LAMARIN KADDARAR AURE NA COMPLETE NOVEL

LAMARIN KADDARAR AURE NA COMPLETE NOVEL

Da zamuyi maka magana kasa hannu ayi mata aiki to muna tunanin aihuwar da saura   amma Allah da kansa ya ƙarɓi abarsa ."

Mama jin Haisam shiru bai dawo ba yasata neman gurin zama amma tanajin yawan faɗuwar gaba , hangoshi tayi yana share hawaye kamar ƙaramin yaro , a saninta Haisam bai cika zubar da hawaye ba inba babban abu ne ya faru ba , lallai akwai abinda ya faru mama ta faɗa a fili “.

 Yana isowa gurinta yace " mama ta mutu !!zaro ido mama tayi tanajin abin kamar a mafarki ƙarya kakeyi Haisam ,waye ya mutu ?Maimunatu ya bata amsa innalilahi ta bazama cikin asibitin da gudu , binta Haisam yayi yana ƙwala mata kira amma ina sai da tayi ɗakin da gawar Maimunatu take ta bude gawar da aka lulluɓeta da farin mayafi , salati ta dinga rafkawa tana surutai marasa amfani ..

Ashe tafiya zakiyi kintafi da ciki , tsayawa Haisam yayi a bakin ƙofa idanunsa cike da hawaye yana share wa wani na biyo baya , haka likitocin suka shigo suka samesu suma sun tausaya musu amma dayake lamarin na Allah ne da yafi kowa so ya karɓi abinsa suka cigaba da yiwa su Haisam nasih.

Haka ‘asibitin suka bada mota aka sa gawar Maimunatu suka nufi gida , tun a hanya Haisam yafara sanar da ƴan uwansu dana Maimunatu , mahaifiyarta ko kuka tasa tana ihu ,

Kafin su ƙaraso an ɓalle ƙofar gidan mutanen kusa sunata shigowa , da shigarsu aka wuce ta gawar ɗakinta aka ɗibi ruwan ɗumi aka yimata wanka aka karɓo likafani a masallaci , aka suturce ta, kasancewar iyayenta duk sunzo ana fito da gawar ta mahaifiyarta ta miƙe tana ihu wani malami ne ya fara yimata wa’azi da ban haƙuri , kuka kam ansha haka aka kaita makwancin ta rai kenan baƙon duniya.

Gida ya cika da ƴan uwa da abokan arziƙi mama kam hauka ne batayi ba amma tadingi kuka sosai ga cikin babu tadinga mai maitawa a cikinzuciyarta…✍️.

Follow me on wattpad momislam2020

????????????????????????????
???? ???? ????

LAMARIN ƘADDARAR AURE NA!!! .

  ????     ????       ????

????????????????????????????

Story and writing by

ZAINAB HABIB
(mom islam)

My wattpad momislam2020

My telegram link

https://t.me/joinchat/IaKr804dfndik1e2

Zainabhabibu713gmail.com

WANAN LITTAFI GABA ƊAYANSA SADAUKARWA NE GA SHUGABA

(ANTY HAUWA MAMAN USWAN)

ALLAH YA ƘARA MIKI LAFIYA DA NISAN KWANA

????AREWA WRITERS ASSOCIATION????

EPISODE 37 & 38

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM

Duk abinda Sadiq ya nema Abdallah ya tura masa harda kuɗi masu yawa , washe gari yayi sammakon zuwa gidan su momyn Sadiq ,samu yayi ta kwashe duk wani kaya nata durƙusawa yayi a gurin ya saki wani kuka mai cin rai a fili yace ” ina sonki wlh ina sonki amma soyayyar da nake yimiki bazai sa inkasa yanke hukunci dai dai da abinda kika aikata ba , fuskarsa tayi shaɓe shaɓe da hawaye kamar ƙaramin yaro , miƙewa yayi ya nufi bedroom ɗinsa ya kwanta zuciyarsa fall baƙin ciki da haka bacci mai nauyi yayi nasarar ɗaukarsa , ya daɗe yana baccin tare da mafarkai iri iri na ban tsoro rin ɗin wayarsa ce ta tashe sa daga bacci salati yayi kana ya janyo wayar ya danna ya kara a kunne ,wlkslm naji yace ” daga ɗayan ɓangaren akace ango hutun ya isa haka ma’aikata nada buƙatar ka kuma kasan gobe za’ayi taron cika shekara biyar da buɗe ma’aikatar mu bamuyi wasu shirye shirye ba? innalilahi Abdallah yace “.

garin ya hakan ta faru kash mutumin da yakira ne yace “bye zai zuwa goben , tom kawai Abdallah yace ” kana ya shige toilet ya watsa ruwa yana fitowa ya cigaba da tunane tunanen sa , da sauri ya saka kaya ya fice daga gidan yaukam kowa ya gansa yasan babu lafiya kasancewar ko mai bai shafa ba , abubuwa sun taru sun yi masa yawa ga matsalarshi da momyn Sadiq ga gurin aiki .

