Our website is made possible by displaying online advertisements to our visitors. Please consider supporting us by whitelisting our website.
LAMARIN KADDARAR AURE NA COMPLETE NOVEL

LAMARIN KADDARAR AURE NA COMPLETE NOVEL

Ad

_____

Zama tayi jugub a kujera tana share gumin da yake karyo mata tare da mai maita innalilahi a zuciyarta .

Abdallah wayarsa ya ciro yafara danne danne amma inka lura dashi sosai hankalinsa a tashe yake ,

Ko kaษ—an bata ฦ™aunar taji yayi mata magana hakan yasata miฦ™ewa ta nufi hanyar da zata sadata da bedroom ษ—inta keee!!! taji Abdallah yace ” cikin tsawa juyowa tayi batare da tace “komai ba ,

Kuma maida hankalinsa kan wayar dake hanunsa yayi a zahiri kukan zuci yakeyi dan nafili yaฦ™i fitowa .

Takai wasu mintuna a tsaye a gurin dan yanzu tsoransa ma takeji kar tayi ฦ™waฦ™waran motsi ya yanke mata mumunan hukunci,

Tashin hankali gami da rashin ฦ™aunar maman sadiq ya darsu a zuciyar Abdallah ,mai maicin da zuciyarsa take yimasa shine zina ?zina tayi kenam ba ษ—ana bane ?” ya ilahi ya riฦ™e kansa da yake sara masa.”

Ya ษ—ago kansa ya dubi maman Sadiq yace “naji duk abinda kuke ta taunawa akai dame na rageki ci ko sha ko tufafi kokuma haฦ™inki ne bana saukewa kiji tsoron Allah ,

Yaci gaba da cewa kin cuceni kin cuci ษ—anki dan bazance ษ—ana ba ,

Momyn Sadiq jira take taji kalamin Abdallah na ฦ™arshe yace ya yafe mata sai taji akasin hakan yace ” na sakeki saki biyu inkin sami miji kiyi aure kuma ki tafi da ษ—anki banida alaฦ™a dashiโ€ฆ..โœ๏ธ.

Fans kuyi haฦ™uri kwana biyu kunjini shiru nayi tafiya ne amma na dawo ganin sharhinku shine zai sa kusami pagin gaba amma in bangani ba sai bayan sallah gaskiya ๐Ÿค—.

๐Ÿ’ฆ๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐Ÿ’ฆ
๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’

LAMARIN ฦ˜ADDARAR AURE NA!!! .

  ๐Ÿ’     ๐Ÿ’       ๐Ÿ’

๐Ÿ’ฆ๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐Ÿ’ฆ

Story and writing by

ZAINAB HABIB
(mom islam)

My wattpad momislam2020

My telegram link

https://t.me/joinchat/IaKr804dfndik1e2

Zainabhabibu713gmail.com

WANAN LITTAFI GABA ฦŠAYANSA SADAUKARWA NE GA SHUGABA

(ANTY HAUWA MAMAN USWAN)

ALLAH YA ฦ˜ARA MIKI LAFIYA DA NISAN KWANA

๐Ÿ’ฆAREWA WRITERS ASSOCIATION๐Ÿ’ฆ

EPISODE 33 & 34

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM

Kasa tsayuwa tayi a gurin saboda wani jiri dake ษ—ibarta ta durฦ™usa kan guwaiwar ta tana kuka mai tsuma zuciyar mai karatu oh ni ฦดa su ina zansa kai na ,rarrafowa gabansa tare da sunkuyar da kanta ฦ™asa tace “dan darajar iyayenka ka yafemin wlh ba ‘asonโ€ฆ!!! wani wawan mari ya wanketa dashi kana ya miฦ™e tsaye yace “kar in dawo in samu kina gidannan wlh sai kinyi dana sani , ya fice zuciyarsa na suya , driving yakeyi amma hankalinsa a tashe yake ,ikon Allah ne ya kaishi gida , ko horn baiyi ba ya buษ—e murfin motar ya fice tare da buษ—e get ษ—in , mai gadi dake zaune a wata farar kujera ta roba ganin Abdallah ya shigo a fusace ya miฦ™e yana cewa Alhji barka dai ywwa kawai yace .”

Bai jira ฦ™ara jin wata maganar ba ya shige ciki , mai gadi ne ya jinjina kai ya ฦ™walawa driver kira da sauri ya taho sabda shima ya lura da yanayin Alhajin .”

