Our website is made possible by displaying online advertisements to our visitors. Please consider supporting us by whitelisting our website.
LAMARIN KADDARAR AURE NA COMPLETE NOVEL

LAMARIN KADDARAR AURE NA COMPLETE NOVEL

Ad

_____

Murmishin yaฦ™e tahau yimasa dan tana tunanin inhr yaga wanan photon to kashinta ya bushe , Abdallah mutum ne mai lura da ankara ,yana ganin Afnan na wanan yaฦ™en dariya ce kawai baiyi mata ba amma a zahiri baiyi mata kyau ba kuma ya fara tunanin da akwai abinda yake faruwa da Afnan taฦ™i gaya masa ne , kasancewar da abinda ya dawo dashi ,ya riฦ™o hannunta tare da rungumota suka nufi kitchen soyayyen dankalin data soya ษ—azu ya zubo musu tana rungume a hanunsa suka dawo parlo a baki ya fara bata tanaci tana zuba shagwaษ“a ,amma a ฦ™asan zuciyarta tana fargabar ranar da sharin wanan budurwa zai hau kanta , kawar da zancen tayi kar Abdallah ya ganota.”

Kwance yake yanata saฦ™a da warwara shin ko ya amince da maganar mama na auran Uwani ne ? wata zuciyar ce tace ” aikuwa da ka auri ciwon kai , dafe kansa yayi dan yama rasa tunanin me zaiyi wanan wace irin jarabwa ce ? ya tambayi kansa , tashi yayi ya dawo palo kallon palon ya shigayi yaushe rabonsa da shara , tsaki yaja kana ya koma bedroom ษ—insa ya shiga toilet ya watsa ruwa , yana fitowa ya zauna nanma dai tunanin ne ya addabi zuciyarsa , badan yaji ance Afnan tayi aure ba da babu abinda zai hana ya dawo da ita , wasu siraran hawaye ne suka zubo masa , sharewa yayi ya fara shafa mansa mai ฦ™amshi , bayan ya gyara sumar kansa ya feshe jikinsa da turare , yaje gaban drower buษ—ewa yayi ya tsaya a gurin yana tunanin kalar kayan da zai sa tuno kalar kayan da Afnan takeso yayi wato farin boyel da farar baฦ™ar hula da takalmi baฦ™i sai agogo fari , bayan ya sa ne ya dubi kansa a mudubi yai wani murmishi wanda ya ฦ™ara fito da ainihin kyansa can kuma ya dake tare da ษ“ata rai , to wa nayiwa wanan kwaliyar ? hhhh lol niko nace Uwani โ€ฆkey ษ—in mashin ษ—insa ya ษ—auka tare da rufo ฦ™ofar ya nufi waje ,Faty da ta fito daga maฦ™ota ganin Haisam ya tuno mata da Afnan hawaye tabb ฦ™wayar idonta ta shige gida ,Haisam bai lura da abinda ke wakana ba yaja mashin ษ—insa ya nufi gidansu mama , dan yanason zuwa gurin aiki da wuri.

Da isarshi anguwar tasu ya hango Uwani taci ษ—amara tana shirin faษ—a da wata budurwa wacce a shekaru ta zarce ta amma tana shirin faษ—a da ita taษ“ษ“ , Haisam ne ya jinjina kai kana ya tada mashin ษ—insa ya nufi gida , yana shiga ya sami baba a kan kujera ฦดar tsugunno yana shan kunu , baba na ganin Haisam ya hau washe baki yana fara’a , durฦ™usawa Haisam yayi ya gaida baba amsawa baba yayi yace ka shiga ciki a zubo maka kunun naฦ™oshi Haisam yace ” tare da miฦ™awa baba dubu biyar , baba zai yi magana Haisam yace” baba kayi shiru kawai ,share hawaye baba yayi kana yace ” Allah yayi maka albarka Allah ya baka mata tagari Allah ya yalwata arziฦ™inka , dajin wanan adu’ar sai da jikin Haisam yayi sanyi sosai,

