COLONEL UBAIDULLAH COMPLETE HAUSA NOVEL

COLONEL UBAIDULLAH COMPLETE HAUSA NOVEL

COLONEL UBAIDULLAH COMPLETE HAUSA NOVEL

Sun jima a haka kafin daga bisani ya zare bakinsa daga nata, idonsa sun kaɗa sunyi jajur dan jaraba da ta taso masa lokaci guda, cikin dauriya ya fara bata abinci, kaɗan ta ci, ta kauda kanta gefe tana yatsine fuska ta ce.
“Am ok”, Ubaidullah ganin bata ci abincin sosai bane ya saka shi haɗe rai sosai ya yi kamar bai ji me tace ba, ya ci gaba da ɗura mata abinci har sai da ta fara kakarin amai kafin ya kyaleta, tashi tayi ta wuce bedroom dinta ba tare da ta kallesa ba, ruwa ta watsa, sannan ta canza kaya itama, ta fito ta same shi, kama hannunta ya yi suka fita, nan suka tarar dasu Ummi, har dasu Umma da Inna a parking space, nan suka shiga mota suka koma asibitin.

Su na shiga Abi’atu ta hango Shafa’atu zaune a jikin wata Addanta tana ta faman kuka, da gudu Abi’atu ta karaso ta rungumeta ta hau lallashinta, yawancin yan uwa da aka zo domin fara shirin biki duk sunzo asibitin, nan Ummi take shaida musu cewa Abba yace za a daga bikin, nan wata Gwaggonsu tace sam, lokacin bikin ma za a rage a daura aure tayi jinyar mijinta, bayan ya warke yaji sauki sai ayi shagalin biki, kasancewar Gwaggo itace babba haka kowa ya amince za a daura auren Safwan da Shafa’atu gobe da ya ji sauki kuma sai ayi shagalin biki, sai dare tukunna Safwan ya farfado kuma Alhamdulillah ya gane kowa, nan suka shiga hamdala su na godewa Ubangiji, da dare da suka koma gida bayan Ubaidullah ya yi wanka ya kwanta ya tuno dasu memories da lapton din da yasa aka kawosa gida dasu, kamar an zaburesa haka ya mike ya fito, yana fitowa itama tana fitowa,karo suka yi zata fadi ya riƙeta gami da jefo mata tambaya.
“Ina zakije?”
“Kitchen”
“Me za ki yi?” haɗe rai tayi dan bata ga dalilin tambayar da yake mata ba, ganin ta hau turo masa baki ta ƙi basa amsa ya sa shi matseta ta yi yar kara tana harararsa.
“Au zasu tashi ne?”
Ya tambayeta yana kafeta da ido”
“Su wa?”
“Ƴan rashin kunyan mana, yanzu nayi maganinki” kwace jikinta ta yi tana cewa.
“Ai ban ga amfanin tambayarka bane” ta fada ta wuce kitchen, murmushi ya yi, ya fuskaci Abi’atu akwaita da gautsi, zama ya yi ya dauki lapton din ya bude ya hau bincike a ciki, fitowa ta yi daga kitchen din ganin system din a hannunsa yasata zuwa wajansa da sauri ta zauna, sai kuma ta fashe da kuka, da sauri ya kalleta ya ce.
“Lafiya?” cikin kuka ta ce.
“Na’ilah”
“Na’ilah,a ina?” bata tsaya basa amsa ba illa system din ta karba ta shiga in da ta ga samarin nan sun shiga, nan videos suka watso, zaro ido Ubaidullah ya yi, yana kallon tashin hankali, bincikawa Abi’atu ta ci gaba da yi har aka zo kan na margayiya, da sauri Ubaidullah ya karba yana gani, wasu zafafan hawaye ne suka wanke masa fuska ganin yadda ƙanwarsa ke neman taimako har wa innan azzaluman suka farmata, cikin gaggawa Ubaidullah ya dannawa Zaidu kira sannan ya ce ya duba email dinsa ya turo masa da sakonni, ko da Zaidu ya duba sai da ya yi danasanin meyasa ma ya kalla, kuka sosai Zaidu ke yi tamkar ba soja ba, Ubaidullah ya sake kiransa akan cewa, ina an kawo masu laifin barracks, Zaidu ya amsa da cewa ba a kawosu 9ja barracks ba, abacha barracks aka kai su, sai gobe za a shigo dasu 9ja barracks, Ubaidullah ya ce gobe idan jikin Safwan da sauki sosai zai bi jirgin yamma ya dawo abuja, da haka suka yi sallama da Zaidu, su na kiyasta kalar azaban da zasu gana musu kafin su kashesu, videos din ya turawa Zeey sannan ya kirata ya mata bayanin abun da zata