kuma in anje gida an qarasa murnar, ina da wasu masu jiran a waje” yana fara’a da jun sun burge shi yake maganar, shawarwarin da zasu taimaka masu ya basu, ya rubuta magani inda yace su je su nuna takardar kawai za a basu kyauta ne,godiya sukai mai yawa sika fita, he locked there hands together, dan ji yake kamar ya dauke ta karta wahala, he is happy, kula da hakan da yai ne yasa ta tsada su a wani wajen da ba mutane sosai tace” Babe can i ask u a favour?” ” Anything for u my love,just say it, inshaa Allahu in baifi qarfina ba i will do it for u” murmushi tai ta sunkuyar da kai qasa” Yah pls don’t tell anyone that i am pregnant plssss” ta qara damqe hannayen su” But why, abun murja ne fa? Don’t u want them to be happy for us, and must importantly to pray for us, and our baby” ya qarasa cikin rada, ” Yah is not what i meant, kawai ni kunya nake ji, kowa ya san me nai na samu cikin nan, har da Abba???? ” kiran Abban ta da tai wata kunya ta qara kamata kamar yama gani, dariya Jabeer yake sosai yana riqe ciki, ” amma kema baki da wayo na kula, to bari kiji, tin kan a kawo ki aka san in an maki aure zamui abin da zaki samu ciki, come on mu wuce gida rana da dukar min ke” maqale kafada tai tana turo baki, ” what again?” ” i am so hungry” but we just ate?” ” yeh i know, but i am still hungry” yatsina fuska take kamar in bata ci ba wani abu zai same ta ne, ” k then me kk so?” ” Yah ga me agwaluma can ita nake so, kuma ina son waccan zogalen dafaffe” “ikon Allah, ashe kwadayin da kk ta min kwanaki bbyn mu ce ke saka ki” ya maqale murya” Yah ka taho mun da gyada mai gishiri, ka tahon da rake, kazo man da akwaluma mai yawa” kukan shagwaba zatai yai maza ya kama bakin shi, alamar yayi shiru” yi hakuri ba zan sake ba kin ga a titi muke duk da katangar nan ta kare mu kinga masu agwalumar zasu maki dariya” narke fuska tai” Oh ni Juwairah yau naa ga tsokana da ranar Allah””Auuuuu kin fi son a tsikane ki da dare kar ki damu wannan ma ba a barmu a baya ba ai” da sauri yai wajen masu agwaluma yana dariya, zura hannun ta tai a riga tana shafa cikn ta dayake a lafe kamar ba komai, amma tana jin motsawa kadan kadan, ” Ikon Rahman, wato wai ni Juwairah ke dauke da ciki ban sani ba, Allah na gode maka, kasa duk abin da zan haifa ya zama musulmi mumini salihi, Allah ka sani na bi dukkan yanda Annabin ka ya tsara mana don samun ‘ya’ya na gari, tin kafin aure na har yanzu da ka ban wannan arziqi, Allah ka sa su zama wadan da muslunci da musulmai zasui alfahari da amfanuwa da haihuwar su, Allah na gode maka ka ba wadan da basu da shi, ka sauqaqa min wajen haihuwa” hannun shi yasaka ya ce” Earth to Juwaireren mama, tinanin me kk haka? Na dawo ina tsaye baki ji ba, wato har zaki fara manta ni ko” ya fada yana shagwabe baki kamar yaro” ba komai muje gida nayi na sha abunnan yunwa ta qaruwa take” dariya yai suka kama hanyar fita suka samu abin hawa sai gida, lokacin da yake fadawa innar mu gudu ta saka tai bangaren su tana dariya, kowa murna yake a gidan kamar me, labari nan danan ya bazu a dangi Juwairah na dauke da cikin wata hudu da sati biyu, kowa na murna da saka albarka, jin wannan labarin da Goggo Sarai tai ya daga mata hankali, domin tunanin ta ya tafi akan dama yaran ta ne, ko dan samun wani kaso nadukiyoyin surukan nata,nan take tinanin Salma ya fado mata, wayar ta ta dakko, taita zabga kira ana mata turanci, hankalin ta ya tashi sosai, mayafi ta yafa ta leqa ta kira Abban su, ta bashi ya ji me ake fada, ce mata yai wai layin baya aiki yanzu,” wai ni wa kk kira haka ne, Malam wannan Yarinyar Salma mana, duk Yan uwan ta sunyi waya anji daga wajen su amma ita shiru, ga wannan kabarin da ya iske ni na samun cikin wannan kodadiyar” ” hmmmm Sarauta kenan A gabana kk sok ki ciwa ‘yata fuska wai kodaddiyar ‘ya na gode, Allah zai raba su lfy, ita kuma Salma Allah ya sa ki same ta a wayar, in kun yi magana kin sanar da ni” yai shigewar shi ciki, wayar suwaiba ta kira ta dauka itama tambayar ta tai tace bata ji daga wajen ta ba, Saudat ma amsa daya ta bata, hankalin ta suka kwantar akan cewa ta yu ma sun fita qasar waje d mijin ne shiyasa, wani farin ciki ne ya maye damuwar ta.

