LAMARIN KADDARAR AURE NA COMPLETE NOVEL

LAMARIN KADDARAR AURE NA COMPLETE NOVEL

Haka dai jikin nasa babu k’wari ta temaka masa yayi wanka, yana fitowa ta fito masa da kayansa , ya Sanya , marasa nauyi , zubo masa macaroni tayi a plet , wace taji kayan k’amshi da albasa, sanin baya cikin han kalinshi ya sata d’aukan cokali tafara bashi a baki , ci yakeyi kamar mara lafiya , hakan sam bai yiwa , Afnan dad’i ba, cikin zuciyar ta tace ”zan bishi a hankali insha Allah zai fad’amin koma menene ,ganin har yanzu yak’i sakin jikinsa yasata ,fashewa da kuka , kasancewar ta mai saurin kuka , kallonta yayi cikin tashin hankali ,yace ”mai kuma ya faru”mik’ewa tayi ta shige bedroom ,ko kulasa batayi ba , damuyoyi biyu kenan , Haisam ya ce lokacin da ya mik’e zuwa bawa Afnan hak’uri , ranta ya 6aci matuk’a saboda a rayuwarta bata son tayiwa mutum magana ya shareta , shikam Haisam oga ne ,bakin gado ya zauna tare da janyota jikinsa yana shafa gashin kanta , k’arfin hali kawai, ya keyi, amma ba dan zuciyarsa na yimasa dad’i ba, shuru tayi kamar ba ita keyin kukan ba , ta d’ago ido tana kallon sa ,murmishin dole ya k’ir k’iro , hakan yasa ta maida masa da murmishin , haka dai ya samu ya lalla6a ta har bacci mai nauyi yayi nasarar d’aukarta, gyara mata kwanciya yayi tare da lulu6eta kasancewar ,garin ana sanyi , ya mik’e a hankali ya ,koma bedroom d’insa , zagaye d’akin ya shiga yi yana mai k’ara tuno kudirin maman nashi , tausayawa Afnan yakeyi ,ya koma ya kwanta ,bacci 6arawo ya kwashe shi ,k’arfe kiran sallahr farko a kunnen sa , hakan yasa shi yin adu’ar tashi daga bacci ya shiga toilet ya d’auro alwalah , sai da yayi nafil fili sanan ya ,tafi d’akin Afnan , ya kwanta gefenta yana shafa fuskarta ,tare da hura mata iska ,bud’e ido tayi ta sakar masa murmishi ,shima hakan yayi mata ,yace ”lokaci yayi nisa kitashi kiyi sallah.”

To tace ”masa ganin zai tafi ne tace ”Allah ya dawo min dakai lafiya mijina , amen ya Allah my honey, cewar Haisam lokacin da yake shirin sa takalmi,kasancewar yana dad’ewa a masallaci , yasata kunna risho ta d’ora ruwan zafi ta dawo tayi alwala ,tayi sallah tana idarwa ,bayan tayi adu’oin ta , da ta saba , ta mik’e ta fara da gyra gado ta tsaftace ko ina tasa turaren wuta mai k’amshi , juye ruwan wankan tayi , ta shige toilet tayi wanka, tana fitowa ta koma kitchen ,ta juye wanda ta mayar , jin shigowar Haisam , tayi yana shigowa parlor ta durk’usa tace ”barka da safiya my man , da fara’arsa yace ”gimbiya ta kintashi lpy , lafiya Lou tace ”ruwan wanka ya kammalu yana toilet , okay Haisam yace ”please zamuje ki tayani cire kaya, mik’ewa sukayi rik’e da hanun juna , suna gama cire kayan, ya shiga wanka ita kuma ta fara kwaliya bayan ta d’ora shayi a kitchen, riga da zani ta sa na atamfa mai ratsin green da fari sai d’ingon bak’i a gefe , tayi kyau sosai ,d’akinsa ya wuce sai da ya gama shiryawa , sanan ya fito sanye da k’ananun kaya , sun amshi jikinsa kasan cewa shi fari dogo kya kyawa ,wow mijina wanan kyau haka?” dariya yayi yace ”kai matar Haisam wanan kashe kala haka , kamar zamuje , rufe masa baki tayi tace ”na gama tea madara da sauran su zan sa ,so me za’a dafa indomie ko doya da k’wai , kawai kiyi indomie and egg zai fi sauri , ficewa Afnan tayi ta fara hidimar girki , misalin k’arfe 9am ta kammala komai ta jerasu a tebur da cokula da cup , suna karyawa suna hira , Haisam ne ya mik’e tare da cewa ni zan tafi , ki kularmin da kanki , Allah ya tsare Allah ya bada sa’a , amen Haisam yace bayan ya bata kud’in cefane ya fice , kwashe kwanukan da suka gama breakfast tayi ,kana ta wanke su ta dawo ,ta kunna kallo ,misalin k’arfe uku na rana , taji alamar bugun k’ofa , mik’e wa tayi ,dan bacci ma takeyi sbda tana fashin sallah , k’arasawa tayi , bakin k’ofar , ganin k’anwarta Salma yasata fad’ad’a fara’ar ta .”

