LAMARIN KADDARAR AURE NA COMPLETE NOVEL

Ad
_____
Zama tayi jugub a kujera tana share gumin da yake karyo mata tare da mai maita innalilahi a zuciyarta .
Abdallah wayarsa ya ciro yafara danne danne amma inka lura dashi sosai hankalinsa a tashe yake ,
Ko kaษan bata ฦaunar taji yayi mata magana hakan yasata miฦewa ta nufi hanyar da zata sadata da bedroom ษinta keee!!! taji Abdallah yace ” cikin tsawa juyowa tayi batare da tace “komai ba ,
Kuma maida hankalinsa kan wayar dake hanunsa yayi a zahiri kukan zuci yakeyi dan nafili yaฦi fitowa .
Takai wasu mintuna a tsaye a gurin dan yanzu tsoransa ma takeji kar tayi ฦwaฦwaran motsi ya yanke mata mumunan hukunci,
Tashin hankali gami da rashin ฦaunar maman sadiq ya darsu a zuciyar Abdallah ,mai maicin da zuciyarsa take yimasa shine zina ?zina tayi kenam ba ษana bane ?” ya ilahi ya riฦe kansa da yake sara masa.”
Ya ษago kansa ya dubi maman Sadiq yace “naji duk abinda kuke ta taunawa akai dame na rageki ci ko sha ko tufafi kokuma haฦinki ne bana saukewa kiji tsoron Allah ,
Yaci gaba da cewa kin cuceni kin cuci ษanki dan bazance ษana ba ,
Momyn Sadiq jira take taji kalamin Abdallah na ฦarshe yace ya yafe mata sai taji akasin hakan yace ” na sakeki saki biyu inkin sami miji kiyi aure kuma ki tafi da ษanki banida alaฦa dashiโฆ..โ๏ธ.
Fans kuyi haฦuri kwana biyu kunjini shiru nayi tafiya ne amma na dawo ganin sharhinku shine zai sa kusami pagin gaba amma in bangani ba sai bayan sallah gaskiya ๐ค.
๐ฆ๐น๐น๐น๐น๐น๐ฆ
๐ ๐ ๐
LAMARIN ฦADDARAR AURE NA!!! .
๐ ๐ ๐
๐ฆ๐น๐น๐น๐น๐น๐ฆ
Story and writing by
ZAINAB HABIB
(mom islam)
My wattpad momislam2020
My telegram link
Zainabhabibu713gmail.com
WANAN LITTAFI GABA ฦAYANSA SADAUKARWA NE GA SHUGABA
(ANTY HAUWA MAMAN USWAN)
ALLAH YA ฦARA MIKI LAFIYA DA NISAN KWANA
๐ฆAREWA WRITERS ASSOCIATION๐ฆ
EPISODE 33 & 34
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
Kasa tsayuwa tayi a gurin saboda wani jiri dake ษibarta ta durฦusa kan guwaiwar ta tana kuka mai tsuma zuciyar mai karatu oh ni ฦดa su ina zansa kai na ,rarrafowa gabansa tare da sunkuyar da kanta ฦasa tace “dan darajar iyayenka ka yafemin wlh ba ‘asonโฆ!!! wani wawan mari ya wanketa dashi kana ya miฦe tsaye yace “kar in dawo in samu kina gidannan wlh sai kinyi dana sani , ya fice zuciyarsa na suya , driving yakeyi amma hankalinsa a tashe yake ,ikon Allah ne ya kaishi gida , ko horn baiyi ba ya buษe murfin motar ya fice tare da buษe get ษin , mai gadi dake zaune a wata farar kujera ta roba ganin Abdallah ya shigo a fusace ya miฦe yana cewa Alhji barka dai ywwa kawai yace .”
Bai jira ฦara jin wata maganar ba ya shige ciki , mai gadi ne ya jinjina kai ya ฦwalawa driver kira da sauri ya taho sabda shima ya lura da yanayin Alhajin .”
