LAMARIN KADDARAR AURE NA COMPLETE NOVEL

LAMARIN KADDARAR AURE NA COMPLETE NOVEL

Yau ne Afnan ta gama idda ,Abdallah yayi maganar aure , dady ne yace “ka tambayi Afnan ɗin inhar ta ‘amince to babu matsala ,kwana biyu tsakani momy tasa aka shiga yiwa Afnan dilka saboda ta ƙara kyau inda zata gigita samari , yanzu idon Afnan yafi dz buɗewa nesa ba kusa ba , ƙarar wayarta ce tasata duba mai kiran , Abdallah ne ,dama yama sani anshafe labarin ɗaukar wayarshi intai ring sai ɗaya ,dole sai tayi sau biyu, aslm mijina katseta yayi da gani a palo dan Allah ki fito yanzu , gyalenta ta ɗaukz tare da ƙara feshe jikinta da humra , isa gurinshi tayi da sallama tace “ranka shida ɗe barka da isowa , ywa gimbiya komai naki birgeni yakeyi dariya tayi masa mai haɗe da fari da ido tace “kaima ai hakanne ,gyara zamanshi yayi yace “kinsan me ? a’a Afnan tace sai ka faɗa , inason a kawo sadaki ne kin amince manya su shiga tsakani ? murmishi tayi tace “haba honey nama ɗauka wata maganar ce nikam tun yaushe na amince karka damu , kai amma godiya nake sosai cewar Abdallah inason komai kar ya ɗauki lokaci nafison in ga amaryata a gidana , dariya Afnan tayi tace “ai ka sameni ma tun yaushe.”

Yau duk rabi hirar tasu ta lamari auran ne , Afnan ji takeyi kamar yanzu ne zatayi sabon aure , wani nishaɗi takeji , momy ma sai daɗa zugata takeyi, ana kuma gyarata tun ba’a kawo sadakin ba ma bare ayi maganar aure , yau kwanan Abdallah uku bai zo ba kasancewar ya gayawa Afnan cewar zaiyi tafiya , a yau iyayensa sukazo nema masa auran Afnan tare da dukiyar aure , dubu ɗari da hamsin suka zube gaban su dady , dan su biyu ne shida abokinsa , fatan alkairi sukayi kana sukayi musu sallama , Abdallah na Ibadan yaje gurin wani kaya nashi da aka kawo , sana’ar kayan sawa yakeyi kama daga takalma na mata harma na maza shaddoji da atamfofi da sarƙa da ɗan kunne duk dai , kuɗi a gurinshi ba’a magana , duk kuɗin dadyn Afnan to Abdallah yasha gabansa .”

BAYAN SATI UKU .

Yau kwanan sa ɗaya rabonsa da gidan dan yanzu sai yayi ra’ayi yake shigowa , Maimunatu na kwance zazzaɓi ya rufeta ta koma abin tausayi , jin alamun shigowar mutum yasata daddafa bango ta fito , ganin Haisam zaune da ƴar laptop ɗinsa a gabansa yana sarafata yasata zama gefen shi , ɗago kai yayi ya galla mata harara yace “wane irin iskanci ne zakizo ki zauna min dalla tashi jiki duk tsami , dariyar yaƙe tayi kana tace “ka temaka ka kaini asibiti , kallon kinma rainani yayi mata ya maida hankalinsa ga abinda ke gabansa , kuka tafara shaɓe shaɓe ta miƙe jiri na ɗibarta ta tsuguna a fabansa tace “dan darajar iyayenka dan Allah ka temakeni zan mutu , shi dariya ma tabashi , gani yakeyi kamar langwai take yimasa yace “inna fice naga wanda zaki laƙewa kauce dallah ,haka ya fice ya barta a gurin wani gagarumin amai ne ya taso mata ba shiri tadinga kwarara shi kamar zata amayar da hanjin cikinta , nunfashinta sama sama ta ɗauki ruwan dake kusa da ita a tebur ta sha ai kamar ta kuma kiran aman tacigaba , tashin zuciya ya takura mata wanan wace irin rayuwace ?” cewar Maimunatu jiri na ɗibarta ta ɗauko tsumman rigarta ta naɗe aman ta koma ɗaki bawai dan gurin ya gogu ba sbda wari ma gurin ya ɗauka amma haka ta koma ɗaki ,

