MIJIN KANWATA COMPLETE NOVELNOVELS

MIJIN KANWATA COMPLETE NOVEL

Sai da tayi wanka ta Sauya kaya taci abinci da Sallah sannan suka sami Zama da yan”uwanta tana kuka tana Musu Godiya ta Roki gafara Wajen Hajiya Zabba”u kamar ta mata Sujjuda ta tabbatar mata data yafe mata su suka rakata ta kara Rokan gafaran Fulani tace ta yafe mata Sai Dare Salame ta samu ganin maimartaba Tana kuka tana kara Rokonsa gafara.
Cikin Alhini ya kalleta yana Fadin”Na yafe miki Tuni salamatu..Daman nayi miki wannan Hukuncin ne saboda ki gane kuskuran abunda kika aikatane..Tunda kuma kin gane bakomai Allah ya kyauta na gaba..Kiyi koyi da yar”uwanki Zabba”u Zuciyarta na Zinare ne..Sannan na Fadama yan”uwanki Bazan nemi Isa ya maidake dakin ki ba In yaji zai iya Miki afuwan na baki Daman in kuma ya Nuna A”a ki sani bazan Zura miki Ido ba Haka ba ki Daidaita da koma waye Na Daura miki aure ki tafi Gidan Auranki….!
Salame na Hawaye tace”Nagode..Allah ya kara Nisan kwana Ranka ya Dade..!
Da haka ta Dawo Cikin Gida tana kukan Tsausayin kanta,Wayoyinta Daman suna Hannun Kilishi ta Dauko mata nan take ta Goge Duka Lambobin Hajiya Zaliha,Domin itace Silan duk ma abunda ya Faru Da kanta ta Kira Laila ta Fadamata Maimartaba ya mata afuwa da Taimakon yan”uwanta Salame kuka Laila nan take fadamata ai Ta koma makaranta Tana Masters dinta,Sannan Alhaji isa zai kara aure ya Fadamata nan da Lokaci kadan Hajiya Salame Hawaye yaki Tsayamata jin wannan Labarin sun Rabu da Laila kan zata tambayeshi in ya barta Gobe Direba zai kawota ta ganta Tunda yanzu bata zuwa ko”ina Daga makaranta sai gida.
Sai Washegari su Hajiya Zabba”u suka koma,Hajiya Zabba”u har takai Abujan tana Tunanin yadda Zata Taimaki Salame ta koma Dakinta Kafin su baro sun ji labarin Auran da Alhaji Isan zai kara yazo ya Fadama maimartaba yar Wazirin Gombe yake so har sun Daidaita Har Sarki ya Tura Dan aiki Domim anema mai auran
Tana so Salame ta koma Dakinta Bazata so Ta kare haka ba Inda aka Fara sai a karisa ta hakan
Koda ta koma Abba yaji Labarim Abunda ya Faru sun yi mgana da Maimartaba kuma yaji Dadi sosai ai Hannunka baya taba Rubewa ka yanke ka yar sai dai da tayi mganar Yayi ma Alhaji isa mgana ya maida Salame yace mata ba a Haka shi bazai iya mai mgana ba ta bari in yaga zai maida ta shikenan in kuma baya Bukatarta yanzu Allah ya bata wani Dole tayi Shuri Tunda Daman wajensa ne Hop dinta.
Alhaji Isa yaji Labarin komai bakin Laila sannan ya barta taje taga Mahaifiyarta Hajiya Salame sun Rumgume da Laila suna kuka Laila taga Mommah dinta Duk ta Lalace ita kuma Salame taga Laila ta Sauya ta kara Hankali harda Hijabinta nan ta kwana suna ta Hira ta bata Labarin zuwan Hajiya Zaliha,da yarda sukayi da ita Hajiya Salame na Hawaye tace”muguwa..Allah ya Isa tsakanina Dake Zaliha..!
Laaila tace”Mommah haka Allah ya Tsara..Kada ki damu na koma makaranta na shiga Islamiya na Fara Cire Sulaiman araina na Tabbata ba Alherina bane ko yau na samu miji Aurena zan yi..!