yi, nan ta amsa masa cike da girmamawa, a ranar Ubaidullah bai rintsa ba, ko da washe gari da safe misalin karfe shaɗaya da rabi aka daura aure, kuma jikin Safwan din da sauki sosai, nan Ubaidullah ya musu sallama a asibitin gami da cewa zai wuce, Allah ya kiyaye hanya su Abba da Ummi da Safwan din da sauran wa inda suke wajan suka masa tare da fatan Allah ya ba shi sa’a, gida ya dawo dasu Mama, Hafiza da kuma matarsa Abi’atu, bayan ya gama shirinsa cikin kakinsa wa inda a ko da yaushe suke masa kyau, fitowa ya yi, a parlour ya sameta tana tsaye, cikin sanyin jiki ya zo gabanta ya kama hannunta ya ce.
“Zan wuce, kafin na tafi sai na tabbatar hukunci ta hau kan wa inda suka yi sanadiyyar ƙanwata da yaran jama’a, zamu tafi india kuma aiki ne mai hatsarin gaske, ban sani ba ko zan dawo ko bazan dawo ba, idan na mutu ki yafe m…..” sauri toshe masa baki ta yi ta fashe da kuka ta rungumesa, dan murmushi ya yi, ya ce.
“My Abi’ah, ki jirani! Ki jira dawowata, zan ba ki mamaki” yana gama faɗi ya bata light kiss a gaba daya fuskarta, sannan yasa kai ya fice, ita kuma ta zube a wajan tana kuka dan ba zata iya jurar ganin tafiyarsa ba, dan ko ba komai fadan da sukeyi ba karamin sabo bane ya shiga tsakaninsu, kuma ko ba komai zaman da suka yi ta fara son mijinta, itama kuma ta ga alamun hakan a wajansa, addua ta hau masa tana durƙushe a wajan, ko da ya fito sallama ya yi da Mama da Hafiza, sannan ya ce, bai yarda su dinga fita ba, zai aiko musu sojoji mutum uku masu kula dasu, addua Mama ta yi masa da fatan alkhairi gami da ƙarfafa masa guiwa, ya yi murmushi ya amsa da ameen gami da yi mata godiya, da haka aka bude masa mota ya shige, basu tsaya ko ina ba sai airport, ko da suka isa mintinsa shabiyar jirginsu ya daga izuwa birnin tarayya, karfe huɗu dai-dai a barracks ta yi masa, ya yinda dubbannin sojoji aka zo tarban Ubaidullah abun har mamaki ya ba shi, da masu sara masa da masu miƙa masa hannu,shima ƙamewa ya yi yana sarawa manyansa, kafin daga bisani suka rungumi juna da aminansa, Zeey ce ta taho da murnarta tana sanye da kaki a jikinta murmushi ta yi masa sannan ta sara masa gami da cewa.
“Wlcm back Sir, Captain Ubaidullah Abdullahi” karo na farko da Zeey ta fara ganin dariyan Ubaidullah,dan kuwa dariya ya mata gami da cewa.
“Tnk u Zeey, a gaskiya ke din ta dabance,kuma kin zama ta musamman a wajana” itama dariyar ta yi ta ce.
“Kamar yadda kai ma kake na musamman awajan kowa ko? ya Madam? Fatan ka barota lafiya,dasu Mama da Ƙanwarmu Hafiza?”
“Duk su na lafiya Alhamdulillah”
“Ya mai jikin fatan yana samun lafiya?”
“Eh jikinsa da sauki sosai, dan yau ma aka daura aurensa, sabida dole akwai abun da zai bukata wanda dole sai muharramarsa ce zata iya yi masa hakan” jinjina kai suka yi, sannan Zeey ta kuma cewa.
“Ba a kawo masu laifin wannan barracks din ba fa, har yanzu su na Abacha Barracks, amma ka je ka huta, tun da ka iso, idan ka gama dasu, Rumaisa da mahaifinta da Ema duk su na kulle” girgiza kai Ubaidullah ya yi ya ce.
“No Zeey ban ga ta hutu ba, in dai wa innan azzuluman su na numfashi a doron duniya, bari naje na gana da General Of The Army, sannan na zo na wuce Abacha Barracks din” KB ya ce.
“Gaskiya kam, dan tun jiya nake cikin zaƙuwa a kawosu, jiya fa Zaidu kwana ya yi yana kuka, dama baka turo masa ba wallahi” Zeey ta girgiza kai cike da tausayawa ta ce.
“Ka je ku gama da General din, Captain, nima na gama aikin da ka sakani jiya” murmushi ya yi ya ce.
“Ina alfahari dake Zeey, just keep it up” itama murmushin ta yi sannan ta wuce.

