Our website is made possible by displaying online advertisements to our visitors. Please consider supporting us by whitelisting our website.
LAMARIN KADDARAR AURE NA COMPLETE NOVEL

LAMARIN KADDARAR AURE NA COMPLETE NOVEL

Ad

_____

Kawar da zancen tayi ta ษ—auko wayarta , lambar momy ta dannawa kira ring ษ—aya ta ษ—auka , sallama Afnan tayi bayan momy ta amsa Afnan tace “ya dady da anty suna lpy momy tace .

“lafiyarki kuwa Afnan?” naji muryar taki tayi kama da ta mai kuka , kuma dai dai ta muryar tayi kana tace ” llah momy wlh ba komai nayi missing ษ—inku ne inason zuwa , momy ce tace ” to shine zaki ษ“ata ranki ? ki kwantar da hankalinki muna lpy karki dinga tada hankali kinga ba ke kaษ—ai bace , waro ido Afnan tayi kana tace ” momy nikaษ—ai ce man au wai kun ษ—auka cikine da ni ? eh momy tace ” hmm wlh banida komai , cewar Afnan , momy ce tace ” Allah zai kawo ki kwantar da hanlalinki kinji , to tace ” tayiwa momy sallama , numbar anty ummi ta kira dan tasan tayi laifi yaushe rabon da suyi waya.”

Lokacin taga gidan Haisam tana cin azaba gurin mama batada wata uwa banda anty ummi yanzu kuma da ta auri burin iyayenta shine zata watsa mata ฦ™asa a ido ina , jin an ษ—aga wayar ya sata cewa aslamu alaikum , daga ษ—ayan ษ“angaren anty ummi tace " walaikissalam Afnan kinanan? uhm anty da farko dai ayimin afuwa dan Allah , nasan ban kyauta ba , share zancen anty tayi da cewa karki damu yarinyata ,


nan suka kuma gaisawa kana sukayi sallama  , turo ฦ™ofar da Abdallah yayi ne yasata kai dubanta ga inda ya ke , tsaye yake a bakin ฦ™ofa ya zura hannayensa cikin aljihu , ya kallonta.

Zaune suka a wani tsararren palo wanda yaji kayan more rayuwa wannan palo shine zakaji ana yiwa kirari da aljannar duniya , hajiya Maryam ce zaune kusada mai gidan nata wato Alhaji Aliyu mai nera , Alhaji Aliyu mai nera shaharaten mai kuษ—i ne na ji da gani , sananne ne kowa ya sanshi a babu wanda zaka yiwa kwatancen sunansa yace ” bai sanshi ba , shine uba ga Husna ฦดa ษ—aya tilo da Allah ya basu ,Husna tayi karatu sosai musamman ma na boko , har yanzu taฦ™i fito da mijin aure da zarar Alhaji yayi magana mahaifiyarta zatace guda nawa take karya takura mata , akwai wata rana tana cikin tafiya a motar ta , sai motar ta sami matsala , tana tsaye bakin titi motar Abdallah tazo wucewa , bayan ta sa masa hannu alamar ya tsaya ta roฦ™esa da ya temaka ya rage mata hanya zuwa gidansu,

Suna cikin tafiya tana satar kallonsa dan Abdallah kyakyawane in baku manta ba , suna isowa tace " ya bata lambarsa , baiyi mata musu ba ya bata har ya zamo daga wanan rana tana kiransa suna gaisawa , kwanci tashi asarar mai rai , Husna ta fara nunawa Abdallah tsantsar soyayya tun bai san tanayi ba har yazo ya gane , wata rana yazo gidansu badan yaso ba sai cewa da tayi zasu gaisa da mahaifiyarta , yake gaya mata shikam yanada mata , Husna tayu baฦ™inciki amma kadancewarta wayayya ta nuna babu komai gashi yac" bai shirya yin aure nan kusa ba , itadai a tata zuciyar ta ฦ™udiri aniyar auransa ko ta wane hali  wanan kenan.

Alhaji ne ya dubi Hajiya Maryam yace ” lokaci yayi da zan fitarwa da Husna mijin aure sbda lokutan da na ษ—aukar mata sun cika , kukan da Husna ta fara ne yasa su Alhaji juyowa kallonta , kuma bai fasa maganar ba , Hajiya Maryam ce tace “a wanan karon ina goyon bayanka ai tanada samarin ruwan ido ne yasa take rainawa mutane hankali , Husna batada zaษ“i banda dole ta karษ“i zaษ“in iyayenta amma kuka yaci ฦ™arfinta ,tashi tayi da gudu ta haura samma inada ษ—akinta yake , ta faษ—a gado tare da sakin wani sabon kukan , tunanin Abdallah da yayi mata nisa tafara yanzu yazanyi duk wata hanya da zanbi dan haddasa musu fitina na kasa dole nabi abinda su hajiya sukeso , da haka bacci mai nauyi yayi nasarar ษ—aukarta .”