Hajiya Salame ta Rumgumeta Tana kuka tana Saka mata albarka kamar kar tatafi Haka take ji da Zasu Rabu da juna.
An saka Ranar Alhaji Isa da Madina Diyar wazirin gombe nan da Wata Daya Da Hajiya Zabba”u taji labari ita ta Kira Salame tana kara bata baki itace ma ke baya baya da ita Hajiya tace”Salame nice fa zabba”u..!
Salame na sharan kwallah tace”Ina jin nauyin ki ne Zabba’u ban chanchanci Wannan kaunar Daga gareki ba..!
Hajiya Zabba”u tace”Kada ki damu mu manta baya..Daman ai hakan ta Faru duka don musan kaddaranmu Salame..!komai ya wuce kin ji ko..?
Salame tace”Hakane..Nagode kwarai..Ki kara bama Sunaima da Sulaiman Hakuri don Allah..!
Hajiya tace”Zan ce yazo shi da ita su gaisheki Daman sun kwana Biyu basu Leko ba..!
Salame tace”Ni Zabba”‘u..?anya na Chanchanta..!
Hajiya tace”Ke Uwace ai Salame..Sannan ai naka naka ne komai Lalacewarsa kuwa..!
Da haka suka Rabu Hajiya bata Fara Kiran Sulaiman ba sai da ta Kira Alhaji Isa tatayashi Murna sannan ta Shigar da mganarta na Ya maida Salame bazai iyama Zabba”u gaddama ba sannan yana son Salame bazai ki maidata ba ammh yaji Dadin da Zai kara aure hakan ma wani karin Sanin Rayuwar Duniyace ga Salame yace mata Kada ta Damu zai yi Tunani.
Kwana Biyu da mganarsu Salame ta Kirata tana Murma tace yanzu Maimartaba ya Kirata yana Fadamata Alhaji isa zai maidata Dakinta Za”a maida auransu Ranar jumma”,a Hajiya bata nuna mata komai ba Tayata Murna Tana Hawaye Rayuwa kenan in ba Domin Rayuwa Data koyama Salame Hankali ba Waya isa yasa ta Zauna da kishiya ammh sai gashi yanzu ko Ta kan ma Kishiyan bata Damu ba Murna ma take yi.
Salame batassn Hajiya Zabba”u ta Kira Alhaji isa ba sai da yazo sukayi mgana yace ta godema Zabba”u Tayi kuka sosai ta kima kara Tabbatar ma kanta Zabba”u bata Rama Sharri da Sharri ba ta Kirata tana ta Kuka da Godiya.
Hajiya Zabba”u tayi karamcin Domin Ranar Jumma”a Da aka maida Auran Salame da baban Laila tazo Kargi ita da Hajiya Falmata da Abba,Sulaimam da Sunaima ma sun zo Hajiya ta Kira Saraki tace ya kawo Sunaima Shi baima san abubuwan da suka Faru ba sai da yazo yaji Da kuma Daurin auran da aka Sake Awashegari Salame zasu wuce jos Laila batazo ba Tana Gida tace zata tarbi Mommah dinta Murna ya kamata Burinta ya Cika Auran Iyayanta bai kare ba Dalilinta Har Hajiya Zabba”u ta Kira tana mata Godiyan Saboda Salame ta Fadamata komai Hajiya tace kada ta Damu bakomai.
Sunaima Tsoron Allah ya kara kamata dataga Yadda Hajiya Salame ta koma Bata gama mamaki ba sai da ta Rumgumeta tana Rokonta gafara to ita me zatace ai ba ita tayima Laifi ba,Sulaimam ma da suka shigo Haka take neman Dukamai ya Dagota yana Fadin”Haba Inna..Ai har Abada Sulaiman D’a yake gareki..!
Sai kuka tana ta Godiya yace bakomai shi bai riketa ba ya yafe mata Har Abada.
Cikin Sunaima ya fito kowa ya ganta sai addu’an Allah ya Raba Lafiya Ita kunyar su Hajiya take ji su kan ba Ruwansu Sulaiman sai da ya bata kunya da sukaje gaida Maimartaba Daya kalleta yace”Diyata ina Fatan Takwara na bai kara bata miki ba ko..?fadamin in har kina kam bakan ki Yau ba sai gobe ba zan Tsaya miki sai ya baki Takardanki..!