TA ɗauki wayarta ta danna lambar mahaifiyarta , cikin sa’a ta ɗaga tare da cewa”Maimuna lafiyarki kuwa ?”naji muryarki wata iri kamar mara lafiya ,cikin ƙarfin hali Maimunatu tace “umma banida lafiya kamar zan mutu ga Haisam ɗin yaƙi kulani , to meye yake damunki cewar umma?”wlh amai ne da zazzaɓi gakuma tashin zuciya ,Alhmdulilah ƴar albarka kinyi ƙoƙari kin haifu Allah ya inganta shiɗin waye da zaiƙi kulaki lallai ma , bari yanzu zan fita gidan barka daganan zan wuce gurin wani malami da aka yimin kwatancensa jiya kwantar da hankalinki zakisha gata shiɗin banza ma , kashe wayar umma tayi zuciyarta fal farinciki yo aisu kakarsu ta yanke saƙa.”

Anty Aisha ce ta zauka a gidan misalin ƙarfe huɗu na yamma kai tsaye ɗakin yayan nata ta wuce, yana ganinta ya washe haƙora tare da cewa dama so nakeyi in kiraki a waya yanzu to sai gaki kin iso , sassuta murya Anty tayi kamar munafuka tace “ai gani dama zmfanin ɗan uwa kenan yanzu mai yafaru Alhaji ?”dady ne yace “akan maganar auran Afnan ne, riƙe baki anty tayi tace “yanzu gidan matsiyacin zaka maidata?”a haba ni na isa ai wani sabo Allah ya kawo mata shi wancan ai harya bata takardar ta tun yaushe hidindimun bikinne dai ankawo sadaki ankuma sa rana wata biyu me dame kike ganin ya kamata a siyo banason wancan kayan ɗakin nata so nakeyi a canza mata masu tsadar gaske , cikin fara’a anty tace “dama abinda zance kenan to suɗin wa za’a bawa naga basuyi komai ba , dady ne yace “wa nakeda shi bayan ke kece zaki kwashe ,ai da sauri anty ta sunkuyar da kai tana zubowa Alhaji godiya.”

Alhaji ne yace “ai ba komai yanzu nawa ne kike ganin zai isa kokuma tare zamuje kasuwar , ai kam dayafi Alhaji ita kuma uwar tata sai ka bata kuɗin siyan kayayyakin abinci kuttt hmmm…

Kumafa kin kawo shawara barinje banki in dawo zuwa gobe sai mu tafi , yana ficewa anty ta wuce saɗaf saɗaf ta fice dan batason su haɗa ido da kowa, tana fita bakin get tayi hamdala da tari abin hawa ta fice , kai tsaye dady ɗakin momy ya wuce , samunta yayi ita da Afnan suna duba wasu turaruka da aka kawo musu daga saudiya, zama dady yayi yace "biki nata ƙaratowa harkun fara shirye shirye ne ?momy ce ta kashewa dady ido ɗaya tace "turarukan Afnan ne ƙawata da zata dawo daga saudiya nabata sautu to shine ta kawomin , kuɗinsu dubu ɗari uku , ok babh matsala amma sai naje bank dan yanzu babu kuɗi a hanuna masu yawwa....✍️.

Follow me and vote on wattpad

????????????????????????????
???? ???? ????

LAMARIN K’ADDARAR AURE NA!!!

     ????     ????     ????

????????????????????????????

Story and writing by

ZAINAB HABIB
{Mom islam}

My wattpad momislam2020

My telegram link
https://t.me/joinchat/IaKr804dfndik1e2

Zainabhabibu713 gmail.com


AREWA WRITER’S ASSOCIATION


????{Arewa ginshiƙin al’ummah}????


https://www.facebook.com/104534761033461/postsarewawritersassociation@gmail.com
https://youtube.com/channel/UC2en2LRwD-FljFg2U2OYhDQ

Barka da zuwa tashar S ZARIA HAUSA TV ku danna mana Subscribe tare da kararrawar sanarwa domin samun sabbin shirye-shiryen mu mu gode.

BISMILLAHIR RAHMANI RAHIM

EPISODE 21 & 22

Tun safe Abdallah ya sanarwa Afnan yana hanya abinci iri iri momy ta sata yi masa farinciki kuwa kowa na gidan ya gane tana cikin nishaɗi.

Ƙarfe biyu na rana sai ga kiransa , ya sauka a airport tsabar farinciki Afnan tace “ko inzo ɗaukarka ne?” no my Afy cikin kasalakiyar murya yace “.