Salma wadda ta koma Salame kuwa, ana can qauye, jikin ta qaura yai la’asar, ba kowa ne da yasan ta zai gane ta ba, duk ta kode ta jeme.

Yau ne ranar karbar jini a wajen su Suwaiba wanda Oga Zaks ya buqaci ko a kai su, ya qara dana su, ko akai jini……..
..
[11/26, 12:35 PM] Hermeebrah: ???????? ‘YAN ABUJA ????????

     BY HAERMEEBRAERH

page 13:

Mijin Suwaiba ne Alhj Salihu yai wa mijin Saudat magana akan yanda zasu aiwatar da qudirin su na samun abinda suke so cikin sauqi, dariya suka bushe da shi suka tafa, a tare suka furta” ‘YAN ABUJA” lokacin suna dawowa gida,dan daga wajen Oga Zaks clube suka wuce as usual amma yau basu dade ba dan sha dayan dare suka dawo gida , cikin kwalli kowa ya tadda iyalin shi, an sha kayan ado, fatar nan har wani sheqi take sabida jin dadi da hutu, sai dai suna isa kowacce ta tanadi magana a bakin ta da ta ja masu jibga, Suwai ba ce ta fara gabatar da uzurin ta kamar yanda Goggo sarai ta sa ta fadi” Mine ” “Na’am” tana fada tana wani tauqi tana manne mai a jiki, ” dama cewa nai ko zamu asibiti a duba mu ne, lfyr mu qalaou kuwa? Har yanzu fa ban taba koda barin wata ba, ga qanwar mu na da ciki, kuma zai zama mana abin gori mu da mahaifiyar mu ace mu uku ba mai ciki” wani wawan mari ya antaya mata, ya hankada ta qasa sai da ta kifa, ” dan uwarki ni zaki mayar qaramin mutum qaramin yaro? Wanda bai san me yake ba? OHHH wato ki haihu na samu magaji ko? Ko ki kashe ni ki karbe dukiya ta ko? To bari kiji wani abu, wannan dukiyardaga karuwai sai masu saida giya su zasu more ta, ba tsarin yara a rayuwar nan tawa, ban sani ba ko gaba, amma as of now ban da wannan burin da kwadayin yaran da ke zaki sani neman haihuwa” ” dan Allah ka saurare ni ka kuma fahimce ni” kan ta qarasa ya rufe ta da mugun duka ko ta ina yana ” baki yarda ki daina sa in sa da ni ba ko, ina fada kina fada kema , aiko xaki ci uwar ki yau, sai soyayyar yara ta fita a zuciyar ki yau”, waya ya ciro ya dinga zabga mata, tin tana kuka har ta rufe idon ta a qasan wajen ta daina mitsawa, a haka ya samu damar ida qudirin shi na mata allurar bacci, ya debi jinin ta dan mugunta har keda biyar, yana gamawa yai ma mijin Saudat magana ta waya, yaji yana haki, tambayar shi yai ko lfy, ya bashi amsa da ” sai da jakar taci duka tukunna, wai ni zatai wa zancen haihuwa” ” kalla rabu da su wannan shegiyar uwar tasu ce zata zugo su ai gashi ta ja musu duka , ni leda biyar na diba dan uban ta, ai ta gina jikin da kayan kudin” dariya Kalla yai sosai,” ni kuma hudu da diba” to sai mun hadu yanzu zan fito,tsallake ta yai ya fice dakin shi ya saka jinin a inda aka basu su saka, wata jakar fata da akai mata ado da ja, da ratsin baqi a jikin ta ta ratayawa ce, ba a son su aje ta a qasa ko da da mistake ne sai sun ba da wani wannan ya tashi aiki, in ba haka ba sai an kaiwa Oga Zaks matan, domin ko kusantar su yai jinin nasu diban shi ake, sun isa wajen Oga zaks, suna isa suka miqa mai jinin wata dariya ya barke da ita kamar an yaga zani, ba ko dadin saurara” aikin ku na kyau, shiyasa kuka fi sauran abokan harka shanawa, bakuda tsoro, bakwa jinkiri, ku gaggauta maza muje a ba Dodo jinin kyawawa ya sha” ta shi sukai suka shiga wani daki, dan tsoro ina leqawa nai baya a 360 ba zan iya dakko maku rahoton komai