Our website is made possible by displaying online advertisements to our visitors. Please consider supporting us by whitelisting our website.
LAMARIN KADDARAR AURE NA COMPLETE NOVEL

LAMARIN KADDARAR AURE NA COMPLETE NOVEL

Ad

_____

Yau ne Afnan ta gama idda ,Abdallah yayi maganar aure , dady ne yace “ka tambayi Afnan ษ—in inhar ta ‘amince to babu matsala ,kwana biyu tsakani momy tasa aka shiga yiwa Afnan dilka saboda ta ฦ™ara kyau inda zata gigita samari , yanzu idon Afnan yafi dz buษ—ewa nesa ba kusa ba , ฦ™arar wayarta ce tasata duba mai kiran , Abdallah ne ,dama yama sani anshafe labarin ษ—aukar wayarshi intai ring sai ษ—aya ,dole sai tayi sau biyu, aslm mijina katseta yayi da gani a palo dan Allah ki fito yanzu , gyalenta ta ษ—aukz tare da ฦ™ara feshe jikinta da humra , isa gurinshi tayi da sallama tace “ranka shida ษ—e barka da isowa , ywa gimbiya komai naki birgeni yakeyi dariya tayi masa mai haษ—e da fari da ido tace “kaima ai hakanne ,gyara zamanshi yayi yace “kinsan me ? a’a Afnan tace sai ka faษ—a , inason a kawo sadaki ne kin amince manya su shiga tsakani ? murmishi tayi tace “haba honey nama ษ—auka wata maganar ce nikam tun yaushe na amince karka damu , kai amma godiya nake sosai cewar Abdallah inason komai kar ya ษ—auki lokaci nafison in ga amaryata a gidana , dariya Afnan tayi tace “ai ka sameni ma tun yaushe.”

Yau duk rabi hirar tasu ta lamari auran ne , Afnan ji takeyi kamar yanzu ne zatayi sabon aure , wani nishaษ—i takeji , momy ma sai daษ—a zugata takeyi, ana kuma gyarata tun ba’a kawo sadakin ba ma bare ayi maganar aure , yau kwanan Abdallah uku bai zo ba kasancewar ya gayawa Afnan cewar zaiyi tafiya , a yau iyayensa sukazo nema masa auran Afnan tare da dukiyar aure , dubu ษ—ari da hamsin suka zube gaban su dady , dan su biyu ne shida abokinsa , fatan alkairi sukayi kana sukayi musu sallama , Abdallah na Ibadan yaje gurin wani kaya nashi da aka kawo , sana’ar kayan sawa yakeyi kama daga takalma na mata harma na maza shaddoji da atamfofi da sarฦ™a da ษ—an kunne duk dai , kuษ—i a gurinshi ba’a magana , duk kuษ—in dadyn Afnan to Abdallah yasha gabansa .”

BAYAN SATI UKU .

Yau kwanan sa ษ—aya rabonsa da gidan dan yanzu sai yayi ra’ayi yake shigowa , Maimunatu na kwance zazzaษ“i ya rufeta ta koma abin tausayi , jin alamun shigowar mutum yasata daddafa bango ta fito , ganin Haisam zaune da ฦดar laptop ษ—insa a gabansa yana sarafata yasata zama gefen shi , ษ—ago kai yayi ya galla mata harara yace “wane irin iskanci ne zakizo ki zauna min dalla tashi jiki duk tsami , dariyar yaฦ™e tayi kana tace “ka temaka ka kaini asibiti , kallon kinma rainani yayi mata ya maida hankalinsa ga abinda ke gabansa , kuka tafara shaษ“e shaษ“e ta miฦ™e jiri na ษ—ibarta ta tsuguna a fabansa tace “dan darajar iyayenka dan Allah ka temakeni zan mutu , shi dariya ma tabashi , gani yakeyi kamar langwai take yimasa yace “inna fice naga wanda zaki laฦ™ewa kauce dallah ,haka ya fice ya barta a gurin wani gagarumin amai ne ya taso mata ba shiri tadinga kwarara shi kamar zata amayar da hanjin cikinta , nunfashinta sama sama ta ษ—auki ruwan dake kusa da ita a tebur ta sha ai kamar ta kuma kiran aman tacigaba , tashin zuciya ya takura mata wanan wace irin rayuwace ?” cewar Maimunatu jiri na ษ—ibarta ta ษ—auko tsumman rigarta ta naษ—e aman ta koma ษ—aki bawai dan gurin ya gogu ba sbda wari ma gurin ya ษ—auka amma haka ta koma ษ—aki ,

