NOVELS

GARKUWA PART 3

Acan cikin ɗakin Mamey kuwa.
Sosai sautin addu’a da karatun da Jafar keyi yatsanan ta yana kankame da Mamey, wacce ke ƙwance ida nunta a rufe, har lokacin bata farka daga.
Baccin sihirin da akasa takeyi ba saboda nauyin. Baccin da suka je fata ciki.
Sheko bakinsa baya iya furta komai sai addu’o’in sai kuma hawaye da keta tsatstsafowa daga cikin ida nunsa sabida fargarba da kuma zafin da yakeji,
Abba kuwa dake can part ɗinsa da yake Part ɗin shi na natsakanin na matan nashi ne.
Yana cikin ɗakinsa dake sama.
Haka yasa yarinƙa jiyo muryar Jafar da irin addu’o’in dayake cikin kiɗima, da kajin addu’ar kasan acikin tsananin firgici da tashin hankali yake yinsa,
Wuf yamike yanufo part in Mamey kasan cewar babu wata tazara sakaninsu.
Gudu-gudu sauri-sauri ya isa.
Cikin hanzari yatura kofar bedroom ɗin Mamey cikin sananin tashin hankali da kaɗuwa ganin yadda Yah Jafar ke rungume da Mamey sai innalillahi yake da karfi hawaye yagama wanke fuskarsa idanunsa sun yi jazir saboda kuka da zafin da yakeji da fargabar ganin tamkar Mamey a mace take a kiɗime yanufo in da suke yana faɗin.
“Subahanallahi kai Jafar meya farune me ya sameta?”.
Yayi tambayar hankali a tashe, tare da miƙa hannu ya ɗago kan Mamey dake kan kafar Ya Jafar yashiga girgizata yana kiran sunan ta.
“Aisha! Aisha!! Ummu Jabeer!.
Gani shiru bata ko matsi sai dai tana numfashi ya tsananta firgicinsa.

Hankali a tashe yakuma kallon ya Jafar wanda keta addu’o’in babu ko kakkautawa.
Mai da kan Mamey’n yayi ya kwantar kan cinyar kafar Jafar.
Kana ya juya a kiɗime ya fita a ɗakin da sauri ya nufi sashin mahaifinsa Lamiɗo.

Shi ko ya Jafar cigaba da maimata innalillahi yakeyi yana zubda hawayen.

A can ɓangaren Hajia Mama kuwa.
fitowar ta daga ɗakinta kenan cike da jin daɗin yadda bokan ya karfafa mata guiwa tanajin daɗi a ranta yanzu komai zai tafi mata yadda take bukata zata rabu da zugar yayan Mamey da ita duk kowa ya huta, tana fita ta hangi Abba ta window yafita daga cikin part ɗinsa hankali a tashe.

Fuska ta ɗan yamusa tazauna saman ɗaya daga cikin kujerun parlour’n, can kuma tamike kamar an tsikareta tabi bayansa da sauri.

Acan shashin Lamiɗo kuwa.
Da sauri Lamiɗo da Galadima suka mike, bayan Abba yagama sanar musu abin da ke faruwa.
A tare suka fito suka nufi part ɗin Mamey’n.

Lamiɗo na gaba Galadima da Abba na biye dashi suka shiga ɗakin, in da Abba yabar Yah Jafar a haka suka iske shi yana ganinsu ya miƙe da sauri Mamey yashiga nuna wasu Lamiɗo da hannu yana kuka yana nuna musu ita da kwatanta musu yadda Hajia Mama tayi mata.

Da sauri Hajia Mama ta turo kofar dan taga shigowar su Lamiɗo’n.
Jafar kuwa yana ganinta yashiga nunata da hannu sai kuma ya nuna Mamey’n yana cigaba da ƙwatanta yadda tayi matan shidai baki kam babu shi sai dai addu’o’in da kuma kukan dayake tayi.

Gaba ɗaya su suka maida kallonsu kan Hajia Mama nan take Lamiɗo da Galadima da Abba suka ɗiga ayar tambaya a kanta.
itako ganin bawai magana Jafar ɗin keyiba sai bata damuba bata kuma fahimci cewa sun zargi meyafaru ba kuma basu gane me. Jafar ɗin yake cewa ba da hakan ba.
Hajia mama kuwa cikeda da karfin hali irin nata na makiran mugaye mata tafara tafa hannu tana masar kwalla tana faɗin
“Innalillahi wa’inna’ilaihirraji’un Jafar me nake gani haka me yasami Mamey’n ku? kayi magana mana”.

Sai kuma tasaki kuka mai haɗe da salati.
Lamiɗo ne yaɗanyi gyaran murya ganin Mamey’n tafara motsawa alamar tafarka daga nannauyan Baccin da take mikewa tayi zaune tare da zuba musu ido.
Da sauri suka ɗan matso gareta kana duk suka mai da hankalin su kanta.
Suna ce mata sannu Aisha, Amman shiru ba amsa.
Cikin tsananin sauri da tsoro Abba ya matso kusa da ita tare da zubawa yatsun kafarta ido mamaki cike da kiɗima yake kallon yatsun kafarta da suka fara sauya kamannin halitta suka koma kamar na tsuntsu.

