MIJIN KANWATA COMPLETE NOVEL

Falon ya Sake Fitowa bai ga Magajiya ba yana shirin Zuwa Kitchen kenan sai gata ta fito Tana ganinsa ta Rabe gefe kanta a kasa tace”Yallabai wani abu kake Bukata..?
Kansa ya shafa yana Fadin”No..Wasim yaci abinci kafin ya kwanta..?
Magajiya tace”Eh Hajiya ta basu Tea Shida mai sunan Hajiya kafin ta Fita..!
In sukace Hajiyanan wani Haushi ke kamasa bai ce komai ba ya kada kai ya wuce har zai koma sama sai ya Fasa ya Karkata aqalan Tafiyarsa zuwa Dakin da abaya yake zame masa Wajem shiga da yin komai nasa na Rayuwa wani Lokacin sai ma ya manta yana da Dakin barcinsa a sama Sunaira Tana da kiyuwar Hawan Bene shiyasa sanda zai yi ginin ta Dingamai Complain shi kuma yana son Rayuwa a upstair domin tun yana Gida asama yayi Rayuwa,shiyasa bayan Tarewarsu Sunaira bata yarda ta Bisa saman sai ya shammaceta saidai shi ya Biyota ahaka ahaka duk ta Kwashe Rabin kayansa zuwa Dakinta Shi kanshi Daga baya mantawa mayake da Turakar tasa yafi Jin Dadin Rayuwa kusa da Noory dinsa tafi su.
Lokacin Daya Tun kari Dakin gabansa Sai da ya Fadi yaji wani sanyi na Shigarsa,Rabonsa da Dakin tun bayan Lokacin Rasuwar Sunaira Daya maida Dakin wajen kwanansa man yake komai,baya Fita ko”ina ya wuni aciki ya kuma kwana kayan sunaira su suka Zamemai abun Farincikinsa dasu yake kwana yake dashi Sai da Maimairtaba da kansa da Abbansa suka zo har tsakar Dakin suka Tallabeshi atare suka Fita dashi zuwa Falo suna Faman Lallashinsa da ban baki alokacin baya cikin Hayyacinsa Hawaye kawai yake domin yasan wannan Hakurin da ake bashi na Rashi ne ba na wani aabu.
Tundaga Lokacin aka saka aka kwashe komai na Sunaira aka kai gidan Iyayenyta aka Fitar da duk abunda Zai Tunamai da ita ballatana Har ya kallah yaji Rauni.
Harta kayan Dakin Lokacin da Sunaima Zata tare an sauyasu ammh har alokacin yanajin yana da alaqa mai Girma da Dakin Domin sun Zuba wata Rayuwa mai Wahala mantawa shida Sunaira acikin Dakin nan.
Lokacin Daya Dora Hannunsa Saman Handle din Kofar ya Turata ta Bude ya shiga,an Rage hasken Dakin Duhu yadan mamaye ganinsa Hannunsa na Rawa ya Lalubi makunnun Hasken da Daman ya Haddace mazauninsa ya Kunna Haske ya Gauraye Dakin Gabadaya
Wani yam yam yake ji acikin Jikinsa Lokacin Dayake bin Dakin da kallo Duk da an sauya Zaman komai acikin Dakin shi a idanuwansa yana Hango komai acikin Muhallinsa ne yana Hango kansa shi da sunaira akan Tsakiyar makeken gadon Royal din Dake Dakin Asatin dazata Fara wannan Ciwon ciwom Dayayi Sanadiyar barinta Duniya.
Yana kallon Abun kamar acikin magaji ne sanda suka gama Farantama juna rai ya Dauketa kamar yar Tsana Duk da Tana dan Jiki suka Shige Tiolet achan din ma kafin suyi wanka sai da suka kara Zuba wata Soyayyar kafin siyo wanka su Fito yana kallon Sanda ya Direta gaban Madubin Dakin kam karamar Kujeran Dreesing mirror.
Shi ya Dauko mata Handryer dinta Ya jona mata ya Fara Taimaka mata ta Busar da gashinta itama ta rantse sai ta Busar mai da nashi gashin yana ta bari ammh Taki mikewa tayi shi ya koma ya Zauna ta Rika saka Hannunta Cikin sumarsa kamar Tana Tafiyam Tsutsa Lokaci Daya tana Busar mai da gashi nokewa mata yake ganin da gayya takeyimai yasa ya Mike yana Rike Handery din hannunta Lokaci Daya yana kallon kyakyawan Fuskarta yana Fadin”Stop it Noory..Ina jin wani iri..!
