NOVELS

GARKUWA PART 3

To lokacine mukaga sarƙar dake wuyanta.
Mai ɗauke da tambarin masarautar Joɗa kasan cewar masarautar fulɓe ce kuma mahaifin Alhaji Abboi abo kine ga Lamiɗo akan ɗan ziyarci juna kaɗan kaɗan to sanadin hakane Alhaji Abboi ya gane tambarin dake jin sarƙar na masarautar Joɗa ce.

Tofa anan muka gane cewa duk yadda akayi ita ahalin masarautar Joɗa ce.
Kuma Sarkin bakanmu ya tabbatar mana ita mutunce aikin sihirine to sai dai babu yadda za’ayi mu fuskanceku da mgnar kai tsaye tunda bamu san komai nakuba.”

Ɗan tsakaita maganar yayi yaɗan ja numfashi kana yaci gaba da faɗin.

“Ni banine mahaifin Shatu ba Alh Abboi shine mahaifinta ga kuma mahaifiyarta.

Ni makiyayin mahaifinta ne.
inayi masa kiwone yana biyan.
Mafi akasari duk karshen wata suna zuwa tare da ita nan Rugar Arɗo Babayo.
To ita Shatu tanason yanayin daji rugarmu shiyasa duk sanda zaizo da ita zai zo, in zai koma kuma wasu lokutan yakan koma yabarta anan Rugarmu da yake ranar Jumma’a yake zuwa, to sai ranar lahadi da yamma Al’ameen ko wani daga cikin yayunta yazo ya ɗauke ta su koma.
Yawan zuwasu shi yasa tasaba da da yarana sosai da mai ɗakina.

To amman zuwansu da Allah ya ƙaddara lamarin Ummey ta juye a gabanta fir babu yadda ba’ayi da ita ta komaba taƙi bin mahaifinta fir taƙi tace ita zata zauna da Ummey ita ta zaɓa Junainah suna.
Wannan yasa dole mahaifinta ya koma ya barta.

To lokacin da Ummey’n Shatu’n ta faɗo hannunmu muka kuma ga wannan sarkar dake wuyanta na masarautar Joɗa shine Alh Abboi yace mu ƙaura mu dawo nan.
Nigeria kusa da masarautar Joɗa cikin Rugar Bani dan tasami kusan ci da masarautar.
to nan fa muka dawo Nigeria har da ita Shatu’n dan taƙi yar da a raba su da Ummey’n ta ashe rabo ke jawota nan.
dole iyayenta suka haƙura suka barta tare dani.
Muna dawowa nan muka sata a makarantar cikin Shikan”.
Nan yaci gaba da basu labarin duk wani bayanin gwa-gwar mayar da
Shatu tayi a ka Ummey
duk sai da ya basu labari.
Ya ƙara da cewa.
“Lokacin da muka zo Nigeria da Ummey
wato (Mamey) Ba’ana naɗan shekaru sha takwas a duniya, lokacin (Parvina) wato Shatu kenan ita kuma du-du shekarun ta takwas ne,
to kafin mu dawo ma Mamey bata dawo daga haiyacin taba bata fara magana ba, lokacin da mukazo.
Nigeria Rugar Bani sai Ba’ana yace zai bata mgnin zata fara mgn kuma zata zama dai-dai sai dai zaiyi wuya ta tuna baya,
Amman zata dawo tayi mgn amman da sharadi. kasan cewar fatanmu ta tuna baya mu maidata ga ahlinta yasa mukace mun amince da sharaɗinsa wanda bamu san menene sharaɗin ba.

Shi saida ya fara bata mgnin kuma yace sai da sharaɗin in Ummey ta worke ta fara mgn muyi al’ƙawarin aura mishi Shatu.
To lokacin mu baƙine bamu san halinsa na ɓoyeba kuma burinmu da fatanmu ta worke mu maidata hannun ƴan uwanta sai muka amince mukayi mishi wannan al’ƙawarin bisa rashin sanin halin daga ranar Mata yake kiran Shatu.