ba anan, gidan Saudat na je, tana kwance rabin jikin ta na kujera, rabi na qasa, fuskar ta ta kumbura tai sintim, dan tafi ta kwanaki hayewa, jikin ta ko digon duka babu, a zuciyata nace wanan Alhj Kalla shi na shi hukuncin Kalla mari ne kawai???? mari kam iya mari ta shashi da dikkan alamu, dan ina jin shi ya sata suma ma, ruwa na yayyafa mata na labe, a firgice ta miqe tana” ni bana son Yaran ma har abada, kayi hakuri ka daina kallan mari” tana fada tana kuka fuska dagaje2 da hawaye ga majina da yawun azaba” dube2 ta hau yu taga ba kowa, ga wani irin jiri dake dibar ba, da tsananin ciwon kai, komawa tai ta kwanta, tana maida nunfashi, suwai ba ko vata farka ba sai da suka koma gida wajen qarfe hudun asuba, yana isa daga ta yai toilet da ita ya hada ruwan zafi ya saka ta, ihu ta saka na azaba, dan jikin ta duk ya farfashe,” kayi hakuri mai sunan Annabawa na tuba, ba zan qara maka zancen yara ba har mu mutu, ka yafeni sharri shedan ne” rife mata baki yai yana hawayen munafurci, yana bata hakuri shima, harda in ya sake ko taba hannun ta da sunan duka ne, duk.hukuncin da taga za ta mai ta masa, runtse idon ta tai.tana jin yanda zafi ke shigar ta, nan take zuwa Abuja ya sire mata a rai, wannan wace irin azaba ce, in kaci dadi na wata daya sai an zaizaye maka shi a kwana daya? Yanzu yanda take jin ta kamar wadda akaiwa yasar wani abu, bata da qarfi ga cuwon kai da take ji kamar kan ya fice, barin ta yai ya tafi kitchen ya samu fruits ya markade ya tace ya kawo mata ya sa mata abaki yace ki sha zaki samu qarfi sosai a jikin ki, bangaren d masu aikin su suke yaje,ya tas mai girke2 dan ya mata farfesu, ko na naman meye ma a samu ta samu kwarin jiki, ai ko ba komai ta maida mugun yawu, sannan abinda ya kawo ta kenan, inji shi, farfesun naman rago yai mata da yaji kayan hadi, irin farfesunnan ne wanda mutum zai zaci gashi ne, yasha kayan lambu a ciki, qamshi da maiqo sai tashi.yake, fresh milk ya hadi mata da shi, ya koma toilet din bata shanye jus din da ya mata ba dika, dakko ta yai ya dawo da ita gado ya cire towel din ya samo riga iya guiwa mai dan fadi ya zura mata, kanta ta jingina da frame din gadon idon ta lumshe, zuwa yai ya dakko wannan hadin ya shigo da shi, ai tana jin wani qamshi mai dadi sai ga idon Suwai a bude, wani yawu ta hadiya na kwadayi, Alhj Salihu yace” shegiya dangin maita, ji fa uban ta da taci amma ta ga nama har ta miqe” a ranshi yake wanan maganar, isa yai gaban ta ya aje mata ya fara bata taga baya sauri, daga mai hannu tai.ta saka nata dayan hannu ko ta kan spoon din bata bi ba, ta hau ci kamar tsihuwar mayya, ci take ba ko tsayawa sai da tai nak, ta kora da fresh milk, ta zame ta kwanta, lokacin Subh payer ta yi amma ko a jikin su, haka suka kwanta bacci, manne mata yai yana shafa ta, abin ku da wadda ta dade miji na gabza in ta nemi haqqin auren ta, yau.ta samu a bagas dik da zafin da take ji haka ta miqa mai kanta, ranar ta murna ba iyaka, tini ta nemi zafin ciwon ra rasa, kusan abinda ya faru kenan a gidan Saudat,sai dai akwai wani plan da Suwaiba ta hada a qasan ranta na ganin me yasa ba su son su haihu, suna son su san me ya hana su haihuwa????

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39Next page

Leave a Reply

Back to top button