Tana yarfamai Dogon Gashinta a Fuska Tana Fadin”Saboda mene Sarakina.?
Alokacin Duk duniya ita kadai ke Kiransa Saraki yaji sunan Har Tsakiyan kansa Lumshe ido yayi kafin ya Bude yana Fadin”Wani iri nake ji..In kika Cigaba da min Allah zan kara Kwakuleki ne kin sani ko..?
Dariya ta kyalkyallce dashi bai biye mata ba ya kwace abun hannunta ya kashe ya maidashi Cikin Wata Dirowa ya sungumeta gabadayanta Har Towel din jikinta na Zamewa yana Fadin”Muje na ganki..Sai kiji Dadin Dariyan Dakyau..!
Kan gadom ya Direta ya Bita ya Danne yana aika mata da sumba ko ta ko”ina,Dariya take alokacin Fararan Hakoranta suna bayyana Kiran sa sunansa take kamar koyaushe in tana son Rokonsa”Haba nawan..Sulaiman haba sulen Sunaira..Kada kamin haka Haba Abban Wasim da Wafiyya Sarkin Goben Kargi haba yallabaina Ranka ya Dade na..!
Take Fada alokacin Tana Dariya Shima Dariyan yake yana kallonta yana Fadin”Kin mamta baki Kira Inna da Baba ba..!
Mintsinansa tayi a Damtsen hannunsa yadan Saki kara Dariya ta saka kafin ta sunne kan Kirjinsa tana kara Sakin Dariyanta Kanta ya shafa yana Fadin”Ina Bukatar karin wasu ya”yan..Mai sunan Fulani nake so da Maimairtaba..!
Tana jinsa sanda ya Fara Chanza Tashar itama Tallabosa Tayi Tana Fadin”Nima zan tayaka Sarakina..Ina so na samo.mai sunanka ne na saka masa sunanka in ya Girma na Zaunar dashi na Fadamai Tarihin Sunan wanda yaci Sulaiman Gwarzon Sunaira ne har Gidan Aljannah..!
Alokacin Dagashi har ita basu san da Zanen kaddaransu ya Harbo Gefen Mahaifarta ba basusan Cikin da suka so su samu ba yana makale da ita agefen Mahaifa Domin Allah shi ya riga ya gama Nashi namu ne mutane muke Wahalar da kanmu wajen Shirmenmu Farincikin da suka kasance shine na Karshe a wannan Ranar bayan kwana Daya ya Tafi Lagos wajen Taron yadda Harkan kasuw Zata Bunkusa Taro ne yaan kasuwa Kasashen Duniya gabadaya Kamfononi da ma”aikata da manyan yan kasuwa yanachan yaji Kiran Waya kiran wayar da ya Zama Barazana ga Rayuwarsa na Labarin Sunaira ta yanke jiki ta Fadi a Bandaki Jini ya yanke mata tana asibitin Garkuwa Dake kaduna Likitoci sun Tabbatar da Ciki agefen Mahaifarta in ana son Tsira da Lafiyarta sai anyi aiki an maidashi Cikin maHaifa aikin da akayi shi da kwana Daya Sunaira ta amsa Kiran Mahallaci a Hannunsa Tana Rike da Hannayensa Idanuwanta tana kallonsa Suka ida Kafewa Ta amsa Kiran Allah akan idonsa da Idon Iyayenta da yan”uwanta kan Idanuwam Hajiyarsu da Abba da Fulani Har Duniya ta Nade bazai manta da wannan Ranar ba.
Sulaiman ya kasa Controling din yanayinsa da wannan Raunin Hawaye sun Jigamai Idanuwansa yadda baya ganin gabansa Da Rarrafe ya karisa Gaban gadon yana kaallon yarsa wacce tana da Shekara Uku aduniya Sunaira tatafi ta barta, bata ko gama Shan Dimin Mahaifiya da kowani D”a yake sha ba Mutuwa ta Raba Tsakaninsu yana kaallonta sai dai Tana Rikidemai me Tana komai ma Sunaira da irin kyakyawan Mirmishimta akoda yaushe.