Kullum Shatu ita ke zuwa gidansu Ba’ana da safe tana karɓawa Ummey magani a gunsa, dan shi tun tashin sa yake wannan cacube-cacuben nasa, so kullum.
Shike bawa Shatu magani ta kawo wa
Ummey tana sha har Ummey tadawo tafara magana sai dai bata iya tuna baya ba nan. Ba’ana’n ke ce mana duk randa taga wasu nata ko ƴan uwan ta ko wani abu nata zai yiwu tunanin ta
yadawo ta iya tuna baya.”

Sai kuma ya ɗan tsagaita tare da sauƙe numfashi kana a hankali yaci gaba da cewa.
“Toh tun daga ranar ne muka fara neman hanya da dalilin da zai haɗamu daku mutanen masarautar Joɗa.
Sabida munsan aikin sihirine dole akwai Magauta sannan a gefen Ba’ana kuwa ya addabemu ya hana Shatu salama duk mai sonta sai yaga bayanshi.

To sai marigayi Cuɓaɗo ya bamu tabbacin bulalin Shaɗin masarautar Joɗa ne kawai zai karya duk wani sihirin jikin Ba’ana to kasan cewar yana sonta so na gsky bai cutar da ita in hankalinmu ya tashi kan muna tsoron ya aureta takan ce mana.
“Abinda in na gama karatuna zamu koma Yahunde sabida ita bamu sanar mata mun gano asalin Ummey ƴar ina bane gudun ita yarinyace kada tai ta gayawa wasu.

To munata son yadda alaƙa zata haɗamu sai kuma ga ƙabilar ɓachama su tasomu gaba.
Ran da muka zo nan na forko da muka ga Jamil sosai muka ƙara ƙarfafa guiwar ita ahlin masarautar Joɗa ce dan akwai kamar jini tare dashi da ita.
To da akayi faɗa kukaje mana jaje da gayya Arɗo Bani ya gaggayawa mai martaba Lamiɗo mgn dan ya tunzurashi ayi Shaɗi mu jefi tsuntsu biyu da dutse ɗaya kenan.

Mun dawo da ita, mu kuma samu mgnin Ba’ana to kuma Alhamdulillah duk abin neman ya samu.

Sai kuma yayi ƙasa da kanshi murya na rawa yace.

“Sai dai sanadin faɗan ni na rasa kowa nawa”.
Bappa ya ƙarashe mgnar cikin rauni da zubda hawayen tuno matarsa da zaratan yaranshi.

Cikin raunin tuno ahlinshi kuka mai rauni ya rufeshi yayinda Shatuma kuka mai ƙarfi ya kubce mata hakama Ummey sabida ita dai gata ta dawo ahlinta shi kuma garin dawo da ita cikin ƴaƴanta ya rasa nashi yaran.

Cikin tsananin jin daɗi
Sheykh ya ɗan muskuta cikin tsananin farin ciki da jin daɗin da godewa Allah daya bashi damar kuɓutar dasu ƴaƴan Bappa su Gaini shima zaisa Bappa farin ciki kwatankwacin yadda ya sashi.
Cikin sauri da bada umarni ya kalli Jamil tare da cewa.
“Jamil tashi maza kaje kazo dasu”.
“To”. Jamil yace kana ya miƙe da sauri yafita batare da ɓata lokaciba sabida ya gano su waye Gaini.

Yana zuwa yace.
“Yah Gaini taso taso kuzo ga Bappanku da Shatu da Junainah”.
Ai kafinma ya rufe baki duk sun muƙe cikin tsananin zaƙuwa suka biyo bayanshi.

Shi kuwa Bappa da Arɗo Bani da Alhaji Haro da Alhaji Umaru rauninsu ya rigada ya dawo tuno irin kisan gillar da ƙabilar ɓachama sukayi musu.

Shi kuwa Sheykh dasu Lamiɗo shiru sukayi sabida son yi musu ba zata.

Da sauri Jamil yasa hannunshi ya tura ƙofar suka shigo tare da cewa.
“Assalamu alaikum Bappa share hawayenka gasu Yah Gaini Seyo da Giɗi”.

Duk sauran mutanen falon duk suka ɗago kansu.