Wangale get ษin yayi ya shigo da motar, sukazo suka zauna kafa hirar shigowar uban gidan nasu ,
Bai sameta a palo ba ya nemi guri ya zauna , kashe tv da yaketa ฦararsa shi kaษai yayi , ya ษora ฦafa ษaya kan ษaya abubuwan da suka faru tsakaninsa da momyn Sadiq suka fara dawo masa ..
Cikin zuciyarsa yace ” ko kaษan banyi dana sanin rabuwa dake ba dan bansan ko bada ni kaษai kike taraiyya ba .
Shigowar Afnan ce ta sanyashi katse tunanin tare da faษaษa fara’arsa irin karta gane yana cikin wani hali , takowa takeyi cikin isa da ฦasaita ,
kai kace ฦดar wani sarkin ce .”
Zama tayi gefensa tare da ratayo hanunta a kafaษarsa tace “lafiya mijina ? naga kamar kana cikin damuwa ” a’a Afy kaina ke ciwo yanzu ma so nakeyi na ษan kwanta ..
Badan ta yarda ba ta ฦyaleshi amma ta fuskanci akwai abinda yake damunsa jikinta a sanyaye tayi bedroom ษinta ta fashe da kuka ,
jiyo kukan yayi lokacin da zaiyi hanyar bedroom ษinsa ya dawo zuwa ษakin nata , dole ya jata gado ya rungume ta yana jijiga ta kamar baby har bacci yai gaba da ita .
Ajiyar zuciya ya sauke can kuma sai wasu zafafan hawaye suka sauko daga idonsa , kallon sa ya kai ga Afnan dake ta bacci hankalinta kwance amma fuskarta duk alamun hawaye gasunan ..
In ya tuna Sadiq ba ษansa bane sai ya saki wani mahaukacin kuka mai ban tausayi , yana cikin hakan ne yaji ring ษin wayarsa ..
Kasancewar ya bar wayoyinsa a palo ya miฦe a hankali ya isa gurin wayar da ษaga warsa, my son yagani sai da yakuma zubar da hawaye sanan ya ษaga wayar, kafin yayi magana yaji Sadiq yace “dady na koma school fa gashi yanzu banida wasu kuษi a hanuna , jimm Abdallah yayu can kuma yace “zan tura maka zuwa anjima inna fita , nagode dady Sadiq yace ” lokacin da Abdallah ya jiyo ฦarar tafi da dariyaku ya kashe wayar , kirane yakuma shigowa a karo na biyu Abdallah ya ษaga a fusace yace “wai lafiya ?am dady wayar momy ce tun jiya a kashe dan Allah in kuna kusa ka bata , bana kusa Abdallah ya bashi amsa a taฦaice ya kashe wayar duka ma.”
Lefin momynsa yana neman shafarsa ko da yake yanata shawara da zuciyarsa akan ya fito ya faษawa Sadiq ba shine ubansa ba sai kuma ya kawar da tunanin , ya shafe mimtuna a gurin yanata tunani iri iri amma babu wata mafita da yaga ta dace , kwanciya yayi a doguwar kujerar tare da ษaga kansa sama , yau ษinnan a tunani ya ฦare , bayan Afnan ta tashi tayi wanka ta shirya cikin doguwar riga baฦa mai adon faraten dutsina ba ฦaramin kyau tayi ba , samun Abdallah tayi kwance a palo bacci ya ษaukesa gashi lokacin ฦarfe shida na yamma , kasa tashinsa tayi kwai ta miฦe tayi hanyar kitchen,
Abinci mai sauฦi ta yi doya da miyar ฦwai dan yau tunda taga mai gidan babu walwala take jinta babu daษi , tana gamawa ta dawo palo ta zauna gefensa tana shafa fuskarsa a hankali , buษe ido yayi yana salati “ana kiran sallah fa , oky yace “tare da miฦewa ya nufi hanyar toilet , bin bayansa da kallo tayi tana mamakin sayawarsa daga fitarsa zuwa yanzu , kodai wani ya ษata masa rai ne ? ta tambayi kanta , dawowarsa ce yasata ษago kai tare da cewa Allah ya tsare amen yace “yasa kai ya ficeโฆ.โ๏ธ.