Abdallah ne ya ฦ™araso kusa da Afnan ya ษ—auketa ya ษ—ora akan cinya kamar ฦ™aramar yarinya , raษ—a mata yayi a kunne wai two days mai ya sami baby na ne tadena bani kulawa ?” narkewa Afnan tayi kana tace ” nikam babu ruwana da kai , mekuma nayi ? cewar Abdallah , Afnan ce tace ” dan me bazaka dawo da matarka ba ?” walwalar fuskar Abdallah ce ta gushe ya kalli Afnan yace ” zaki iya zama da miji mazinaci ? zaro ido tayi tana kallon Abdallah da idonsa ya ciko da ฦ™wallah tare da girgiza kai , to inhar bazaki iya ba karki ฦ™ara yimin zancenta akwai maza a duniya bani kaษ—ai bane autan maza ya kamata kisani babu ni babu momy sadiq!!!!!.

Jin zancen nasa babu daษ—i takeyi amma babu inda zatayi dole ta kawar da zance dakuma tinanin momy Sadiq ta rungumi mijinta , rungumota yayi yana shafa mata gashin kanta tare da murza ฦดan yatsunta , itama fara yimasa wani salo tayi na daban dama tayi amfani da maganin da momy ta bata , tunda naga Abdallah ya fara harata yasani rufo musu ฦ™ofa nayo waje.

Yau Afnan ta tambayi zuwa gida , daฦ™yar Abdallah ya barta amma da sharaษ—in karta daษ—e, tun safe tayiwa momy waya akan gatanan zuwa , kowa na gidan murna yakeyi dan an daษ—e ba’a haษ—u ba , momy tasa an shirya mata abinci kala kala, dady ma yau bai fita ba sbda yanason su gaisa da ฦดarsa ,

Abdallah na fita ta fara shiri tana gyara gado taci karo da kuษ—i masu yawaa  tunani ta fara ko Abdallah ya mance dasu ne , ring ษ—in wayarta ne ya katse mata tunani , Abdallah me mai kiran amsawa tayi tare da cewa ka isa lpy , lpy lou sweety ina kewarki dariya Afnan tasa tare da cewa " kai mijina daga fitarka ? eh man Afy jinake kamar in dawo , zaro ido tayi kamar yana ganinta tasan inhar sukaci gaba da maganar zai iya dawowa yayi mata haramiyar zuwa gidansu , am sorry Allah ya dawomin dakai lpy mijina akwai tanadin da nayi maka so karkaji komai , nidai fatana karka bari ฦดan mata su kallemin kai , dariya sukasa a tare kowa ya ajiye wayar , dafa ฦ™irjinta tayi kana tace " my man rigima , tacigaba da shirinta

๐Ÿ’ฆ๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐Ÿ’ฆ
๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’

LAMARIN ฦ˜ADDARAR AURE NA!!! .

  ๐Ÿ’     ๐Ÿ’       ๐Ÿ’

๐Ÿ’ฆ๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐Ÿ’ฆ

Story and writing by

ZAINAB HABIB
(mom islam)

My wattpad momislam2020

My telegram link

https://t.me/joinchat/IaKr804dfndik1e2

Zainabhabibu713gmail.com

๐Ÿ’ฆAREWA WRITERS ASSOCIATION๐Ÿ’ฆ

EPISODE 49 & 50

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM

Biki ya kankama na Haisam da Uwani kasancewar mama tace ” inhar yabarta to yabar mata , badan yaso ba ya amince da abinda takeso tunda bazata fasa ba , fatanshi dai Allah ya sanya musu albarka shikenan , hidindimu akeyi sosai sbda yanzu Haisam kuษ—i sun zauna masa ba laifi harya siyi mota mai kyau ya kuma sauyawa gidan nasa fenti komai dai yayi masha Allah ,

Dama tunda iyayen Maimunatu suka zo suka kwashe kayanta ya kulle ษ—akin sai yau da za'ayiwa ษ—akin fenti ya buษ—esa , kowa sai sam barka yakeyi amma ana cece kuce akan amarya  ,ranar ษ—aurin aure kowanne na dangin mama da magoya bayanta suna farinciki sosai , da yamma za'a kai Uwani tunda taji alamun zuwan motoci tafara kuka ita bazatabi wancan mugun ba , karyazo yana yimata mugunta , kowadai lallaษ“ata yakeyi tunda Uwani dole sai lallaษ“o , tun a mota take rafka salati da koke koke kamar wacce za'a kai gidan yanka , ana isowa ฦ™ofar gidan nanma sai da aka ririฦ™eta tana neman guduwa , 