Sulaiman na Dariya yace”ranka ya Dade..In.na bata Takardanta Ina zata kai mai sunanka ko mai sunan Fulani..!
Yafada yana Dafa Cikin Da Sauri ta matsa Tana Hararansa Maimartaba na Dariya yace’Lalle yau ka tabbatar kaci sunan SULAIMAN..Allah ya Ingata ya Raba Lafiya Allah ya baku zaman lafiya da zuru”a Dayyiba..!
Sulaiman. Nata amswa da Ameen ganin yana neman bata wani kunyan yasa ta Sulale ta koma Cikin Gida Shashen kilishi ta koma ta kwanta Ta Huta Kunyar yawo take da Cikin dake jikimta
Nan suka kwana Washegari Salame da Alhaji isa suka wuce Jos ba rakiyan kowa sai Fatan Alherin yan”uwa. ranar Sunaima gidan Hajiya uwa ta kwana Sai washegari ta Leka Gidan Hajiya Indo,Sai Monday da Safe suka koma Kaduna su Hajiya Ranar Lahadi suka koma Abuja.

Janafty
MIJIN KANWATA..!
(k’addarata)

Wattpad:Jamilaumar351
Mallakar:Janafty❤️

Kar’she..

Haka Sunaima da Sulaiman suka cigaba da Renon Cikin jikinta Cikin Soyayya da aminci Duk wani gata Takowani bangare ba inda Sunaima bata gani ba Itakam sai dai ta kara godema Allah a kullun tayi sallah sai tayi addu”an Allah ya jikan Sunaira Allah ya haska Kabarinta har gaban Abada bazata ta taba mantawa da yar”uwanta ba.
Bata da wata damuwa Su Wasim dai da gaske sun zama ya”yan Baba da Inna Basama Damuwa yanzu Daga Sunaimar har Sulaiman sun daina Damuwa dasu ko sunzo gidan basa nuna Rigima Kamar baya in zasu tafi Har Bye bye suke musu sun Riga sun zama ya”yan Inna.
Ranar Har korafi Sunaima tayi mai Bayan sun dawo Daga gidan Inna Ranar Lahadi chan yakaita ta wuni Sai Dare yaje ya Daukota kallonsa Tayi yana Driving kafin tace”Saraki da gaske kabar ma su Inna yaran nan ko..?
Yana yar dariya yace”Eh mana kin Dauka wasa nake yi..Wasim da Wafiyya na inna da Baba ne,In kika Haifi mai sunan Maimartaba ko Fulani sai na barma su Hajiya su kuma kinga an raba ne ba Cuta ba Cutarwa..!
Tana Hararansa tace”In na Sake haihuwa kuma sai ka kaima Maimartaba ko..?
Yana Dariya yace”Kai Tanque Baby kin Tunamin ya kamata Maimartaba da Abba su samu kyakyawan Tukwaicin Auramin wannan Zankadediyar yarinyar ga Son girma ga Dadin zama ga baiwa ga Basira ga Dadin chan din..!
Sunaima Hararansa kawai take yi Shi kuma yana Dariya kafin ta kada kai Tana Fadin”Allah ya shiryamin kai Saraki..!
Hannunta ya rike da Hannu Daya ya Dafa Cikinta atare Daya Turo yace”Ameen Sunaimata..Allah ya Jikan Sunaira yasa ta Huta..!
Dukkansu Cikin wani yanayi suka kalli Juna kafin su amsa da Ameen Ameen Daganan sukayi Shuru har suka isa gida ba wanda ya kara mgana Daga alamun yau Mutuwar ta Dawo musu Sabuwa,barin ma Sunaima da sai da Sulaiman ya zauna yana Lallashi kuka ta sakamai wiwi kamar karamar yarinya.
