LAMARIN KADDARAR AURE NA COMPLETE NOVEL
Cikin fara’a mama tace ”to d’an albarka baka d’auki number ,Maimunatun ba , sbda gudun fad’an mama yasashi , kar6ar wayar ,ya d’auki number ya fice , 6angaren maimunatu kuwa murna cike da zuciyarta ta buga tsalle kana tace ”wanan gayen da alamu kyakyawa ne , zanso ganinsa , tayiwa wayar kiss ,sai k’arfe 11pm Haisam ya koma gida ,Afnan mai saurin kuka , taci kukanta ta gaji hartayi bacci , yana shigowa tare da mashin d’ainsa ya kulle gidan , ya jingine mashin d’in ,k’arasawa yayi ,bedroom d’in Afnan , samunta yayi tayi bacci ,haska fuskarta yai da fitilar wayarsa kasan cewar babu wutar nepa , ganin hawaye bushe a fuskarta , yasashi cewa Allah sarki baiwar Allah , ya koma d’akinsa yai alwalah ya kwanta, tunnin yarinyar ne keyi masa yawo a brain d’insa , tabbas yasan inhar Afnan tasan labarin nan to kashinsa ya bushe , dan wlh zata iya barinsa , yasan Afnan ba ajinsa bace , mahaifinta nada dukiya taban mamaki amma ta za6e shi, to wai shin ita haihuwar nan ba ta Allah bace ?” ganin yana shirin yin sa6o ne ya sashi yin shiru , yayi adu’a bacci mai nauyi ya kwashesa , washe gari antashi da sanyi sosai ,bayan sunyi sallahr asbha Afnan ta koma d’akin Haisam baccin safe , bacci mai nauyi yai awon gaba dasu ba su suka farka ba sai misalin k’arfe goma Na safe , Afnan ce ta fara bud’e ido ta zare jikinta a na Haisam , gyara gidan tayi ta koma d’ora abin karyawa , tana gamawa ta shige wanka , jera kayan shayin tayi a kan tebur , kana ta nufi d’akin Haisam , tana shirin tashin sa raji ya fara salati , kwantowa tayi kan cinyarsa tace ”barka da safiya , ruwan wanka ya kammala , okay to tayani cire kayan.”
Tayashi tayi suka shige toilet yai wanka , yana fitowa ta taimaka masa ya shafa mai ,ta ciro masa kaya ya sanya shadda ce green taji aiki ,inka ganshi kamar sabon ango sai wani shek’i yake zubawa , bayan sungama breakfast ,ya dubeta cikin tausayawa zai yimata magana ya fasa , Afnan ta lura da yanayin sa , tace ”akwai magana a bakinka ko ?”gayamin mai ya faru? Haisam ne ya marai raice ,fuskar kamar mai shirin kuka yace ” lovely mama ce …mama tace me ?”inajinka , shiru Haisam yayi kana yace ”aure takeson in k’ara , a razane Afnan ta mik’e lokaci d’aya hawaye suka cika mata ido ,ta dubi Haisam da kansa yake k’asa , yak’i had’a ido da ita , hmm kawai Afnan tace ”ta shige bedroom , ta janyo akwatinta , wanda ta d’ibi kayanta na kwanaki da tayi yaji, shirin sa hijab takeyi Haisam ya sha gabanta , yace ”dan Allah ki saurare ni kiyi hak’uri , a fad’ace ta dubeshi tace ”a halin yanzu bana k’aunar jin sautin muryar ka kabani guri intafi gidan iyayena , ada bana tunanin tafiya gidan mu yau kam wlh bazan kwana anan gidan ba , kuka takeyi mai ban tausayi , ta juyo da jajayen idanunta tace ”ada in ana yimin gori nakanji haushi , wai yau bakinka ne ke gayamin maganar aure,? kai da kanka kamar a mafarki.”
Haisam yayi magiyar duniya Afnan tak’i yarda ta zauna , komawa bakin k’ofa yayi da gudu ya tare yana kallonta , amma nace dai karki fita ko?”idanunta da suka rufe tace ”koma me zakace kace dan wlh nikam nagaji da gorin da ake yimin , ta k’arashe maganar da share hawayen da suka kwaranyo mata , kasancewar ta doguwa kuma mai k’arfin jiki , ta shammaci Haisam ta turashi gefe , taja akwatinta ta fice , tsabar 6acin rai hartazo bakin titi bata lura ba , sbda tsakaninsu da d’an tafiya ,mai mashin ta tare tace ”ya kaita unguwar su , d’ora akwatin tayi itama ta hau suka d’auki hanya , suna isa gidan ta bud’e jakar hanunta ta mik’a masa kud’insa , kasa shiga gidan tayi dan rabonta da gidanan zatakai wata shida , tunda ta ta6a kawo k’ara mutanen gidan suka koreta kamar ba gidan su ba , cikin sanyin jiki taja akwatinta , ta bud’e get d’in ta shige , jikinta ne yakuma sanyi sbda tana tunanin abinda zata je ta tarar, bud’e k’ofar da zata sadata da d’akin mahaifiyar tata tayi , ganin babu ,yasata samun guri ta zauna ,jin alamun shigowar mutum yasata dai daita nutsuwar ta , mezan gani? nace mezan gani? uban me kikazo yimin da akwati?” cikin kuka Afnan ta gangaro daga kan kujerar da take zaune tace “mama ki yafemin dan Allah ,Haisam ne zai ƙara aure…aure?!!cewar momy ,da kyau kinga irin abinda muke jiye miki ko? dady ne ya shigo yana cewa”menakeji kamar hayaniya , hango Afnan yayi durƙushe a ƙasa yace “mekikazo yi ?bakin canza iyaye bane ? dady wlh ba haka bane kuyi hak’uri , momy ce tace ”wai aure mijin zai k’ara shine tazo , dady ne yace ” to ta tattara ta koma ai mijin ta za6a akan mu to taje ta rik’e mijin , suna tsaye a kanta suna zazzaga mata masifa .”