Ido cikin ido Shatu tayi da Yah Giɗi’nta abokin tsamarta.
Wani irin yunƙura tayi ta miƙe tsaye tare da cewa.
“La’ilahaillaha Muhammadu rasulullah Sallallahu alaihi Wasallam Alhamdulillah Bappa gasu Yah Gaini”.
Jin kalaman Shatu ne yasa Bappa dayake sunkuye ya ɗago kanshi yana kalli bakin ƙofar shigowa ya sauƙe kwayar idanunshi kan…..!

Kuyi haƙuri da typing errors ina cikin ciwon kai nayi typing ɗin a daddafe.

Littafin GARKUWA na kuɗine Special Group 1k Normal group 300.
A yawan posting ne babban cinsu 0005388578 Jaiz Bank Aisha Aliyu Garkuwa in kin tura sai kiyi screenshort na Debit Alert ki turo min ta whatsApp 09097853276 ƴan 3oo in naki da halin biya ta Account zaki iya sayan katin mtn na ɗari uku ki copy numbers ɗin ku turo min ta whatsApp ɗin 09097853276.

                            By
              *GARKUWAR FULANI*

4/6/21, 4:15 PM – &: “Aranar wata jumma da da wanna Zazzafar ƙaddara ta rufta damu shekaru goma sha uku baya.”
Sai kuma ya ɗan tsakaita
tare da jan
sassayan numfashi ya gyara
zamansa tare dasa tafin hannunshi ya share hawayensa.
Yayin da gaba
ɗayansu kacokam
suka mai da hankalin su kansa,
Duk sun ƙagu suji yadda a kayi a wannan ranar da basu manceba.
Shi kuwa Yah Jafar wani numfashin yakuma.
Saukewa kana yaci gaba da cewa.
“Ranar da dare bayan anyi sallan isha’i duk muna falon Mamey dani dasu Jalal Jamil Affan da Ummi da Imran yana ɗan sheksru takwas lokacin.
Anan mukaci abinci kana muka zauna muna hira.
Kasan cewar akwai shaƙuwa mai tarin yawa tsakanin Mamey da Affan da yake tana da son yara.
Amman son Affan da banne a wurinta har su Jamil kance wa Affan na hannun daman Mamey.
Takanyi Dariya tace.
“Eh ɗin ai ya fiku nitsuwa”.
Muna zaune sai hamma Mamey keyi tare da miƙa da lumshe idonta hakane yasa tace mana.
Duk ta sallamemu saida safe tanajin bacci.
Ummi tace.
To.
Still Kuma sai mukaci gaba da hira.
Da ido muka bita ganin ta miƙa cikin sanyi tace.
“Kai zanje inyi bacci wlh wani irin bacci mai nauyi nakeji yana fuzgata tamkar zan faɗi.
Ni na shiga saida safenku”.
Allah ya bamu al’khairi mukace dukanmu kana ta shiga.
Tana shiga kwanta ko second uku batayi da kwanciya ba tayi bacci.
Mu kuwa muna gama hira muka watse.
To su Jalal ne ƙarshen fita ashe basu tasheta ta rufe ƙofarta ba a famintata kenan fa?”.
Ya ƙare mgnar yana kallon su Jamil.
Da sauri Jamil yace.
Eh.
Cikin sanyi ya kalli su Lamiɗo kana yaci gaba da cewa.
“Ina komawa ɗaki na kira Juwairiyya muka fara hira a waya kamar kullum.
To bayan mun gama
waya da Juwairiyya
har na kwanta sai na mike na nufi
ɗakin Mamey dan
inaso nayi mata magana a kan Juwairiyya fa tasanar wa mahaifin su maganar auren mu da ita, tun da lokacin takammala
karatun ta dan haka itama ta gayawa Abba na ayi batun aurenmu dan nima tuni lokacin na gama karatuna har na fara aiki.
Kuma a kwanakin ne aka bani sarautar Galadima wanda da mijin Gimbiya Saudatu ce mai matsayin to daya rasune Lamiɗo ya maida mulkin kaina.
A zatonshi ta hakane zaisa yaranshi bazasuyi faɗa da junaba tunda bazasuce ya baiwa wane ya hana waneba.
Ni a lokacin dagani har Mamey da Jabeer da baya ƙasar ma ba son wannan mulkin mukayiba bisa dole aka bani ita.
Sai kuma ya jingina bayanshi da kujera kana yaci gaba da cewa.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button