Baisan sadda ya fada kan gadon ba ya Tattaro Wafiya cikin Jikinsa ya kamkameta Cikin Dashewar Murya ya Saki kukansa da amon Muryansa Hawaye na Zuba Daga kwarmim Idonsa baya Cikin Hayyacinsa yasa har baisan irin Rikon da yayi ma Wafiya mai Zafi bane sai da yaji Mutsu mutsunta tatashi Tana Neman kwantan kanta,ayadda yake wannan kukan duk bawan Mai imanin Daya gansa sai ya Tsausayamai Domin Magidanci mai ji da komai Rayuwa kamar Sulaiman Aliyu Sulaiman kwamce yana kuka kukan zucci Dana Sararin tabbas abun a Tsausayamai ne kuma aduba Rauninsa
Chan sama sama yaji kukan Wafiyya shi ya Dawo dashi Daga Hayyacinsa ya Zabura ya Mike zaune ya Rikota yana Lallashinta Fadi yake”Shiii…Sorry Hajiyata Nine..Daady ne..Baba ne..!
Gabadaya ya Rude baima san abunda yake Fadi ba ita kuwa tasan jikin Babanta da Muryansa yasa ta kara Lafewa tana Sauke Nunfashi Kwantawa yayi ya Dorata saman Kirjinsa yana Lallashinta Har barci ya Dauketa Tana Sauke Numfashi bazai iya Katse mata wannan barcin nata ba yasa ya gyara mata zama akan Kirjinsa nasa shi kuma ya Kurama Rufin Dakin ido Komai Daki Daki yana Dawo mai kamar Alokacin komai ke Faruwa
Barci barawo me ya sace shi bayan Tsawon Lokaci daya Dauka bai Runtsa ba da asuba kuma Kukan Wasiyya ya Tadashi Daga barci ta Fara Rigima ya Mike a kasalance ya Fice Dauke da ita Zuwa Dakin Magajiya ya isketa Tatashi Har ta Dauro alwala bai ce mata komai ba ya mikamata Wafiyya ya Fice tana Binta da kallon tsausayin Domin jiya da Daddaran taje Daukan Wafiiyya ta kawo ta wajenta ta kwanta Ta ganta Kan jikin Uban suna barci Tsausayinsu ya kamasu ta koma Daki tana Rokon Allah ya Tallafama wannan bawan Allah ya Dubi Rauninsa.
Sanda ya Fito Daga Dakin Magajiya yana kallon Samira na lekensa ta Kofar Dakinta Data Bude kadan ya ganta sai yayi kamar bai ganta ba Yunwa yake ji ya kwama bai ci komai ba Rabonsa da abinci tun Breakfast din Safe,Sama ya Haura ya shiga wanka a gurguje koda ya fito har an Tada Salla a wasu masallatan Farar Jallabiyansa ya saka da Hulansa Tabani kaji Hadisi ya Dauki Carbi Daman ya Dauro alwalansa ya Sauko Zuwa maaallacin Dake Tsallake inda yake Sallah yana Fita Haraban Gidan ya ci karo da Megadi yana shimfida Darduma nan gaban Dakinsa zai Tada Sallah yana ganinsa ya Shiga sosai kai Domin yasan yayi Fadan Salla acikin Gida ya Rika zuwa Cikin jam”i.
Kallo Daya yayi masa ya kauda kai bai cemai komai ba ya Bude karamar Kofa ya Fice sum sum Megadin ya Namnade Darduman yabi bayansa Sani ba anan yake kwana ba yana Hayin banki ne inda yake zaune da Matarsa da Dansu Daya.
Sulaiman bai dawo gidan ba sai bakwai na safe yana cikin masalllaci yana ta Tasibihi yana shigowa ba kowa afalon ammh har an Shirya Dining din da abun karyawa Allah Sarki Magajiya bata gajiya da Hidimansa Data yaransa Tun bayan Rasuwar Sunaira Wlh itace Bangonsa.
Sama ya Haura,bai samu natsuwa ba sai da yasha Furansa yaji Dama dama wanka ya karayi ya shirya Cikin American suit masu ruwan Toka ya matse Wuyansa da Tie ya Dauko Karamar Jakar Briefcase dinsa da Wayoyinsa ya Nufi kasa yana Tafe yana Laluban Lambar sani yasan Halinsa sai ya Zauna yana Jiransa.