Cikin Sunaima na Shiga wata na Shida komai ya Sauya Abaya Datake gudun Sulaiman yanzu kuwa tafi shi ma son abun Tun yana mamaki Har dai ya Fahimci Ciki ne ya sakata Haka,Bata gajiya yanzu Shine ma yake Tsausayamata Saboda Cikin Dake Jikinta ammh ita bata Tsausayin kanta.
In ya dawo yaga tazo ta Rabe Daga Jikinsa tana Kifta kananan idanuwanta da bakinta kamar kuma yadda yace zai fara Dariya yana jan Karam Hancinta Daya kara Girma Yana Fadin”Uhm an zo za”a Tsotsemin Ruwa jiki..!
Shagwabe Fuska take yi kamar Zatayi kuka tana Fadin”Ni ko Saraki..Bakomai..!
Sai yayi Fuska yana Fadin”Nan fa Daya..Nan a baya ina Binki kina min Wulakanci ni da Hakkina yanzu kuma kin ga ke keda Riba sai wani nanemin kikeyi ke gashi ba ke Kadai ba Ran Mutum Biyu ni Sulaimanu Ya kike so nayi da Raina kalli Wuyana sai Faman Bushewa nake yi a tsaye kamar karan Dawa..!
Yafada yana Tattaba wuyansa Sunaima Sai ta Turesa tana Fadin”Nima bani ke kawo kaina ba..Cikin ka ke kawoni..!
Yana Dariya yace”bawani yarinya..Salon wayau ne kina Fakewa da Ciki kina Tsotsemin Ruwan Jikina..!
Sai Sunaima ta fara Hawaye tana Fadi “Naji bakomai..Nima indai ina da Hakki aka Hanani mutum shi da Allah..!
Yana Dariya ya Rike bakinsa Tana kokarin Daga kafa Ya taddaota ta baya ya Hadata ita da Cikin ya Rumgume ya kamkame yana Fadin”Abun bai kai haka ba Gimbiyata..Wasa fa nake miki ke kuma baki bani kunyar tsokanata ba.Ni naki ne Har Abada Sunaima ba ruwan jikina ba ko Jinina na yarda Duk ki Tsotse Riban auran kenan Mata tafi Miji kokari..!
Yafada yana Tusa kanta Cikin Wuyanta Kokarin Zame kanta take yi Tana Fadin”Ni ka kyaleni..!
Cikin kwaikwayonta yace”Nidai A”a..Ban yarda ba sai an Turani kan gado an yi su..!
Bata bari ya karisa ba ta Juyo da Sauri Har Cikinta na amsawa tace”Na shige su Saraki..!
Yana Dariya yace”To in baki so na Karisa muje mu kashe Arna..Nifa ina jin Dadi fa..Kinsan bayan Darajan aure Duk iskancin Dan Bariki bai isa yaci mai Ciki ba sai Aure..Shi ke da wannan Baiwar..!
Yafada yana kai Hannunsa wata Jahar tana jinsa batasamu mgana ba illah Fadi datake”Bakin ka baya Haila Saraki..!
Yana kara kamkameta yace”Ina fa zai yi Haila..ai Haila sai Sunimaita mai Kayan Dadi..!
In tace zata Biyema Saraki ko Kwana zasu yi bakinsa baya Shuru sai tasamu Dama ta Hade bakinsu Waje daya suka fara bama juna Muradinsu Daganan Da tsayuwa ta gagara aka Koma aka Zube saman Cafet ysu anan aka ssha Shagali zaku sha mamakin yadda Sunaima taja duka Ragamar Tafiya ta Sarrafa Sulaiman yadda ya kamata Duk da Cikin Jikinta kamkameta yayi yana Hawaye Cikin Wata irin Murya yake Fadin”I love u Sunaima..Kada ki barni..Kada kema ki Mutu ki barni bazan iya rayuwa baki ba wannan karon mutuwa zan yi..!
Sai da ta Rufe mai baki itama kukan take Share share kukan Kauna Soyayya da Sadaukarwan kukan kaddaranta datajata zuwa wannan Babin ayau sai gasu dukkansu suna kamkame da juna suna Share ma juna Hawaye kauna da Sadaukarwa duk alokaci Daya.