Babu sharhi ๐คจ?.
๐ฆ๐น๐น๐น๐น๐น๐ฆ
๐ ๐ ๐
LAMARIN ฦADDARAR AURE NA!!! .
๐ ๐ ๐
๐ฆ๐น๐น๐น๐น๐น๐ฆ
Story and writing by
ZAINAB HABIB
(mom islam)
My wattpad momislam2020
My telegram link
Zainabhabibu713gmail.com
WANAN LITTAFI GABA ฦAYANSA SADAUKARWA NE GA SHUGABA
(ANTY HAUWA MAMAN USWAN)
ALLAH YA ฦARA MIKI LAFIYA DA NISAN KWANA
๐ฆAREWA WRITERS ASSOCIATION๐ฆ
EPISODE 35 & 36
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
Washe gari safiyar litinin (monday) Maimunatu ta tashi da wani matsanancin ciwon mara da baya , jin shiru har ฦarfe takwas bata fito ba yasa mama nufar ษakin , jiyo nishin Maimunatu yasa hankalinta mugun tashi ta shigo a guje , ganinta tayi durฦushe tanata juyi idanunta sunyi ja , subhannallah mama tace " tare da kamo mai munatu ta gyara mata tsuguno , yau kam babu magana kuma bata yiwa mama musu , ganin abin ya wuce tunani gashi dai alamun aihuwar ce amma har yanzu shiru , sake Maimunatu tayi ta wuce ษakin Haisam dake bacci ..
Bugun ฦofar takeyi tana ฦwala masa kira , a tsorace ya taso ya buษe ฦofar yace "lafiya mama?" inafa lafiya maza fito kazo ka ษauko mashin ษinka muje asibiti wanan yarinyar inaga aihuwa ce , ai dajin tace aihuwa ce yasashi azamar sauya kaya ya fito da sauri mama ta kwaso kayan yaro , kasancewar ba zaman daษi sukeyi dashi ba amma yana siyo kayan jarirai , kai tsaye suka nufi asibiti ,da isarsu aka wuce ,da Maimunatu ษakin aihuwa ..
Mama da Haisam sun zuba tagumi kawai jira suke suji ance ta aihu ,
ฦangaren Maimunatu likitoci ne zagaye a kanta sunata aiki ,itako batasan inda kanta yake ba ,adu’a sukeyi duk wacce ta faษo musu amma kaf ษinsu hankalinsu ya fara tashi , tun ฦarfe tara na safe gashi yanzu ฦarfe biyar na yamma , wata likita ce ta fito fuska babu walwala ganin hakan yasa mama miฦewa da sauri Haisam da bai san ko mai ke faruwa shima ya miฦe , hango likitar yayi ta doso gurin su โฆ
Tun a zuciyarsa yafara mai maita innalilahi haka mama itama , likitar ce tace “waye mijin Maimunatu a nan ko kai ne ? ta nuna Haisam ,cikin tashin hankali yace ” nine ok “kazo office munason ganinka , to Haisam yace “jin ba abinda yake tunani bane yasashi sakin fuskarsa ,
Da sallama ya shiga ya nemi guri ya zauna likitar da tazo ta kirashi ne takuma cewa malam muna mai baka haฦuri akan rashin matarka , a razane Haisam ya miฦe daga zaman da yayi yace " ban gane ba ?".
Kina nufin Maimunatu ce ta rasu ? wani doctor dake gefe tunda Haisam ya shigo bai ce komai ba yace ” abokina kayi haฦuri kulli nafsin za’ikatull maut kayi haฦuri adu’arka take buฦata ..
Da zamuyi maka magana kasa hannu ayi mata aiki to muna tunanin aihuwar da saura amma Allah da kansa ya ฦarษi abarsa ."
Mama jin Haisam shiru bai dawo ba yasata neman gurin zama amma tanajin yawan faษuwar gaba , hangoshi tayi yana share hawaye kamar ฦaramin yaro , a saninta Haisam bai cika zubar da hawaye ba inba babban abu ne ya faru ba , lallai akwai abinda ya faru mama ta faษa a fili “.
Ad
_____