LAMARIN KADDARAR AURE NA COMPLETE NOVEL

LAMARIN K’ADDARAR AURE NA!!
???? ???? ????
????????????????????????????
Story and writing by
ZAINAB HABIB
{Mom islam}
*Rashin sharhi zaisa ya komai na kud’i????.
AREWA WRITER’S ASSOCIATION
????{Arewa ginshiƙin al’ummah}????
Barka da zuwa tashar S ZARIA HAUSA TV ku danna mana Subscribe tare da kararrawar sanarwa domin samun sabbin shirye-shiryen mu mu gode.
BISMILLAHIR RAHMANI RAHIM
????️EPISODE 5 & 6
Sunkuyar da kai k’asa Haisam yayi yace ”ki k’ara hak’uri mama ,insha Allah Afnan zata haihu , banzan kallo ta watsa masa ,kana tace ”ubanwa kafi sanin tin tini ?”aure babu fashi na rantse da Allah kamar kayishi , cikin sanyin jiki Haisam ya mik’e tare da gyra hular kansa yace ”mama nabarki lafiya , ko kalonsa batayi ba , ya fice ,mashin d’insa ya hau kana ya nufi gidansa , samun k’ofar gidan a bud’e yasashi sanin , Afnan bata fito ba , to har yanzu 6acin ran ne , ya tambayi kansa , kulle k’ofar yayi yasa sak’ata kana ya nufi cikin gidan , yana shiga direct ya wuce parlorn da zai sadashi da ita , yana shiga parlorn ya ganta ,a kwance a kan 3 sitter idanunta , na kallon sama , d’ago mata kai yayi yace ”my sweetheart , inata sallama amma baki kulani ba ?”maida kalonta tai zuwa gareshi , da fararen idanunta masu rikitashi , batace komai ba , Haisam , daya shiga damuwa ganin 6acin rai k’arara a fuskar ,Afnan ya kuma janyota jikinta ya zauna a gefen ta ya d’orata a kan cinyarsa yace ”dan Allah kiyi hak’uri , tabbas abinda mama tafad’a bai dace , ba kinsan kuma mahaifiya dole nayi mata biyayya , Afnan ce ta shafo gefen kumatun Haisam ,tace ” abin alfahari na karka damu , nice nace ina sonka kuma har gobe bazan dena sonka ba , cikin farinciki ya had’e hannayensa biyu alamar godiya , ya rik’o hanunta ya mik’ar da ita , kana yace ”zo mushiga kitchen inkuma bazaki iya ba , ni barinje ko ruwan zafi in dafa miki.”
Hanunta ta rataya a kafa d’arshi suka nufi kitchen , indomie suka dafa da suka soya k’wai , kana suka juye a plet suka nufi parlor , zama tayi a kan kafet d’in da ya mamaye tsakiyar d’akin ,shima ya zauna kusa da ita , sai da suka gama ciyar da junansu , hira sukeyi ,cikin nishad’i kamar ba ita ta gama kuka ba , saboda faranta mata yasashi k’in fita aiki sunata gwada wa junansu soyayya , sauya salonsa yayi zuwa had’e bakinsu guri d’aya ganin hakan yasa nabasu guri , a duk lokacin da Haisam ya sami nutsuwa da Afnan , yana sanya mata albarka fiyeda tunani dan jinta yakeyi kamar sabuwar amarya , wanka sukayi a tare suna fitowa suka shafa mai mai k’amshi , Afnan ta sauya kaya zuwa doguwar riga milk color mai adon flawoyi , Haisam da yayi shigar k’ananun kaya shima yai kyau sosai , turare Afnan ta d’auko a gaban dress mirror ta fesa masa turare ,tace ”gaskiya my man kayi kyau sosai ,karfa y’an mata su kallemin kai , dariya Haisam yayi tare da rungumo Afnan yace ” tabb babu mai kallo na kedai ki kularmin da kanki , kiss ya manna mata a goshi tayi masa Allah ya tsare , yana fita ta sakawa k’ofar sak’ata ,ta koma bedroom d’inta tafara gyara gado , ta goge ledar d’akin tare da goge gadonta , kasancewar ta mace mara son k’azanta , komawa parlor tayi tafara sharewa ta goge ta goge TV , ta koma tsakar gida ta share takuma wankeshi fess , ta sa turaren wuta mai k’amshi , cikin k’an k’anin lokaci gidan yad’au k’amshi , tana shirin wanke _wanke , taji k’arar buga k’ofa , k’in tashi tayi dan tasan bazai wuce mama ba , kuma yau batada niyar k’unsar bak’in ciki , dan haka tacigaba da aikinta , cikin d’agun murya akace , Fatima ce fa ,da gudu Afnan taje ta bud’ewa Fatima k’ofa tareda k’yal k’yalewa da dariya suka shige parlor , zama sukayi ,Fatima tace ”matsoraciya ,kindawo ko magana babu ?”Afnan ce tace ”ke my man ne yabani tausayi , kuma nayi kewarshi so kinga dole in damu , cikin mamaki na soyayyar su Afnan Fatima tasa dariya kana tace ”masoyan asali , nima da Umar zai yarda da mundinga soyewa , suka kwashe da dariya , Afnan ce tace ”ban gane ba kina nufin ko irin shagwa6ar nan bakya yimasa ?”.