Wangale get ษ—in yayi ya shigo da motar, sukazo suka zauna kafa hirar shigowar uban gidan nasu ,

Bai sameta a palo ba ya nemi guri ya zauna , kashe tv da yaketa ฦ™ararsa shi kaษ—ai yayi , ya ษ—ora ฦ™afa ษ—aya kan ษ—aya abubuwan da suka faru tsakaninsa da momyn Sadiq suka fara dawo masa ..

Cikin zuciyarsa yace ” ko kaษ—an banyi dana sanin rabuwa dake ba dan bansan ko bada ni kaษ—ai kike taraiyya ba .

Shigowar Afnan ce ta sanyashi katse tunanin tare da faษ—aษ—a fara’arsa irin karta gane yana cikin wani hali , takowa takeyi cikin isa da ฦ™asaita ,
kai kace ฦดar wani sarkin ce .”

Zama tayi gefensa tare da ratayo hanunta a kafaษ—arsa tace “lafiya mijina ? naga kamar kana cikin damuwa ” a’a Afy kaina ke ciwo yanzu ma so nakeyi na ษ—an kwanta ..

Badan ta yarda ba ta ฦ™yaleshi amma ta fuskanci akwai abinda yake damunsa jikinta a sanyaye tayi bedroom ษ—inta ta fashe da kuka ,

jiyo kukan yayi lokacin da zaiyi hanyar bedroom ษ—insa ya dawo zuwa ษ—akin nata , dole ya jata gado ya rungume ta yana jijiga ta kamar baby har bacci yai gaba da ita .

Ajiyar zuciya ya sauke can kuma sai wasu zafafan hawaye suka sauko daga idonsa , kallon sa ya kai ga Afnan dake ta bacci hankalinta kwance amma fuskarta duk alamun hawaye gasunan ..

In ya tuna Sadiq ba ษ—ansa bane sai ya saki wani mahaukacin kuka mai ban tausayi , yana cikin hakan ne yaji ring ษ—in wayarsa ..

Kasancewar ya bar wayoyinsa a palo ya miฦ™e a hankali ya isa gurin wayar da ษ—aga warsa, my son yagani sai da yakuma zubar da hawaye sanan ya ษ—aga wayar, kafin yayi magana yaji Sadiq yace “dady na koma school fa gashi yanzu banida wasu kuษ—i a hanuna , jimm Abdallah yayu can kuma yace “zan tura maka zuwa anjima inna fita , nagode dady Sadiq yace ” lokacin da Abdallah ya jiyo ฦ™arar tafi da dariyaku ya kashe wayar , kirane yakuma shigowa a karo na biyu Abdallah ya ษ—aga a fusace yace “wai lafiya ?am dady wayar momy ce tun jiya a kashe dan Allah in kuna kusa ka bata , bana kusa Abdallah ya bashi amsa a taฦ™aice ya kashe wayar duka ma.”

Lefin momynsa yana neman shafarsa ko da yake yanata shawara da zuciyarsa akan ya fito ya faษ—awa Sadiq ba shine ubansa ba sai kuma ya kawar da tunanin , ya shafe mimtuna a gurin yanata tunani iri iri amma babu wata mafita da yaga ta dace , kwanciya yayi a doguwar kujerar tare da ษ—aga kansa sama , yau ษ—innan a tunani ya ฦ™are , bayan Afnan ta tashi tayi wanka ta shirya cikin doguwar riga baฦ™a mai adon faraten dutsina ba ฦ™aramin kyau tayi ba , samun Abdallah tayi kwance a palo bacci ya ษ—aukesa gashi lokacin ฦ™arfe shida na yamma , kasa tashinsa tayi kwai ta miฦ™e tayi hanyar kitchen,

Abinci mai sauฦ™i ta yi doya da miyar ฦ™wai dan yau tunda taga mai gidan babu walwala take jinta babu daษ—i , tana gamawa ta dawo palo ta zauna gefensa tana shafa fuskarsa a hankali , buษ—e ido yayi yana salati “ana kiran sallah fa , oky yace “tare da miฦ™ewa ya nufi hanyar toilet , bin bayansa da kallo tayi tana mamakin sayawarsa daga fitarsa zuwa yanzu , kodai wani ya ษ“ata masa rai ne ? ta tambayi kanta , dawowarsa ce yasata ษ—ago kai tare da cewa Allah ya tsare amen yace “yasa kai ya ficeโ€ฆ.โœ๏ธ.