Oky to me kakeso inyima yaufa da kaina nashiga kitchen “wow”my Afy sabon sunan da ya laƙaba mata kenan inanan zuwa insha Allah nanda 5:pm ɓata rai tayi kamar yana ganinta tace ” yayi yawa namatsu in ganka ,ƴan kwana kinnan da kayi ji nakeyi kamar kayi shekara.”

Oh sorry my Afy zanzo amma surprise zanyi miki ,barin shiga mota oky Afnan tace ” sanin ba ita kaɗaice dashi ba ,dole sai yaje gurin matar sa ya huta ,wasu zafafan hawaye ne suka zubo mata a fili tace “LAMARIN ƘADDARAR AURENA… Allah sarki rayuwa ,

Kai tsaye wanka takuma shiga ta daɗe tana ƙalƙale jikinta daga bisani ta fito ɗaure da tawul a ƙirjinta dakuma kanta , wasu humra masu masifafen ƙamshi ta shafa ,kana ta kawo mai shima mai ƙamshi ta mulke ko ina na jikinta.

 Momy ce ta shigo ɗauke da murmishi a fuskarta tazo gaban Afnan dake kan kujerar dake gaban mirror daughter ki tsara kwaliyar da kyau fa oky mom zanyi nama gama ,

simple makeup tayi wanda ya kuma ƙawata kyakyawar fuskarta , kana ta ɗauko atamfa ɗinkin riga da skirt wanda ya matse ta sosai hakama rigar ta fito da kowace sura ta jikinta .

Ƙarfe biyar dai dai sai ga kiran Abdallah ya shigo , a yangace ta ɗaga tare da rage sautin muryarta , ganinan a parking spice ,oh baby yau kazamo baƙo kenan ?kashe murya yayi kamar mai shirin yin barci yace “.

Nafison ganin kwaliyar da aka yimin kafin in shigo in bada tukwaici , murmishi Afnan tayi ta janyo ƙaramin mayafinta tayo waje , taku takeyi kamar bazata taka ba ga wani fitina nnen ƙamshi dake tashi , 

Tun daga nesa ya hangota wani kasalalen murmishi yayi kana ya shafa sajen fuskarshi , gyara tsayuwarsa yakuma yi yana juyu da keys ɗin nake hanunsa.
tun daga nesa take sakar masa tsadajen murmishi , shima maida mata yakeyi cikin ƙwarewa ,da sako irin nasa, gimbiya Afy sarautar mata takawarki lafiya ,
Uhm to barka yarima zomushiga man ka huta , biyota yayi wanan karon ma itace a gaba shiko yana baya sai rawa yakeyi yana kallon kowane irin taku nata , da isarsu palo ya zube kan luntsumemiyar kujerar da ta ƙarawa ɗakin kyau drinks iri iri Afnan ta zuba masa da tsararen abinci mai rai da lafiya tuwon shinkafa yaji kifi da nama gakuma farfesu na kaza a gefe , kalar abincin da Abdallah yake so ne shiyasa ya zage yaci sosai .
Kallon gefensa da Afnan ke zaune yayi lumshe ido ya sake yi a karo na biyu tare da kamo hanunta yasanya cikin nasa , wani irin tafiyar tsutsa yake yimata da yai sanadiyar saukar mata da kasala , lumshe ido tayi kuma ta kasa hanashi yin hakan.
Afy ya faɗa cikin sasanyar murya,a kasalance ta amsa tare da kai kalonta gareshi .
Nayi missing ɗin kyakyawar fuskarki da komai ma , tunani Afnan ta fara gaskiya da Abdallah ba haka yake ba dan meyasa zai dinga yimata haka alhali iya sadaki kawai ya kawo ba’a ɗaura aure ba ?” tayi nisa cikin tunani ta tsinkayo muryarsa yana cewa “Afy tashi muje ki rakani gurin mota ,to kawai tace “tana miƙewa ta yafa gyaleta , shigo Abdallah bai matsa ba yananan a tsayen , to muje ,Afnan tace tana mai kallonsa , ƙin kulata yayi ya janye gyalen dake jikinta tare da ƙare mata kallo cikin zuciyarsa yana cewa”wanan yarinyar kamar aljana , ga tsayi ga ƙiba ga bobs ga hips komai normal ina na aureta na huta wlh,
Hura masa iska tayi a fuskarsa tare da cewa “baby kazo muje yamma tayi , bangaji da ganin matata ba ,cewar Abdalla h rasa ta cewa Afnan tayi ta zuba masa fararen idanuwanta , to zomuyi sallama ,cewar Abdallah hannayensa yasa duka biyu tare da …..

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19Next page

Leave a Reply

Back to top button