To haka dai Rayuwar ta Cigaba da Tafiya sai da Cikinta ya shiga wata takwas sannan sukaje sukayi Siyayyar kayam Haihu kala kala Both side mace da namiji Duk an yi Scan ance Namiji zata Haifa ammh Saraki yace su ba Allah bane so ba yadda zasu Beliving kam abunda suka Fada.
Saraki yasa an gyarama Sunaima Shashen Sunaira na Upstair inda Laila ta Zauna Daman Alhaji isa yace ya bar mai Duka Kayan baya Bukatar ko Daya shi kuma bayason ya Ga wani abu Daya Danganci Laila yasa aka Kwashe komai aka maida BoyQuaters,aka sauya komai na Shashen komai Sabo nan Sunaima Zata Dawo da Zarar ta Haihu ita tace ma ya barshi ma Dakinta ya isheta yace A”a yagaji da Biyota gwara ta dawo kusa dashi,Dakin kuma bazasu manta dashi ba yana cikin Tarihinsu na Rayuwar auransu shi da ita.
Dole tayi shuru ta zubamai ido BoyQuaters ma ya gyara yace Sani Direbansa zai Dawo nan shi da iyalansa sannan magajiya ma da Samira chan zasu koma wannan Shashen baya son ganin kowa daga shi sai ita sai yaransu..
Kuma tsarin yayi in zasu aiki sai su Shigo in sun gama su koma barayin su Sani kuma abunda yasa ya Dawo dashi kusa dashi Mutum ma Rahma ne ko Saboda Sunaima da kuma yadda Sani ya zama kamar kani a wajensa Sai da ya nemi Shawaran Sunaima da Hajiya suka basa Goyon baya Dari Bisa Dari.
Sunaima Cikinta na Shiga wata tara Ta Daina zuwa asibiti Duk da bata Dauki Hutun Maternity ba Sister Aneesa tace ta bari sai ta Haihu sannan ta Dauka ammh yadda take Fashin zuwa ne yasa Dole aka Sallamata Sulaiman ke hanata zuwa ganinta tayi nauyi sosai.
Sannan yanzu tadaina Rabansa Shi din daya Rabota sai ta Kama Turesa Tana Fadin”Haba Saraki baka ga Tsausayina bakasan Halin da ni ke Ciki bane..?
Kallonta yake yi in tace haka Sai ya Jinjina kai yace”Lalle naga Halin Dan adam..Abun naki ashe hawa ne da Sauka bansani ba wannan kwanaki kina Nemana kina manne dani sai da kika gama Tsotsemin Ruwan jiki..Wato Shime yanzu an gama Cin Moriyan ganga za”a yada kwallonta ko..!ni Lokacin kin Taba tambaya ta wani yanayi nake ciki Saboda ke naki ya fito ko..?
Yafada har da Sauya Fuska Yanzu itama taganesa in yana Tsokanarta Amsa take basa cikin aDanne Dariyanta tace”Ai Lokacin bani bane..Urborn bby dinka ne ba ruwana..,!.
Da sauri yace”Bana son kage..Kada ki kullama yarona Tun kafin ya fito Duniya..Malama kece fa kawai kice kina gefe kina Harbin karkasana..!
Sunaima na Dariya tace”Eh naji bakomai in ma na Tsotse ai hakki na na nema..!
Tafada Lokaci Daya tana Dagamai gira Cikin rike baki yace”Hakki..?lalle ma yarinyar kin fara Samuwa..Bakin ki haka ya Bude bansani ba..?
Yafada yana Dariya itama Dariyan take tana Fadin”Eh mana ai na Daina maka kuka yanzu..kana min zan rama..!
Gira ya Daga yana fadin”Wato kan mage ya waye..Sunaima an yi wayau yanzu..!
Dariya yake sakata yasa ta Rike Cikinta Tana fadin”Sosai ma nayi wayau yanzu.!
Kumatunta ya ja yana Fadin”Wani Wayau..?Tukunna dai..Kefa girman ne kawai da shekarun ba wayau. !
Kwabe Fuska tayi Tana Fadin”Nice ma girman ba wayau ko Saraki..?