“Tace my sis barka da zuwa , d’aukan yaron tayi mai suna Sudais suka k’arasa parlor, suna zama Salma ta ,yamutsa fuska, kana tace ”yanzu sis wanan rayuwar da kika za6awa kanki yayi kenan, kin zauna gidan talaka yana baki wuya , jibi inda kika rame , murmishi Afnan tayi , lokacin da ta mik’e ,zatayi kitchen batace komai ba, ruwa ta d’ibo wa Salma a jug kana ta had’o mata da abinci da tagama yanzu , taliya ce ,mai da yaji , kuma ke6e baki tayi tace ”ta6 Allah ya kyauta sis yanzu abinda kikeci kenan?” juyowa Afnan tayi tace ”mai yasa kika biyoni ,kitchen ?”kinzo ki kuma 6atamin rai ko just ki forgetting komai ,but ya wuce ,komai Allah ne mai yi kuma komai kikaga bawansa dashi , bawai baya sonsa bane .✍️.

Kuyi hakuri nayi tafiya ne wlh ba lallai gobe kusami update ba , ku fahimceni biki mukeyi, masu sharhi naga sharhinku Allah nagode????.

????????????????????????????
???? ???? ????

LAMARIN K’ADDARAR AURE NA!!!

     ????     ????     ????

????????????????????????????

Story and writing by

ZAINAB HABIB
{Mom islam}

zai koma na kud’i tunda kuna karantawa amma bakwa sharhi

karku manta wlh zan dena post a Watsapp zan koma wattpad yafimin ????????


AREWA WRITER’S ASSOCIATION


????{Arewa ginshiƙin al’ummah}????


https://www.facebook.com/104534761033461/postsarewawritersassociation@gmail.com
https://youtube.com/channel/UC2en2LRwD-FljFg2U2OYhDQ

Barka da zuwa tashar S ZARIA HAUSA TV ku danna mana Subscribe tare da kararrawar sanarwa domin samun sabbin shirye-shiryen mu mu gode.

BISMILLAHIR RAHMANI RAHIM

????️EPISODE 7 & 8

Fad’in haka yasa Salma shiru da bakinta , tana gama shan ruwan ta mik’e tace ”sis mukam zamu wuce ,ga wanan kya rage wani abu, no bana so , Afnan tace ”lokacin da ta kamo hanun Sudais tana shirin yin hnyar waje , tsaki Salma taja kana tace ”wlh tunda kikace auran talaka ,hmm ina tausaya miki ko dady , yanzu baya ambaton sunanki , Afnan ce tayi dariyar yak’e wace tafi kuka ciwo ,tace ”ina da Allah tunda kowa na gudu na please in wucewa zakiyi ki fice, karki k’aramin ciwon kai , okay don’t worry , nice ma nazo inda kike ,tunda ke ba neman mu kikeyi ba ,wani wawan mari ,Afnan ta wanka wa Salma , Kana tace ”ficemin a gida ,bana neman temakon ku bance kowa ya temaka min ba , rik’e da kumatu , Salma ta fizge hanun Sudais a na Afnan suka wuce a zuciye , komawa kan kujera Afnan tayi ,rik’e da kanta , cikin damuwa da 6acin rai ta sa kuka mai tsuma zuciya , innalilahi wa inna’ilaihir raji’un ta ambata cikin muryar kuka , ya Allah kayimin magananin matsala ta , tun farkon aure na banida kwanciyar hankali , oh Allah ka duba lamurana, ta kwanta tana kuka ,Fatima ce ta shigo ,hanunta rik’e da wani abu a gora kamar zuma , da sallama ta shiga gidan Afnan tace ”matar Haisam na kawo miki wani sirri na musamman , da jajanyen idanunta Afnan ta dubi Salma, tace ”wa’alaikumus salam , tsoro ne ya kama Fatima tace ”yau kuma maiya faru ?”Afnan ce tace ”dan Allah ki tayani da adu’a Fatima ,insha Allah barinje gida cewar Fatima , Afnan ce tace ”mai kika kawo , a’a kibari zuwa gobe mayi magana ,to Afnan tace Fatima ta wuce gida.”