Wayar ta shiga Daidai Lokacin Daya iso Tsakiyar Falon Sani ya Daga Kiran Alokaci Daya yana Fadin”Yallabai ina kan adaidai ne ganinan karisowa..!
Kwafa kawai yayi ya Datse Kiran yana ayyana Sani ya gama Rainasa Wlh sai dai shi ya Dinga jiransa kullum kamar wani Sa”ansa..!
Ya taka keman zuwa Dakin Wasim sai ga Magajiya ta fito Rike da Hannun Wasim Cikin Shirin makaranta goye da Jakarsa da Lunch Box dinsa Wafiyya ma Ma cikin kayan makarantar ta Command Childreen School,Tarkacen Jakarta na Hannun Magajiya.
Suna ganin Abbin nasu suka Saki Magajiya Harda Wasiyya Dake hannunta ta Fara mika hannu ta Saketa suka Nufeshi Shima kasa ya Durkushe ya ware musu hannu suka Shuge Wasim Dake da Wayau shi ke Fadin”Oyooyo Daddy..!.
Wafiyya da mganarta ta yara take Fadin”Daaddi..Toyoyo..!
Ta kwaikwayi Wasim Rumgumesu yayi yana jin kaunarsu na Ratsashi Cikin Muryansa sanyinsa yace”Gud Mrnin my Sweet Childreen..!
Yake fada yana Dagosu Daya bayan Daya yake basu Peck a Kumatunsu
Cikin Soyayya yace”Kun yi Breakfast..!
Wasim ya Daga kai kafin ya kalli Magajiya Dake gefe kanta na kasa yace”Magajiya ta bamu tea da Egg Daddy..!
Mikewa yayi yana Dauke da Wasiyya yana Fadin”Ehhyye..kun ci Dadi Hajiyata kema kinci Egge din..!
Kai ta gyadamai Tana Shafa sumar kansa Kallon Magajiya yayi kafij yayi mgana ta Fara gaisheshi ya amsa Cikin Kulawa
Kallonta ya karayi yana Fadin”Sannu Magajiya Nagode kwarai..!
Kanta na kasa tace”Ba godiya Tsakanimu Ranka ya Dade..Wlh bazan Taba Biyanku Tarin Alherinku gareni ba..Allah ya Jikam Hajiya karama Allah yayi mata gafara..!
Amsa mata yayi da amin kafin yace”Ba wata Hajiya karama Magajiya..babba da karamar duka Noory ce kin ji ko..?bana so ma karajin kin ce Hajiya karama..!
Kai ta gyada Kafin tace”Afuwan Insha Allahu zan Kiyaye..!
Kai ya kada yana Fadin”Zan fita wajen aiki..Daganan zai kai su makaranta Fatan komai ya kamallah?
Magajiya tace”eh yallabai..Sai dai kai Zaka Fita baka ci komai ba..?bai Damu ba yace”No karki Damu am ok…Nasha Furata dazu..kuma in naje office zan sha Tea in naji yunwa..!
Batace komai ba Domin ba Huruminta bane bata sake mgana ba Wayarsa yake Dubawa Lokaci Daya yana Sakin tsaki yana shirin mgana Sani ya shigo Falon kamar an jehosa yana Faman Sosa keya gaban sa ya Zube yana Fadin”barka da safiya Yallabai..Amin afuwa wlh ban samu abun hawa akan Lokaci bane ayi min afuwa Ranka ya Dade..!
Hararansa yayi Lokaci Daya ya Dauke kansa Sani yasan Laifinsa yasa ya Karisa ya Riko Jakar Wasim da Lunch Box dinsa Data Wasiyya ya Rike Hannun Wasim yana Fadin”Babban Mutum barka da Safiya..!
Wasim na Dariya yana Fadin”Sani…Sani..!
Wafiyya dake hannun Sulaiman itama ta Fara Zillo Tana Dariya Tana Fadin”Chani..Chani!
Sani ya juyo yana Fadin”Na”am Hajiyar Allah..Da Girman kujeranki..!
Sai bangalamai Dariya take tana Mikomai hanmu Sulaaiman ya kallah yaga ya Hade ransa kamar bai Taba Dariya ba sai ya kama kansaya juya suka gaisa da Magajiya.
Sun fara takawa zasu bar Falon Sulaiman yajuyo yana Fadin”Magajiya ina ita wannan yarinyar da Sani ya Daukota Daga Kargi..?