Yana Dariya yace”To ina kika ga wayau.?Zaki hada wayanki da na Saraki ne..?Yarinya ina kika je ina kika Taka a wannan Duniyar..?Bari Maza bisa kanki..!
Yafada yana Dariya sosai yadda Zata Kule yaji Dadin Tsokanarta Hararansa Tayi kafin ta Ture kansa Dake kan Cinyarta da Sauri ya Mike Zaune yana Fadin”Anty Sunaima me yayi Zafi..?
Kai tsaye tace”Shafa kaji..!
Lokaci Daya Tana Murgudamai baki Da Sauri ya Rumgumeta ta baya yana Fadin”Kin ma isa..?ai Tunda kikace na Shafa naji..Yasin sai na Shafa din kuma naji..!
Kokarin Turesa take yafara mata Chakulkuli,ta Gefen Hamnatanta ta Fara Dariya tana Zillewa fadi take”Saraki ka bari Cikina..!
Da Sauri yace”To ki barni na Shafa na gani..!
Dole ta barsa ya fara Hidimansa Itama Tana Tayasa,Ahakan tana da Tsohon Cikin ta tallafesa da komai ya kamallah ya Matseta acikin Jikinsa yana Shafa Cikinta Lokaci Daya yana Fadin”yarinya kima godemin….!
Ture hannunsa Tayi tana Tura mai baki yar Dariya yayi yana Fadin”Daga Taimako..?ko bakisan Yawan yin nan da nake yi ba zai sa ranar Labour Kina Barci sai dai na tashe ki nace kin Haihu baki sani ba..!
Ya fada yana Dariya tana Tayashi,Cikin Dariyan yace”Allah..Wajen Santsi yake yi..Shine nake so na wasa wajen sosai yadda in kikazo Haihuwa wajen zai Wage Sai Sulum kan Yaro ya fito..!
Yafada yana Dariya bakinsa ta matse tana Fadin”Wagewa..hala kofar gari ce..?
Yana Matse hannunta Dake kam bakinsa yace”Zai zama dai..Bakin ki bari na wage wajen ba..My Urborn baby zai min aiki aie..!
Dariya take yi tana Girgiza kai Lokaci Daya take fadin”Saraki Allah ya shiryaka wanda bai Zauna dakai ba yasha Haushinka..!
Yana mata Rada yace”kamar yadda Abaya bamu Fahimci juna ba..Nayi ta jin Haushinki nace kin cika son girma da Girman kai..!
Sunaima tace”Ni kuma nace ka cika Daga kai da Dagawa ga Wulakanci..!
Yana Shafa cikinta yace”Allah..?yanzu fa me zaki ce..?
Sunaima tace”Saraki Very Friendly..Sai wanda ya zauna Dakai yasan ka..Sai ayanzu nake kara ganin Wasu Hallayarka..Kai din ka bambamta da Sauran maza..Ina Alhafari Dakai Saraki..!
Yana jin Dadin kalamanta ya Sumbaci Saman kanta yana Fadin”Nima haka Sunaimata sai da na zauna Dake nasan kedin ta musamman ce..Na kara Godema Inna ta iya Haihuwan ya”yan baiwa..!
Haka sukayi ta gayama juna kalaman Soyayya da yarda Cikin Irin Lokutan da suke samu na juna.
Sunaima ta koma tafiya Dakyar tashi Dakyar,Ciki ya yi kasa ta zama sai a lallaba Hajiya tazo kargi ta Biyo ta ganta Ganin yadda ta koma yasa tama Sulaiman mganar Sunaima ta koma gaban Inna ta Haihu nan da nan ya Hade rai yace bai yarda ba sai dai Asamo wacce Zata zauna da Sunaimar ammh a Tsarinsa babu wankan gida Tunda yana da inda kowama zai zo ya Zauna awadace Sunaima ma bata saka Rai ba Domin tasan Sulaiman bazai bari ba Hajiya kuma Daman Bata matsa ba Duk inda Sunaina Zata tayi jego barin Gidan Mijinta ne sai ta Saki.