TA ษ—auki wayarta ta danna lambar mahaifiyarta , cikin sa’a ta ษ—aga tare da cewa”Maimuna lafiyarki kuwa ?”naji muryarki wata iri kamar mara lafiya ,cikin ฦ™arfin hali Maimunatu tace “umma banida lafiya kamar zan mutu ga Haisam ษ—in yaฦ™i kulani , to meye yake damunki cewar umma?”wlh amai ne da zazzaษ“i gakuma tashin zuciya ,Alhmdulilah ฦดar albarka kinyi ฦ™oฦ™ari kin haifu Allah ya inganta shiษ—in waye da zaiฦ™i kulaki lallai ma , bari yanzu zan fita gidan barka daganan zan wuce gurin wani malami da aka yimin kwatancensa jiya kwantar da hankalinki zakisha gata shiษ—in banza ma , kashe wayar umma tayi zuciyarta fal farinciki yo aisu kakarsu ta yanke saฦ™a.”

Anty Aisha ce ta zauka a gidan misalin ฦ™arfe huษ—u na yamma kai tsaye ษ—akin yayan nata ta wuce, yana ganinta ya washe haฦ™ora tare da cewa dama so nakeyi in kiraki a waya yanzu to sai gaki kin iso , sassuta murya Anty tayi kamar munafuka tace “ai gani dama zmfanin ษ—an uwa kenan yanzu mai yafaru Alhaji ?”dady ne yace “akan maganar auran Afnan ne, riฦ™e baki anty tayi tace “yanzu gidan matsiyacin zaka maidata?”a haba ni na isa ai wani sabo Allah ya kawo mata shi wancan ai harya bata takardar ta tun yaushe hidindimun bikinne dai ankawo sadaki ankuma sa rana wata biyu me dame kike ganin ya kamata a siyo banason wancan kayan ษ—akin nata so nakeyi a canza mata masu tsadar gaske , cikin fara’a anty tace “dama abinda zance kenan to suษ—in wa za’a bawa naga basuyi komai ba , dady ne yace “wa nakeda shi bayan ke kece zaki kwashe ,ai da sauri anty ta sunkuyar da kai tana zubowa Alhaji godiya.”

Alhaji ne yace “ai ba komai yanzu nawa ne kike ganin zai isa kokuma tare zamuje kasuwar , ai kam dayafi Alhaji ita kuma uwar tata sai ka bata kuษ—in siyan kayayyakin abinci kuttt hmmmโ€ฆ

Kumafa kin kawo shawara barinje banki in dawo zuwa gobe sai mu tafi , yana ficewa anty ta wuce saษ—af saษ—af ta fice dan batason su haษ—a ido da kowa, tana fita bakin get tayi hamdala da tari abin hawa ta fice , kai tsaye dady ษ—akin momy ya wuce , samunta yayi ita da Afnan suna duba wasu turaruka da aka kawo musu daga saudiya, zama dady yayi yace "biki nata ฦ™aratowa harkun fara shirye shirye ne ?momy ce ta kashewa dady ido ษ—aya tace "turarukan Afnan ne ฦ™awata da zata dawo daga saudiya nabata sautu to shine ta kawomin , kuษ—insu dubu ษ—ari uku , ok babh matsala amma sai naje bank dan yanzu babu kuษ—i a hanuna masu yawwa....โœ๏ธ.

Follow me and vote on wattpad

๐Ÿ’ฆ๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐Ÿ’ฆ
๐Ÿ’ ๐Ÿ’ ๐Ÿ’

LAMARIN K’ADDARAR AURE NA!!!

     ๐Ÿ’     ๐Ÿ’     ๐Ÿ’

๐Ÿ’ฆ๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐ŸŒน๐Ÿ’ฆ

Story and writing by

ZAINAB HABIB
{Mom islam}

My wattpad momislam2020

My telegram link
https://t.me/joinchat/IaKr804dfndik1e2

Zainabhabibu713 gmail.com


AREWA WRITER’S ASSOCIATION


๐Ÿ’ฆ{Arewa ginshiฦ™in al’ummah}๐Ÿ’ฆ


https://www.facebook.com/104534761033461/postsarewawritersassociation@gmail.com
https://youtube.com/channel/UC2en2LRwD-FljFg2U2OYhDQ

Barka da zuwa tashar S ZARIA HAUSA TV ku danna mana Subscribe tare da kararrawar sanarwa domin samun sabbin shirye-shiryen mu mu gode.

BISMILLAHIR RAHMANI RAHIM

EPISODE 21 & 22

Tun safe Abdallah ya sanarwa Afnan yana hanya abinci iri iri momy ta sata yi masa farinciki kuwa kowa na gidan ya gane tana cikin nishaษ—i.

ฦ˜arfe biyu na rana sai ga kiransa , ya sauka a airport tsabar farinciki Afnan tace “ko inzo ษ—aukarka ne?” no my Afy cikin kasalakiyar murya yace “.