Sani naji ya waigo yana Fadin”Yallabai Samira kenan ai.!
Kallonsa da Sulaiman yayi ne yaaasa yayi Saurin jan hannun Wasim suka Fice Daga Falon Magajiya ta rakasa da yar Dariya Sani ai surutunsa yafisa ma karfi indai shine.
Kanta Sulaiman ya koma yana Fadin”Naga ke kadai ke ta Wahala Magajiya..ga aikin kula da yaranan ga kuma ma gida..ita ban ganta tana wani abu ba?
Kan Magajiya na kasa tace”Tana Taimakamin da kula da yaran Wani Zubin Yallabai..!
Kai tsaye yace”Wani zubin..?daman zama tazo yi..?Ina Lura da ita bata da wannan amfani koda yake ai tanayi abundaya kawota Munafunci da Saka Ido..Koda Hajiya ta kawota bashi Zai Hana naci mata Mutumcin ba Indai bazata gyara ba ai da sunan aiki aka kawota ba Hutu ba..!
Ita dai magajiya kanta na kasa batace komai ba Har ya Fice Daga Falon yana Zabgan Fada.
Yana Fita Samira ta Fito Daman Tana Labe wani kallo tabi magajiya Dashi kafim tace”In kikace zaki bibiyi Rayuwata agidan nan..Bani ce zan shiga Uku ba kece domin ba Kargi ma Zaki koma ba sai da aneni Dangin masu Dattin Hula..Ni Hajiya ta kawoni kuma Umarninta nake bi acikin Gidanan ki kula ki kuma kama Girmanki kafin na Fadamata abunda kike shirin yi..Tsohuwar banza kawai..!
Tafada tana sakin Tsaki Kafin ta wuce tana wani kada Jiki kamar mazari,Da kallo Magajiya ta Bita dashi batace komai ba,Domin bata da tacewa Tun zuwanta Gidan banda Rashin Da”a babu abunda Take shukamata in anyi mgana tace Hajiya to daman ai sai ita kuma gaskiya ta Fada Hajiya Zabba”u bata kyashin cin Zarafin duk wanda ya shuga Harkanta Shiyasa data Fahimci hakan ta kama kanta da Samiran Tana jin Dadin zama da Yallabai bazata so wani abu ya Gifta ba.
Sun gama shiga Motar yau da 4matic dinsa zai Fita dukkansu shida ya’yan nasa Gidan baya suka shiga riverse sani yayi tare da Hon megadi ya wangalemusu get suka Fita sai dai basu kai Fita ba Saboda mai adaidatan daya Tsaya gaban get din Sunaima ta Fito Daga Ciki ta Bude Jakarta ta Dauko kudinsa ta basa ya Tafi saidata Juya ne taga Motar tsaye Tana Jiran ta kauce.
Gefe ta koma Tana kallonsu suka wuce Fuu kamar zasu tashi Sama Glassan Tintied ne Shiyasa bata ga yadda su Wasim suke ta Ihun kiran sunanta ba.
“Anty…Anty….!
Harda wafiya Dake kan jikin Uban Tana Tsalle tana Fadin”Anty Radam a abakinta shi kam ta iya Kira,Sani kam sai da ya maganta ya juyo yana Fadin”Ranka ya Dade…Hajiya fa suka gani kaji suns Ihun kiran Anty..!
In motar ta tanka to sulaiman ya Tanka Wayarsa ma ya Fiddo yana Laluban Habib yaga Kiranss da Safe Lokacin yana wamka yayi bakam Daga sani har yaran,har suka gama kiran sunan Anty suka Hakura.
Har cikin makaranta yakai su kamar yadda ya saba Wafiyya tana Nurseey 1 ne yayinda Wasim ke primary 1 kowa ya saba Daman Sulaiman ke kawo su kuma Baya Tafiya shi da Sani sai ya Damka kowamnensu ajinsu hannunsu malamansu da Jakansu da Lunch Box dinsu da tunsuna Rigima in ya kawosu zai tafi har suka Saba in zai Tafi suna mai Bye bye abaya Tare da Sunaira wani Lokacin suke kawo wasim ko kuma in ya makara ita ta Tuka Mota ta kaishi Lokacin ba”a Saka Wafiyya ba sai bayan Rasuwarta aka Sakata,Daganan kamfani suka wuce.