Saurin miฦ™ewa yayi dan kar mama ta ritsashi a gurin , kasancewar da tazara kaษ—an tsakanin gurin da baba ke zaune dakuma ษ—akin mata , yasa Haisam wucewa can kukan Uwani ya jiyo da robar ษ—ibar ruwa yayi gashi robar a fashe ,dariya ce taso kuษ“uce masa sai ya gimtse , Uwani ce ta kalli Haisam da yabata haushi a rayuwarta ta tsani abu ya faru da ita aฦ™i jajanta mata tace “ษ—an yaya ษ—an gayu wlh kayiwa wanan yarinyar magana dan ni ba sa’ar wasanta bace tamm,

Kallon inda take magana da girgiza yayi bai ce mata komai ba ya nufi ษ—akin mama , shiga yayi ya zauna kasancewar ta shiga wanka , Uwani da baฦ™in ciki ya isheta kasa zama tayi a ษ—akin tayo waje , mama ce ta hangota a zaune bakin ฦ™ofa tana bubuga ฦ™afa alamun masifa , a ‘ a Uwani me kuma ya faru?” fashewa tayi da kuka tace ” ina cikin ษ—ibar ruwa a famfo shine wata gardiyar budurwa tazo ta janye bokiti na tasa nata ,shine nikuma na janye nata shine suka yimin taron dangi harda fasamun bokiti , Haisam tun yana dariya a ciki ciki bai sani ba ta yanzu harda ฦ™ya ฦ™yatawa maganar yarinyar na sashi dariya

๐Ÿ’ฆ๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐Ÿ’ฆ
๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’

LAMARIN ฦ˜ADDARAR AURE NA!!! .

  ๐Ÿ’     ๐Ÿ’       ๐Ÿ’

๐Ÿ’ฆ๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐Ÿ’ฆ

Story and writing by

ZAINAB HABIB
(mom islam)

My wattpad momislam2020

My telegram link

https://t.me/joinchat/IaKr804dfndik1e2

Zainabhabibu713gmail.com

๐Ÿ’ฆAREWA WRITERS ASSOCIATION๐Ÿ’ฆ

EPISODE 45 & 46

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM

Mama ce ta shigo tace “wato kanaji tana kuka baka fita kaga wacce suke faษ—an da ita ba ? sunkuyar da kai yayi tare da cewa mama ai tafi mai faษ—an ฦ™arfi , hakan ya kuma tunzura Uwani tukuma fashewa da kuka ,

 Safiyar Laraba  ฦ™arfe 7:am dai dai  Afnan ta shiga wanka sbda zuwa ษ—auko Sadiq  tunda Abdallah ya lura da harda wanke kai zatayi dan yaga ta ษ—auki shampo , ya ษ—auki wayarta cikin azama yafara bincike ko ina na wayar gallery ya shiga , mai hankalinsa yayi ga hotunan wayar gana bikinsu gana ฦ™awayenta  , gurin hotunan whtsapp ya shiga cin karo yayi da hoton ta daga ita sai pant da bra innalilahi Abdallah yace " ya cigaba da bincika wayar sai kuma ya ga hotonsu shida husna , kansa ya fara ษ—aurewa a ina husna ta san numbar Afnan ? dama sunada alaฦ™a da ita ne ? komawa whtsapp yayi anan yaci karo da lambar Husana sbda ya haddace ta a kansa  ba tun yau suke tare ba, gir giza kansa yayi tareda cije lips ษ—insa , yasan sharrin Husna  fitowar Afnan ne ya sanyashi ฦ™are mata kallo dan ya riga ya ajiye wayar bayason ta fahimci akwai wata matsala , janyota yayi ya kaita gaban drees mirror ya zaunar da ita gaban stool ya shafa mata mai kana ya shafa mata hoda , taฦ™i sakewa dan tana tunanin yaga pic ษ—in ,  

Kasancewar yayi nashi wankan bayan ta gama shiryawa suka fito dama driver ya shirya suka ษ—auki hanya direct gurin da Sadiq yayi musu kwatance suka tsaya , Abdallah ne ya ฦ™ara kiransa yace ” sun ฦ™araso , daga can ษ“angaren Sadiq ya ratayo school bag ษ—insa ya fito bayan ya bada keys ษ—in ya nufi bakin get , yiwa mai gadi sallama yayi ya buษ—e murfin get ษ—in , hango motar dadyn yayi ษ—an nesa da da get ษ—in , ya ษ—anyi tafiya mai tsayi kana ya iso , ba tare da yayi magana ba ya buษ—e gidan gaba ya zauna yai kicin kicin da rai ,