Oky to me kakeso inyima yaufa da kaina nashiga kitchen “wow”my Afy sabon sunan da ya laฦ™aba mata kenan inanan zuwa insha Allah nanda 5:pm ษ“ata rai tayi kamar yana ganinta tace ” yayi yawa namatsu in ganka ,ฦดan kwana kinnan da kayi ji nakeyi kamar kayi shekara.”

Oh sorry my Afy zanzo amma surprise zanyi miki ,barin shiga mota oky Afnan tace ” sanin ba ita kaษ—aice dashi ba ,dole sai yaje gurin matar sa ya huta ,wasu zafafan hawaye ne suka zubo mata a fili tace “LAMARIN ฦ˜ADDARAR AURENAโ€ฆ Allah sarki rayuwa ,

Kai tsaye wanka takuma shiga ta daษ—e tana ฦ™alฦ™ale jikinta daga bisani ta fito ษ—aure da tawul a ฦ™irjinta dakuma kanta , wasu humra masu masifafen ฦ™amshi ta shafa ,kana ta kawo mai shima mai ฦ™amshi ta mulke ko ina na jikinta.

 Momy ce ta shigo ษ—auke da murmishi a fuskarta tazo gaban Afnan dake kan kujerar dake gaban mirror daughter ki tsara kwaliyar da kyau fa oky mom zanyi nama gama ,

simple makeup tayi wanda ya kuma ฦ™awata kyakyawar fuskarta , kana ta ษ—auko atamfa ษ—inkin riga da skirt wanda ya matse ta sosai hakama rigar ta fito da kowace sura ta jikinta .

ฦ˜arfe biyar dai dai sai ga kiran Abdallah ya shigo , a yangace ta ษ—aga tare da rage sautin muryarta , ganinan a parking spice ,oh baby yau kazamo baฦ™o kenan ?kashe murya yayi kamar mai shirin yin barci yace “.

Nafison ganin kwaliyar da aka yimin kafin in shigo in bada tukwaici , murmishi Afnan tayi ta janyo ฦ™aramin mayafinta tayo waje , taku takeyi kamar bazata taka ba ga wani fitina nnen ฦ™amshi dake tashi , 

Tun daga nesa ya hangota wani kasalalen murmishi yayi kana ya shafa sajen fuskarshi , gyara tsayuwarsa yakuma yi yana juyu da keys ษ—in nake hanunsa.
tun daga nesa take sakar masa tsadajen murmishi , shima maida mata yakeyi cikin ฦ™warewa ,da sako irin nasa, gimbiya Afy sarautar mata takawarki lafiya ,
Uhm to barka yarima zomushiga man ka huta , biyota yayi wanan karon ma itace a gaba shiko yana baya sai rawa yakeyi yana kallon kowane irin taku nata , da isarsu palo ya zube kan luntsumemiyar kujerar da ta ฦ™arawa ษ—akin kyau drinks iri iri Afnan ta zuba masa da tsararen abinci mai rai da lafiya tuwon shinkafa yaji kifi da nama gakuma farfesu na kaza a gefe , kalar abincin da Abdallah yake so ne shiyasa ya zage yaci sosai .
Kallon gefensa da Afnan ke zaune yayi lumshe ido ya sake yi a karo na biyu tare da kamo hanunta yasanya cikin nasa , wani irin tafiyar tsutsa yake yimata da yai sanadiyar saukar mata da kasala , lumshe ido tayi kuma ta kasa hanashi yin hakan.
Afy ya faษ—a cikin sasanyar murya,a kasalance ta amsa tare da kai kalonta gareshi .
Nayi missing ษ—in kyakyawar fuskarki da komai ma , tunani Afnan ta fara gaskiya da Abdallah ba haka yake ba dan meyasa zai dinga yimata haka alhali iya sadaki kawai ya kawo ba’a ษ—aura aure ba ?” tayi nisa cikin tunani ta tsinkayo muryarsa yana cewa “Afy tashi muje ki rakani gurin mota ,to kawai tace “tana miฦ™ewa ta yafa gyaleta , shigo Abdallah bai matsa ba yananan a tsayen , to muje ,Afnan tace tana mai kallonsa , ฦ™in kulata yayi ya janye gyalen dake jikinta tare da ฦ™are mata kallo cikin zuciyarsa yana cewa”wanan yarinyar kamar aljana , ga tsayi ga ฦ™iba ga bobs ga hips komai normal ina na aureta na huta wlh,
Hura masa iska tayi a fuskarsa tare da cewa “baby kazo muje yamma tayi , bangaji da ganin matata ba ,cewar Abdalla h rasa ta cewa Afnan tayi ta zuba masa fararen idanuwanta , to zomuyi sallama ,cewar Abdallah hannayensa yasa duka biyu tare da โ€ฆ..

Ad

_____

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19Next page

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button