Babu sharhi ๐Ÿคจ?.

๐Ÿ’ฆ๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐Ÿ’ฆ
๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’

LAMARIN ฦ˜ADDARAR AURE NA!!! .

  ๐Ÿ’     ๐Ÿ’       ๐Ÿ’

๐Ÿ’ฆ๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐Ÿ’ฆ

Story and writing by

ZAINAB HABIB
(mom islam)

My wattpad momislam2020

My telegram link

https://t.me/joinchat/IaKr804dfndik1e2

Zainabhabibu713gmail.com

WANAN LITTAFI GABA ฦŠAYANSA SADAUKARWA NE GA SHUGABA

(ANTY HAUWA MAMAN USWAN)

ALLAH YA ฦ˜ARA MIKI LAFIYA DA NISAN KWANA

๐Ÿ’ฆAREWA WRITERS ASSOCIATION๐Ÿ’ฆ

EPISODE 35 & 36

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM

Washe gari safiyar litinin (monday) Maimunatu ta tashi da wani matsanancin ciwon mara da baya , jin shiru har ฦ™arfe takwas bata fito ba yasa mama nufar ษ—akin , jiyo nishin Maimunatu yasa hankalinta mugun tashi ta shigo a guje , ganinta tayi durฦ™ushe tanata juyi idanunta sunyi ja , subhannallah mama tace " tare da kamo mai munatu ta gyara mata tsuguno , yau kam babu magana kuma bata yiwa mama musu , ganin abin ya wuce tunani gashi dai alamun  aihuwar ce amma har yanzu shiru , sake Maimunatu tayi ta wuce ษ—akin Haisam dake bacci ..

Bugun ฦ™ofar takeyi tana ฦ™wala masa kira , a tsorace ya taso ya buษ—e ฦ™ofar yace "lafiya mama?" inafa lafiya maza fito kazo ka ษ—auko mashin ษ—inka muje asibiti wanan yarinyar inaga aihuwa ce , ai dajin tace aihuwa ce yasashi azamar sauya kaya ya fito da sauri mama ta kwaso kayan yaro , kasancewar ba zaman daษ—i sukeyi dashi ba amma yana siyo kayan jarirai , kai tsaye suka nufi asibiti ,da isarsu aka wuce ,da Maimunatu ษ—akin aihuwa ..

Mama da Haisam sun zuba tagumi kawai jira suke suji ance ta aihu ,

ฦangaren Maimunatu likitoci ne zagaye a kanta sunata aiki ,itako batasan inda kanta yake ba ,adu’a sukeyi duk wacce ta faษ—o musu amma kaf ษ—insu hankalinsu ya fara tashi , tun ฦ™arfe tara na safe gashi yanzu ฦ™arfe biyar na yamma , wata likita ce ta fito fuska babu walwala ganin hakan yasa mama miฦ™ewa da sauri Haisam da bai san ko mai ke faruwa shima ya miฦ™e , hango likitar yayi ta doso gurin su โ€ฆ

Tun a zuciyarsa yafara mai maita innalilahi haka mama itama , likitar ce tace “waye mijin Maimunatu a nan ko kai ne ? ta nuna Haisam ,cikin tashin hankali yace ” nine ok “kazo office munason ganinka , to Haisam yace “jin ba abinda yake tunani bane yasashi sakin fuskarsa ,

Da sallama ya shiga ya nemi guri ya zauna likitar da tazo ta kirashi ne takuma cewa malam muna mai baka haฦ™uri akan rashin matarka , a razane Haisam ya miฦ™e daga zaman da yayi yace " ban gane ba ?".

Kina nufin Maimunatu ce ta rasu ? wani doctor dake gefe tunda Haisam ya shigo bai ce komai ba yace ” abokina kayi haฦ™uri kulli nafsin za’ikatull maut kayi haฦ™uri adu’arka take buฦ™ata ..

Da zamuyi maka magana kasa hannu ayi mata aiki to muna tunanin aihuwar da saura   amma Allah da kansa ya ฦ™arษ“i abarsa ."

Mama jin Haisam shiru bai dawo ba yasata neman gurin zama amma tanajin yawan faษ—uwar gaba , hangoshi tayi yana share hawaye kamar ฦ™aramin yaro , a saninta Haisam bai cika zubar da hawaye ba inba babban abu ne ya faru ba , lallai akwai abinda ya faru mama ta faษ—a a fili “.

Ad

_____

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button