Ammh da kanta taje ta samu Inna sukayi mganar wacce zata zauna da Sunaimar Inna tace sai taje Zuntu tayi mgana akwai Kanwarta Tani zataje tayi mgana da Mijinta in ya amince sai tazo ta zauna da ita,Haka kuwa akayi Inna Taje Zuntu ta samu Tani sukayi mgana Mijinta bai Hana ba Tunda yana da Wata Matar tace da Zarar Sunaima ta Haihu zata zo ta Zauna mata Har sai tayi arba”in.
Cikin Sunaima bai Cika EDD dinsa ba Wataranar Jumma”a ta fara Naguda Sulaiman baya nan yana Office Tunda taji alamu ta Hada kayan Haihuwa Ita da Magajiya suka tafi asibiti,Sani ta Kira yakaisu Daman yana gidan Asibitin Datake aiki ne Tunda nan tayi awo tana zuwa aka shiga Labour Room da ita Tun Safe take abu Daya kuma taki yarda afadama kowa.
Magajiya ce taga rashin kyautar haka wayar Sunaimar na Hannunta da Inna ta Kira ta Fadamata Inna batace Zatazo ba sai dai Tana gida Tana mata addu”am Allah yasa asamu kai Lafiya.
Sulaiman bai sani ba Sai Da ya Kira Sani Zasu Fita akacr Sani baya Kamfani sai ya Kirasa a waya yana Dauka yafaramai Fadan yana ina nan yake Fadamai yana asibiti ya kawo Sunaima ita da Magajiya.
Sulaiman ya fara Fada da Masifan meyasa bai Fadamai ba Hankali Tashe shida Saifullahi dake kusa dashi suka Nufi asibitin Kamar Jiransu ake yi suna Shiga asibitin Sunaima ta Haifi Santalelen yaronta mai kama Da Sulaiman kamar yayi kaki
Suna zuwa Magajiya suka iske bakin Labour room Alokacin Sister Aneesa ta Fito tana Sanar dasu Haihuwan Sulaiman Hannu ya Daga sama yana ma Allah Godiya sai da ya Tabbatar da Lafiyar Sunaima Dake Ciki suna gyarata ita da yaron sannan ya Fara Kiran waya yana Fadama Jama”a Daga Abuja sai Inna ya Kira ya Fadamata Tayi Hamdala sannan ya Kira Baba Shima yayi addu”a da Fatam Allah ya Raya..!
Duk wanda ya kamata yaji Haihuwar nan Sai da Sulaiman ya kira ya Fadamai su Sadiya suna Tsallen Kaduna tayi kira,Sulaiman ya Kira Maimartaba ya Fadamai Cikin Farinciki yace”Alhandulillah..Me aka Samu ne Saraki..?
Saraki yace”An samu Takwaran Maimartaba Kuma Takwaran Saraki Ranka ya Dade..!
Maimartaba baki yaki Rufuwa Cikin Jin Dadi yace”Masha Allahu..An kara Samun gwarzon SULAIMAN din Ne..!To wannan sai dai yaci Sunan SADAUKIN KARGI Allah ya raya Sadauki ya ingantasa ya bama Mahaifiyarsa Lafiya mai Dorewa a isar min da gaisuwata wajen Diyata ta iya Haihuwa sannan da Albishiri Din Maimartaba da kansa zai zo yayi ma Takwaransa Huduba..!
Bakin Saraki yaki Rufuwa jin Abunda Maimartaba yace haka yabama su Fulani sukayi mai barka.
Saifullahi Khadija ya kira ya Fadamawa da mama,Suma suna ta Barka da Fatan Alheri.
Basu samu ganin Sunaima ba sai Dare da aka kaita Aminity Daki na Musamman likita yace sai Gobe zasu Sallameta Allah yasa ko kari Sunaima bata samu ba.
Magajiya na nan Tare dasu Samira ce tazo Daga baya da Ruwan zafi da kayan Tea da Ferfesun kayan Ciki Sai Ahmad da Baba inna taki zuwa Daman bazata zo ba Tana da kawaici da Alkunya tadai kira Zuntu ta Sanar dasu Har Tani tace gobe insha Allahu Tana tafe

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button