Dama tasan za’ayi haka , amma zata jure koma menene da zai faru , ficewa dady yayi ba tare da yace ”komai ba , momy ce ta zauna a gefen kujera tace ”in har kinason farinciki na to wlh sai dai kibar auran wanan munafikin dan bamu gaji tsiya ba , har meyaci dazai wulak’antaki , cikin sha shek’ar kuka tace ”momy bazan iya rayuwa babu Haisam ba , mari momy ta wanka mata tace ”uwar wa kike gayawa haka , to keda Haisam kunyi hanun riga ,inhar inada rai da lafiya to babu ke babu d’an talakawa ,momy ta k’arashe maganar ,tana nunata da yatsa , kuka Afnan ta saki tare da kwantar da kanta a kujerar dake gefenta , mom na fita direct d’akin Anty tayi anty na ninke kaya ta zauna gefen gadonta , cikin 6acin rai tace ”yarinyar ki ta dawo wai mijin zai k’ara aure , ehee aure kuma? cewar anty me ya tara dahar yake tunanin k’aro aure? ” mu dama ba son auranan mukeyi ba ,kawai ta zauna Allah ya fito mata da wani dan wlh wanan yaron ba kalar Afnan bane, momy ce tace ”ganemin dai ,ana haka suka jiyo sallamar Anty ummi ta shigo , nanfa hira ta kaure , suka fara bata labarin Afnan ta dawo gida , cikin rashin jin dad’in maganar tasu tace ”wai maiyasa kuke haka ne ? bakwa tunanin mai kud’i da talaka duka Allah ne ya yisu ? kuma akwai lokacin da Allah zai azurta talakan , momy ce ta dubi Anty ummi tace ”duk da haka dai , girgiza kai Anty ummi tayi dan tasan basajin kira sunyi nisa , anty dake gefe tana yiwa Anty ummi kallon wulak’anci ta juya kai gefe..✍️.
Nayi tafiya ne bazaku dinga samun update kullum ba so yanzu dai sharhi da comments nake so .????
Vote and follow me on wattpad????.
????????????????????????????
???? ???? ????
LAMARIN K’ADDARAR AURE NA!!!
???? ???? ????
????????????????????????????
Story and writing by
ZAINAB HABIB
{Mom islam}
My wattpad momislam2020
Zainabhabibu713 gmail.com
My telegram link
https://t.me/joinchat/IaKr804dfndik1e2
????{AREWA WRITER’S ASSOCIATION}????
BISMILLAHIR RAHMANI RAHIM
EPISODE 9 & 10
Washe gari , mama tayi sammako da sassafe lokacin k’arfe bakwai 7am bubuga k’ofar gidan su Haisam tafara cikin gaggawa , Haisam daya farka daga baccin asbha ya mik’e yana mik’a ya isa bakin k’ofar ya bud’e , ganin mama yasashi d’an durk’usawa yace ”barka mama sannu da zuwa ,yawwa kawai tace ”ta ra6a ta gefensa ta wuce ,ganin gidan ba inda tasaba gani ba ,yasata cewa “ina matar gidan?” sosa kansa yayi kana yace ”ta tafi anguwa , bud’ar bakin mama tace ”Allah yasa intaje karta dawo , shidai Haisam burinsa yaga fitar mama lafiya , ganin ba shirin fita takeyi ba yasashi ,jingina da bango , mama ce ta dubeshi tace ”insha Allah nanda sati biyar ka zamo ango da yardar Allah zaku shekare da jariri , Allah yasa kawai Haisam yace ”dan bashida amsar da zai bata , juyawa tayi zata fice ta juyo tace ”to yakamata kaje gurin yarinyar ku fahimci juna ko ?”to Haisam yace ”da alamun k’aguwa a fuskarsa , mancewa tayi da sallamar ma ta fice , Alhmdulh Haisam yace ”ya koma d’aki yana cewa “dame zanji ga Afnan bata gida ga mama tazo min da wani batu , gaskiya bansan ina zan sa rayuwata ba.”