Dare nayi ta yi abubuwan da tasaba , shigowar Haisam misalin k’arfe 8pm yau ya dawo da wuri , jiki a sanyaye ta mik’e tayi masa oyoyo , ganin yau babu fara’a dakuma barkwancin da tasaba yi masa yasa shi ,k’are mata kallo ,rungumo ta yayi yana murza hanunta da ya rik’e gam , rurin da wayar sa keyi ne yasa shi sakinta , d’aga wayar yayi tare da sallama , jin muryar mama yasa shi k’ara matsawa nesa da Afnan dan yasan labarin gizo baya wuce na k’ok’i , jiyo muryar mama yayi tana cewa ,wlh inhar baka zo yanzu ba to wlh sai nayi mumunan 6ata maka rai , juyawa yayi yaga Afnan bata gurin ,ya rage muryarsa yace ”mama ganinan zuwa, karma kazo wlh zaka gane ta kashe wayar , k’ara sawa bedroom d’in Afnan yayi ,gajinta a zaune tana gyara powder fuskarta yasa shi , sakin fara’a yace ”my lovely barinje in dawo mekikeso ,in taho miki dashi¿” dariya tasa wace kamar ta dole ce tace ”dabino da kwakwa , to karki damu , cikin rawar jiki ya fice, ƙofar gida ya fita ya tada mashin ɗinsa ,kai tsaye gidansu ya nufa ,sallama yayi kana ya shige ɗakin mamanshi ,samunta yayi a zaune tana jijiga ƙafa, yana shiga ta miƙe ,cike da ɓacin rai tace “wato Haisam ban isa in gaya maka magana ba?” yanzu ƙarfe nawa? duba agogo ka gani ,Haisam ne ya kalli agogon hanunsa yace “ƙarfe goma ,to mekake nufi da maganar da muka yi dakai?” Haisam ne yace “kiyi haƙuri mama zanbi umarninki amma kibari zanyi shawara, shawarar banza cewar mama ,to wlh tun wuri kabi umarni na kokuwa na tsi…. innalilahi ya ALLAH mama ki gafarceni karkiyimin baki ,na yarda zanyi auran ,ywwa Allah yai maka albarka , nariga na gama magana hira zaka fara zuwa , kuma daga yau , a kid’ime ta kalli mama da keta washe hak’ora , dubu d’aya ya mik’a mata kana yasa Kai zai fice , dakatar dashi mama tayi , tace ”to yanzu bari a kirata a waya inyaso sai kaje ko?” shiru yayi bai ce komai ba , mama ce ta ciro wayarta a lalita ta mik’awa ,Haisam kana tace ”lalubo min lambar , Maimuna ,yana dubawa yaga number danna kira yayi ya mik’awa mama, hararar shi mama tayi tace ”nice mai zuwa zancen?” zaka fara nunamin halin naka ko?”cikin ladabi ya k’ar6i wayar , sallama tayi ,jiyayi ance “baby takake yakuma gajiyar aiki ?” muryar Haisam babu alamun fara’a yace ”zankira ki gobe , okay I love you , yana kashe wayar ya mik’awa mama.”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19Next page

Leave a Reply

Back to top button