Washe gari tunda ya dawo daga masallaci da asbha bai koma bacci ba ,shirye shirye yaketa yi na inda lamarin taron zai kasance , dan ma abinka da mai kuɗi kira yakeyi a waya a gudanar da komai , bayan Afnan tayi sallah asbha ta nufi ɗakinsa da sanyin jiki , samunsa tayi a zaune da wasu takardu a gabansa da alama na aikin ne , zama tayi dab dashi can kuma ta durƙusa tare da cewa ina kwana “lpy Abdallah yace “ya kike ina lpy sai dai tunanin ka , riƙe kai yayi yasan ko kusa bai kyautawa Afnan ba , naƙin kulata kwana biyu janyota yayi kusa dashi tare da rungumeta , hakan ba ƙaramin daɗi yayi mata ba , dan tana tunanin ko tayi masa laifi ne ? amma yanzu ta gane uzuru ruka ne sukayi masa yawa .”

“Afy zoki shirya , Abdallah yace “lokacin da yake fitowa yana sanye da shadda ruwan toka sai ɗaukar ido takeyi , ganinan zuwa sweety Afnan tace ” kasancewar tun ɗazu ya gaya mata sunada taro , itama shaddar tasa kalar tashi ta ɗauko mayafi da takalmi marar tudu da jakarta fara kalar takalmin da wani glass baƙi ta sanya a idonta , wow gaskiya Afnan tayi kyau dayake ɗinkin doguwar riga ce ba ƙaramin fito da ƙyan dirinta tayi ba kallonta ya tsaya yi sbda shima tayi masa kyau , turare ya ɗauko ya fesa mata yana sakar mata murmishi , suna gamawa suka rufo ƙofar suka nufi gurinda aka tanadar domin ajiye motoci , da ganinsu driver ya taso da sauri ya buɗe mota suka shiga back side ya rufe , shikuma ya shiga gaba , hira sukeyi jefi jefi a motar , amma fuskar Afnan da alamun damuwa , Abdallah sam bai lura da yanayin ta ba kasancewar yanata amsa wayoyi na mutane , faɗuwar gaba takeji a kamar akwai wani abu dazai faru a gurin taronnan , wata zuciyar tace “ki koma gida kawai ‘ ina babu halin yin hakan yasa ta daure zuciyata tare da mai maita innalilahi.”

Sunyi tafiya mai nisa sannan suka iso tsararren gurin taron , misalta tsaruwar gurin ma ɓata lokaci ne gurin yashe gyara kasancewar hidimar ta manyan mutane ce abin ya birge , bayan angama bada kyau tutuka Abdallah ya tashi yayi jawabi akan cigaban kamfaninsu dakuma inda zasu dinga tafiyar da al’amura cikin sauƙi , Afnan dake gefe sai murmishi takeyi , hango wata farar budurwa nayi tana sanye da riga da sikel ɗan kanti ta yafa wani tsdadden mayafi mai kyau fuskarta dauke da kwaliya tanada manyan idanu farare ga gashin kanta dogo , dan anyi mata kitson gaba , cikin yanga take takun hanunta ɗauke da farar takarda dakuma flawoyi ta isa gaban Abdallah , ganin haka yasa Afnan jin wani mugun faɗuwar gaba kamar an caka mata kibiya , lokaci ɗaya murmishin ya ɗauke daga fuskarta hango wanan budurwa suna gaisawa da mijinta kuma hannu da hannu har tana lumshe masa idanu , kuma duk da haka bata bar gurin ba , baƙin ciki ne ya cika zuciyar Afnan ta miƙe tabar gurin , gurin da sukayi parking motarsu ta isa ta buɗe motar ta shige ciki , kuka ta fashe dashi kamar wacce aka aikowa da mutuwa,

Maiyasa maza suke haka ne ? .

wayarta ta ciro tafara dannawa amma hankalinta yana gurin wanan budurwa to wacece ita ?” babu mai bata amsar tambayarta a halin yanzu yasata yin shiru tare da ƙara fashewa da kuka.

Leƙenta Abdallah yakeyi amma sam bai ganta ba , budurwar dake gefensa ta lura da akwai abinda yake nema tace ” maiya faru big boy ?” murmishin yaƙe yayi kana yace ” nup bkm ina duba wani friend ɗina ne naga ma kamar ya tashi , oh budurwar tace ” ina matarka ne ? batanan amsar data fito daga bakinsa kenan , hakan ba ƙaramin daɗi yayiwa budurwar ba , tace “zamuje shan is cream ?sai da yayi jim kafin yace ”to babu matsala yarasa mai yasa baya iya yimata musu ko kad’an , fad’ad’a murmishinta tayi tace ”big boy har yanzu kak’i bani amsar tambayar da nayi maka shekara d’aya data wuce ko ?”.

Jiyo alamun tashin taro sukayi hakan yasa hankalin Abdallah komawa gurin Afnan ya ilahi , yace ” lokacin da ya tuna da ta dad’e da tashi a gurin gashi ko kiranta a waya baiyi ba , dafe da goshi ya yi hanyar fitowa ganin baiga motar tasu ba yasashi jin tsoro kardai Afnan ta tuk’a motar nan ne tayi gida ? yana tsaye yanata tunani kala kala har mutane suka fara fitowa suna mik’o masa hannu suna gaisawa annan ma sai da ya k’ara bata lokaci , janye jikinsa yati ya koma gefe guda ya danna number driver ✍️.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19Next page

Leave a Reply

Back to top button