Mutane sunga tashin hankali , faษ—a aka yimata mai shiga jiki duk rashin kunyarta sai da jikinta yai sanyi , musamman da aka cemata banda yiwa mijinki musu banda yimasa rashin kunya , kasancewar tana tsoron ace wutar jahannama yasata yin laushi da duk wata masifa tata , haka suka tafi suka barta tana kuka , amma a ฦ™arฦ™ashin zuciyarta tsoron Haisam ne fal.

misalin ฦ™arfe goma da rabi kowa ya watse sai raba ido takeyi tana daga zaune a tsakiyar gado taji alamun turo ฦ™ofa, shi kaษ—ai ne sai wata ฦ™atuwar leda dake hanunsa , gyata zaman ษ—an mayafin tayi kana ta kalli ledar Allah yasa kazace , Uwani tace ” lokacin da ta haษ—iyi wani mugun yawu , zama yayi bakin gado tare da cire agogon hanunsa ya miฦ™e , Uwani tashi muje muyi sallah sai da taษ—an harareshi kana ta miฦ™e , kunsan dai mai hali baya fasawa amma a tunaninta ta rage rabi ,

Bakinnan kamar wanda aka ja dan fushi ita ba sallar bace damuwarta cin kazar shine matsalar ta , tana yin alwalalr ta dawo ษ—aki ta zauna gefen gado , Haisam na shigowa yace ” tashi muyi sallah ko kulashi batayiba ta miฦ™e sukayi sallahr ya shafa kanta yayi mata adu’oi kana yayi mata ฦดan tambayoyi game da tsarki dakuma wanka da alwalah , ba laifi tayi koฦ™ari ta wanan fanni.

Jira take sai kuma taga ya miฦ™e ya ษ—auko plet da wuฦ™a ya baje kazar gata ฦ™atuwa , wani yawu takuma haษ—iya , so takeyi taji yace ” mata sakko kuma badan yau sabuwar kunyarshi takeji ba da babu abinda zai hanata daka wawa, sai da ya tsiyaya mata milk a cup kana yace ” bismillah har sikel na harษ—eta ta sakko ta zauna ko irin yangar nan babu tafara bawa cikinta tanayi tana lumshe ido mamaki ta bashi, sai ya tuno darensu na farko shida Afnan lokacin da ya shigo ฦ™in buษ—e fuska tayi kuma da ฦ™yar taci kazar bawata mai yawa taci ba amma ita wanan ko na bakinta bata gama ci take ษ—aukar wani.

Tsayawa yayi kallon ikon Allah bata damu da rashin cinsa ba sai suษ—e hannu takeyi, da ya gaji da dane dannen wayarsa ya miฦ™e ya nufi ษ—akinsa , a gajiye yake hakan yasashi kwanciya ‘a madai daicin gadonsa bacci mai nauyi yayi awon gaba dashi .

Saida takusa cinye kazar sanan ta ajiye ragowa a kan table taje ta faษ—a gado tana tsalle ashe haka aure yake tabb shine naketa kuka , yasin danasan kullum haka za adingayi da ban tada hankali ba , naci ta yau saura ta gobe yasin su inna zasu ganni nayi mulmul , dahaka itama bacci ya sureta .

magunguna momy ta haษ—awa Afnan sbda momy mace ce mai son taga ta mallaki zuciyar miji bata hanyar boka ba , ta hanyar magunguna da turaruka ,da kissa hakan yasa dady yafi sonta itako anty bata ganewa maganin mata kasancewarta bata jituwa da magani shiyasa take masa kallon ko in kula , wasu zafafan turaruka momy ta haษ—awa Afnan a wata ฦดar leda kana ta ฦ™ara da ce mata kartayi wasa da shan magani dakuma kula da abubuwan da mijinta yakeda buฦ™ata , karkuma ta zamo mai ษ—aga murya akan ta mijinta ta zamo mai tausayi da iya kallo dakuma iya tafiya , ta ฦ™ara da cewa ” ta yawaita amfani da turaruka masu daษ—in ฦ™amshi karta dinga barin kanta yana daษ—ewa batare da ta wankesa da shampo ba .

godiya Afnan tayiwa momyn ta , momy ce tace ” bawai na gama bane , abu na gaba inaso kisan wani sirri shi namiji inda kika juyashi haka zai biki tausayi fara’a iya kallo iya tafiya dadaษ—an kalami uwa uba kuma ษ—aukar wanka da iya kissa ,karki zamo kina zama nesa dashi a yayin da kuke tare ki zamo masa tamkar yayayyar yarinya ina fatan duk waษ—annan abubuwan sun shiga kunnenki ,zuwa gaba zan baki wasu muhimman sirrukan , yanzu miฦ™omin wancan zumar , miฦ™ewa Afnan tayi ta kawowa momy zumar momy ce ta buษ—e tare da cewa ki kafa kanki ki shanye ki ษ—auko madara a store ki fasata itama ki shanye , akwai dabino a wanan kwanon ki ษ—ibo kici shima yana temako sosai basai na fayyace miki komai ba.

Ad

_____

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button