Cike da alhini suma su Lamiɗo suke kallon yatsun kafar nata, hankali a tashe.
Cikin gigita Abba ya kamo hannunta tare da nunawa Lamiɗo murya a daburce yace.
“Innalillahi wa innailaihi rajiun Lamiɗo kalli yatsunta”.
wani matsanancin tashin hankalin ne yakuma dabaibayesu lokacin da suka ga yatsun hannunta yafara komawa irinna fiffiken tsuntsu.
Gaba ki ɗaya su haɗa baki sukayi wajan furta “innalillahi wa’inna’ilaihirraji’un hasbullahu wani’imalwakin”. Sabida tsananin firgici da tashin hankali gaba ɗaya jikinsu rawa yakeyi.

Cikin matsanan cin tashin hankali Lamiɗo da cushewar tunani Lamiɗo ya juyo ya kalli Galadima murya a hargitse yace.
“Subahanallahi maza a kira Malam Musa yanzu nan”.
Cikin hanzari Galadima ya amsa da. “To”. Kana yajuya da sauri yafita.

Kan kace me labari yabaza masarautar Joɗo,
Batare da bata lokaci ba sakon kiran da Lamiɗo yayiwa Malam Musa ya isa gareshi.

Cikin ƴan daƙiƙu malam Musa ya iso cikin masarautar Joɗa Lamiɗo yabada umurnin a shigo dashi har cikin ɗakin Mamey.

Yana shiga kallonta malam Musa yayi cikin tashin hankali ya girgizata kai kana yakallesu Lamiɗo yace.
“Sihirine a kamata mai haɗe da tsafi kuma daga yanzu zuwa ko yaushe ko wanne lokacin zata iya juyewa daga mutun ta dawo tsunsuwa”.
Salati suka ɗauka baki ɗayansu nan kuma ɗakin yakacame da koke-koke su Jamil da Jalal Affan Ummi Jafar yayin da duk muryar Hajia Mama yafi amo wajen kuka da shiga tashin hankali ziraran miraran.
(uhum makircin mugu kenan.)
(Sai daifa akwai kishiyoyi na gari da matsalar kishiya kan sasu kukan gaske wlh.)

Ranar kuwa wannan masarautar taga tashin hankali mara misaltuwa,
Jiƙe-jiƙe da hayaƙi da shafe-shafen magungun gargajiya babu wanda malam Musa baiba, kiɗima yasa sun mance da suyi amfanin da ayatul shifa.
Ganin anyi duk abinda za’ayi na gargaji abin yaci tura ne yasa hankalin.
Dr Aliyu yakasa ƙwanciya gani yake ko wata cutarce ta da ban haka yasa ya fitadaga ɗakin yatafi part ɗin sa,
kiran wasu manyan likitoci a bokansa.
Yasanar musu koda wani shawarin da zasu basu bayan sun gama wayar kuwa.
Kayan ai kinsa ya ɗauko yakomo ɗakin Mamey’n yayi iya gwaje-gwajen sa babu abinda ya gane na wani cuta ko wani abu.
Cikin takaici Malam Musa yace.
“Kama bar gwada ta babu wani cuta face sihiri”.
Daga karshe dai dole ya hakura.
Ranar babu wanda ya rumtsa kusan a tsaye suka kwana nan cikin ɗakin Mamey’n ganin yadda gaba ɗaya kamannin halittarta ke juyewa, Gimbiya Aminatu tayi kuka iya kuka.
Lamiɗo ya kira Jadda ya sanar mishi halin da ake ciki tashin hankali iya tashin hankali Jadda da Sitti sun shigeshi nan suka fara shirin tahowa.

Can gabanin kiran sallar asuba lamari ya ƙara munana dan a lokacin suffar Mamey ta gama juyewa izuwa na tsunsuwar Boleru a gabana a gabansu Lamiɗo a gaban mafiya yawan al’ummar Masarautar Joɗa.
nan take kuwa Abba ya yanke jiki yafaɗi yasuma.
Cikin kiɗima Dr Aliyu yayi kansa yafara bashi taimakon gaggawa.
Mamey kuwa da yanzu takoma tsuntsuwa fara kaɗa fiffikenta tayi alamun son tashi take.

Ai kuwa tamkar al’mara sai gashi ta tashi firr ta fire tabi ta window dake a buɗe tayi tacikin Garden tashige cikin tawagarsa tsuntsayen dake wurin.

Innalillahi Jamil Jalal kuwa suma sumewa sukayi.
Cikin hanzari da kiɗima Lamiɗo da Galadima suka zo jikin window nan suka hango ta ta sauka cikin tsuntsayen kawai sai suka fashe da kukan tsoron al’amarin duniya.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button