Fatima ce tace ”mutum sai kiga ya shigo gida babu fara’a ,to yazan yi masa?, gyara zama Afnan tayi kana tace” to yanzu dai ya kamata kisani ,kwaliya da tsafta itace ginshik’in komai , musamman in kika had’a da k’amshi , kuma sai abin yafi bada kala, agogo Afnan ta duba k’arfe hud’u na yamma , hakan yayi dai dai da shigowar ,wata budurwa mai jiki bak’a , kai tsaye ,d’akin dasu Afnan suke ta zarce, samunsu tayi itada Fatima suna hira,wani irin kallo tayi musu , budurwar tace ”wacece Afnan?” Afnan da gabanta yake fad’uwa ta kalli Fatima , Fatima ma ta kalle ta , tace ”to malama babu sallama babu gaisuwa ,sai nema?”girgiza budurwar tayi tace ”to ai ba ita ta kawoni ba dan haka matar gidan nakeson gani, Fatima da Afnan suka mik’e ,Afnan tace ”nice mai gidan ,mai kikeso ?”budurwar ce tace ”tunda naga mai gidan ai magana ,ta k’are , ta juya ta fice, mamaki ne ya kama su Fatima suna bak’in cikin dalilin da yasa basu nakad’a mata duka ba , amma babu komai ,Afnan tace ”idanunta cike da hawaye , Fatima da tsoron kar a yimusu duka yasata ,raku6ewa gefe , tana shan majina kamar wacce taci abinci mai yaji ,tace ”Afnan sai hak’uri.”
Haushi Fatima taba Afnan, wani mugun kallo tayi mata kana tace ”dama kamaki tayi ta sambad’eki , kekam anyi ma tsoraciya , tsoro yayi miki yawa , neman Fatima tayi ta rasa , komawa parlor tayi ta zauna a gefen hanun kujera , ta fara tunanin wanan budur war , to daga ina take ?” mik’ewa tayi dan tasan inta tsaya tunani ,har Haisam ya dawo batayi komai ba ,tsin tsiya ta d’auka ta kuma sharo ko ina na d’akin , dukda dai ba datti yayi ba , tasa turaren wuta , takuma fesa room freshner ad’akin , komawa toilet tayi ta wanke nata ,kana ta wanke na d’akin ,Haisam tana gamawa ta shige wanka, lokacin k’arfe 7pm tayi alwalah ,ta fito ,tanayin sallah ta zauna tsara kwaliya , dama tayi girkinta , mayukanta masu k’amshi ta shafa ,kana ta shafa powder ,tasa janbaki da gazal ta sanya kwali , tayi kyau sosai, mini skirt d’inta da ya tsaya mata iya gwuiwa tasa ,mai kalar pink sai farar riga , fara mai yan kaken hannu iya cibiya , ta kama kanta da yake a tsefe da abin kama gashi ,ta sanya pink d’in hula ,a gaban hular an rubuta my baby .”
K’ara feshe jikinta tayi da had’a d’un humra masu tada hankali ,ta zauna jiran , kiran sallahr isha’i , bayan wasu mintuna ,tajiyo kiran sallah ,hakan yasa ta mik’ewa , ta fara gabatar da sallaha , tana idarwa ta fara salatin annabi tare da kwararo adu’oi na bud’i dakuma k’arin soyayya a gurin mijinta , bayan ta kammalah ,ta nad’e abin sallar, ta d’auko wayarta dake jone a charge ,ta fara duba number Haisam ,cikin sa’a ta shiga , yana d’auka kafin tayi magana carab ,yace ”gimbiya yakk ya gida ?dafatan dai babu wata matsala ko ?”rage sautin muryarta ,tayi kana tace ”uhm ni ka barni sai kewar kallon fuskarka nakeyi ,yasan dole sai an lalla6a ta ,dan haka yace ”to ayimin hak’uri gani nan insha Allah yanzu .”
Dariya tayi ,tace ”fatan alkairi mijina Allah ya dawo min dakai lafiya , amen yace ”ki kulamin da kanki, I love you , kashe ido d’aya tayi kamar yana ganin ta tace ”love yau 2, kallo ta kuna ,a tashar MBC 2 wani film da suka sa ne a ja hankalinta , har k’arfe ,tara a rabi, jin k’arar mashin d’in Haisam ya sata mik’ewa, ta 6oye a jikin labule , sallama yakeyi shiru , baiji anyi magana ba ,my baby ina kika shigane ?”da gudu ta rungume shi tana ,oyoyo mijina , d’a gata sama yayi ya mai data bayan sa ,yana juyi da ita kamar yarinya, rad’a masa tayi a kunne “zomuje muyi wanka, shima cikin rad’a yace ”ba yanzu ba , sauka tayi a bayan nasa, taje bayi ta d’auko bucket ,ta zuba masa ruwan tare da sirkawa, tana shiga ta ganshi zaune da alamun damuwa , zama tayi kusa dashi tace ”mijina lafiya kuwa naganka haka?” babu komai yace ”ya kalle ta ,komai nata birgeshi yakeyi ,amma mama zatace ya k’aro aure ,gaskiya shikam ba ‘ayi masa adalci ba ,Afnan ta lura akwai abinda ke damun mijinta dan haka ,ta mik’ar dashi ,tare da cire masa ma6allin rigarsa , jikinshi yayi sanyi matuk’a ,tunda ya tuno da hukuncin da mama ta keson yankewa.”