Afnan ce tace ” ayi mana afuwa , Sadiq dake cika yana batsewa ya dubi side ษ—in da dadyn ke zaune yaga bama tashi yakeyi ba , dane danen wayarsa yakeyi hawayen da bai shirya zubowarsu bane suka zubo masa , sharewa yayi ya maida hankalinsa ga kallon titi ,Abdallah ko yana kallon Sadiq duk wani abu da yakeyi yanzu kam ya fiddashi daga cikin jerin ฦดaฦดansa , tabbas Sadiq baiyi kama da jininsa ba , suna cikin tafiya naji Abdallah yace ” driver juya zuwa wancan titin kaf ษ—insu ba susan ina zasuje ba hakan yasa kowa yai shiru ya zubawa kwalta ido tunda suka shiga layin gabab Sadiq ke faษ—uwa , Abdallah ne yace ” is ok bayan driver yayi parking suka fito banda Sadiq da ya zauna bama shida niyar fitowa.”

Wata tsawa Abdallah ya daka masa mai firgitarwa , ba ฦ™aramin firgita Sadiq yayi ba dan a iya saninsa dadynsa baya ko yimasa kallon banza bare wanan tsawar a tsorace ya fito , shima driver dake gefe lamrin ya matuฦ™ar bashi mamaki dubada irin soyayyar da Abdallah ke yiwa ษ—an nasa katse tunanin yayi dan yaga sun shige ciki Sadiq ne a baya kamar wanda aka doka , dan ya firgita matuฦ™a , 



 Gidane dai dai misali bazaka kirashi da gidan talakawa ba ,zadai ace gidan masu rufin asiri gidane mai ษ—auke da ษ—an madai daicin get sai filin tsakar gidan da yake malale da siminti daga can ษ“angare hagu wani kasko ne guda biyu masu flawoyi ,ฦ™ofar da zata sadaka da sashe matar gidan itace ฦ™ofar dake kallon ymma kasancewar ฦ™ofofi biyune kusan a jere , babu sashin da Abdallah bai sani ba dan haka ya shige ฦ™ofar dake ษ“angaren dama suma suka rufa masa baya , da sallama a bakinsu suka shige matar gidan na tsakar gida tana wanke wanke ta ga su Abdallah , washe haฦ™ora tayi tare da cewa" lalle marhabun barkanku to kai Sadiq ka shiga dasu man jiki a sanyaye Sadiq yayi musu jagora zuwa babban palon gidan , zaune take a cikin ษ—aki a gefen katifa taci kuanta ta godewa Allah musamman da sukayi waya da Sadiq ya faษ—a mata a hotel ya kwana ta razana sosai , jiyo muryar mamy na kiran sunan Sadia yasata aiyanawa a ranta cewar ai harda Abdallah ma , 

Miฦ™ewa sadiq yayi yahau bankaษ—a labule yana duba islam wato autar mamy , bankaษ—o na ษ—akin da momynsa ke ciki yayi da sauri ya isa gareta ganin hawayen fuskarta yasa shi fara shre mata hawaye ,

Afnan dake zaune gefen Abdallah da sai yanzu ta sami damar yin mgna tace ” ina mukazo ? gidansu momyn Sadiq ya bata amsa a taฦ™aice , jan bakinta tayi tai shiru kana ta zubawa sarautar Allah ido , mamy ce ta shigo hannunta ษ—auke da jug na ruwa da food flaks na abinci ajiywa tayi a gaban su Sadiq kana ta zauna kujera mai kallon tasu , sauka yayi daga kan kujerar yace ” mamy barka da yamma mamy ywwa barka ya gida ya aiyuka lpy lou Abdallah yace” Afnan ma gaisheta tayi kana shiru ya biyo baya , Abdallah ne yace ” nakawo Sadiq ne , da alamun damuwa mamy ta dubeshi tace ” Abdallah naji duk abinda ke faruwa yanzu dai inason kayi haฦ™uri dan Allah banda tone tone , sunkuyar da kai Abdallah yayi yace ” mamy momyn Sadiq bata kyauta min ba wlh eh nasani , labarin bashida daษ—in sake mai maitawa dan Allah kadubi darajar maraici ka maidata ษ—akinta , Afnan sai yanzu ta gano abinda ke faruwa cikin sanyin murya tace “dama bakwa tare da mmn Sadiq? ko kulata bai yi ba shigowar momyn Sadiq da Sadiq ne suka shigo palon .”