Duk in da Ubaidullah ya ratsa sai an kallesa, masu sara masa su na sara masa, har ya isa office din General ba tare da bata lokaci ba, General Of The Army ya bawa Ubaidullah Umarnin shigowa, bayan Ubaidullah ya shigo ya sara masa suka gaisa, General ya sake ba shi hakuri, Ubaidullah ya nuna masa komai ya wuce sannan ya yi gyaran murya ya fara magana.
“Sir, akan yaran da aka kamasu da laifin aikata fyaɗe, gasu videos din b’arnan da suke aikatawa, daga cikin yaran da suka yiwa fyaɗe har da kanwata wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwarta har lahira, Sir! A ko da yaushe sai munji cases din fyaɗe sama da dari a garurruwa daban daban, Sir! Abun da yake daure min kai a matsayinmu na jami’an tsaro ban taba jin wanda aka kai shi kotu aka yanke masa hukunci, ko naji an hukunta masu aikata hakan ba, wanda zai zama izna ga masu aikatawa ko masu burin aikatawa dasu tsarota su hankaltu,dan masu iya magana su na cewa ana tauna tsakuwa ne dan aya taji tsoro, Sir! Ina neman alfarma, a barni na hukuntasu da hannuna ba tare da an kaisu kotu ba, dan naga alama akwai yaran masu kudi a cikinsu wanda suke da daurin gindin manyan ƴan ƙasa, hakika idan za a dinga zalunta bayin Allah marasa karfi sannan a danne musu hakkinsu, hakika duniya ba zata taba zama lafiya ba, dan yanzu an mai da ran muninai ba a bakin komai ba, taya ma duniya za a zauna lafiya bayan jinin bayin Allah da ake wanke kasa dasu sir? Lokaci ya yi da ya kamata ace an samu wani ci gaba a ƙasarmu ta nigeria, Sir! Dama nake so ka bani a karin farko, kafin muje yaƙin karbo yan matan ƙasata wanda aka yi garkuwa dasu” sosai General Of The Army yake kallon Ubaidullah, dan kuwa ba karamin burgesa Ubaidullah ya yi ba, a take ya ce.
“Captain Ubaidullah na baka go ahead, wish u oll the best” murmushi Ubaidullah ya yi, ya sarawa General Of The Army gami da cewa.
“Tnk u sir, Allah ya ɗaga ƙasata nigeria” sannan ya juya ya fice, yana fitowa suka hadu da Hanan, wani dadi ne ya ziyarci zuciyarta, da sauri tazo tana yi masa wlcm back, Ubaidullah ya amsa ba yabo ba fallasa, nan suka dan gaisa sama-sama, sannan suka yi sallama, wajan su Zaidu ya wuce nan suka shiga mota har da Zeey, Abacha Barracks suka wuce, sai da ya je suka gaisa da Major Usman, rungume Ubaidullah Major Usman ya yi, dan yana son Ubaidullah sosai, sannan Ubaidullah ya ce sun zo tafiya da masu laifi ne, nan Major Usman ya bada Umarni akawo su, su tafi dasu, hakan kuwa aka yi, tun akan hanya suke cin duka wajan Zaidu, har suka iso 9ja barracks, direct suka wuce guardroom dasu, inda suka rufesu da duka, tun su na ihu har suka kasa ihu, sai da suka musu lilis, kafin da kyar KB ya janye Ubaidullah da Zaidu, suka koma gefe suka zauna, Ubaidullah ne ya jawo kujera ya matso su sosai, sannan yasa aka kawo masa ruwa, nan KB ya sheƙa musu ruwan, wayar wuta Ubaidullah ya jawo, wanda daga gani kasan shocking zai jona musu ko ba a fada maka ba, a matukar galabaice wani ya ce.
“Yallabai! Dan Allah kayi mana rai, ka yafe mana, ba zamu sake ba, bamu san cewa kai din soja bane, da mun san cewa kai soja ne da bamu fara ɗau…..” saukar naushi ne ya hanasa karasa maganar da yake yi, wanda Zaidu ne ya kai wannan naushin, a matukar tunzure zuciyarsa na ƙuna ya ce.
“Shut’up!!! Mutanen banza!! Allah yana arawa mugayen mutane irinku lokaci dan su aikata barna son ransu, kafin Allah ya dakatar daku a madakata, shin kusan wacece NA’ILAH!!!!? ita din Ƴa ce, ga tsohon SOJA wanda ya riƙe muƙamin Major kafin Allah ya ɗauki ransa a bakin aikinsa, sannan Ɗansa yake riƙe da mukamin Captain, NA’ILAH! ƳA CE GA SOJA! ƘANWAR SOJA, MATAR SOJA! amma ku ka yi sanadiyyar mutuwarta, tun da gaku yan iska ko!!! Shi ne ku ka kyetara ta gonawa kooo!!” ya faɗa gami da sa kafarsa mai dauke da boot army shoe ya take gaban ɗayansu ya saki ihun azaba, Ubaidullah ya jona musu shocking.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54Next page

Leave a Reply

Back to top button