 Kallonsa ya kai gareta kana ya sada kansa ฦ™asa  dan jiyakeyi kamar yaharbeta amma bashida mafita , kuma yana tausayawa rayuwar mutanen gidan kasancewar su masu ษ—an ฦ™aramin hali , gashi mamy nason matsa masa oh Allah Abdallah yace " lokacin da yakai dubansa ga Sadiq ya kauda kansa gefe , shikam ya tsani zina kokuma ษ—an zina ,sake kai dubansa gurin mamy yayi kana yace " da sharaษ—i inhar ta amince bazata jemin da Sadiq gidana ba , wata razananniyar ฦ™ara yasa tare da cewa" to waye mahaifina ki nunamin ."

Muryar Sadiq sukaji Afnan ce ta miฦ™e tare da riฦ™o masa hannu , cikin kakausar murya Abdalah yace " karki kuma gigina taษ“ashi ba jinina bane !!! timmm mamy ta faษ—i sumammiya , da sauri Afnan da momyn Sadiq sukayi kanta mai adu'a nayi mai ษ—ibo ruwa nayi ,duk da haka Abdallah bai dena zazzaga bala'i ba , momyn Sadiq ce tace "inhar kazo kawomin shi ne to , inkuma kazo tayar mana da hankali ne sai ka faษ—a , Afnan dai lamarin ya ษ—aure mata kai ta rasa wane lamari ne ke shirin faruwa da rayuwarta ?" a zuciyarta take wanan batun , eh duk inda kika ษ—auka haka ne , cewar Abdallah dan zan temaka na maidake wlh bacin tausayinki da nakeji babu abinda zai sa na maidake !!!, mamy na farfaษ—owa ta tsinkayo maganarshi ta ฦ™arshe , cikin dauriya dajin zafin kalamin nasa tace " Abdallah abin bai kai ga haka ba mungode basai ka mayarda ita gidanka ba , daganan ta shige ษ—aki , dukaninsu suna tsaye Sadiq ko yabi mamy ษ—akinta

๐Ÿ’ฆ๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐Ÿ’ฆ
๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’

LAMARIN ฦ˜ADDARAR AURE NA!!! .

  ๐Ÿ’     ๐Ÿ’       ๐Ÿ’

๐Ÿ’ฆ๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐Ÿ’ฆ

Story and writing by

ZAINAB HABIB
(mom islam)

My wattpad momislam2020

My telegram link

https://t.me/joinchat/IaKr804dfndik1e2

Zainabhabibu713gmail.com

๐Ÿ’ฆAREWA WRITERS ASSOCIATION๐Ÿ’ฆ

EPISODE 47 & 48

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM

Afnan da tun usulinta batason tashin hankali tafara kuka tare da durฦ™usawa a gaban Abdallah ta riฦ™o masa hannu , kana tace ” dan darajar iyayenka ka kaida ta , bai yi magana ba sai ficewa da yayi daga ษ—akin , momyn Sadiq kasa magana tayi sbda baฦ™in ciki Afnan ce ta rungimeta suka dinga kuka, bayan fitarsa driver ya shigo a guje tare da cewa hajiya mai gida na mota yana jiranki ,sallama tayi musu kana ta rufawa mai gadi baya , buษ—e murfin motar tayi ta shiga suka miฦ™i titi , babu mai cewa kowa komai , shikam zuciyarsa tafar fasa takeyi kamar garwashi gaskiya da ba zina tayi ba zai iya mai data amma tuna abin ya kasance da haka yana ganin sai dai su haฦ™ura kawai , horn ษ—in da driver yayi ne ya tabbatar musu da cewar sun iso gida , buษ—e murfin motar tayi da sauri ta fice tana kuka , tana shiga palo ta wuce bedroom ษ—inta da gudu ta faษ—a gado tana wani irin kuka mai cin rai , ita kam tafi tausayin Sadiq ษ—in a kan mahaifiyar tasa , can kuma wata zuciyar tace ” ke meye naki na tausayin sa bayan bakida alaฦ™a dasu? gaki a cikin matsala ,

Ad

_____

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button