NOVELSWATA ALKARYAR COMPLETE HAUSA NOVEL

WATA ALKARYAR COMPLETE HAUSA NOVEL

WATA ALKARYAR COMPLETE HAUSA NOVEL

“Kiyi hakuri Harirah insha Allah nan da wata biyu zuwa uku zata kawo mana ita, insha Allah  zan dawo Miki da yar ki, don Allah mu bar maganar a tsakanin mu. Domin kar a aji a ce mun cutar dake” ko gabanta bata gani ta fita a gidan bata gani ta nufi waje, Sadam kam dama ya gaji zai leka ne yaji ko lafiya, sai ga Ammyn ta fita tana kuka. Bude mata motar yayi ta ce mishi.
“Zaman asibiti ya kare kaje a sallamo Jamilah ta dawo nan. Ba zan iya rasa su ba domin zuciyata zata iya bugawa.”
“Ammyn lafiya?” Cikin wani irin kuka ta d’ago kai ta ce mata.
“Wai ta tura ta aikatau birni, waye ta sani a inda za a kaita? Hannun waye zata fada? Shin taci abinci? Zata yi wanka waye ya cutar da ita? Me aka mata? Ya take duk ban sani ba sai dai Allah ya sani yasan halin da take ciki, Ya Allah ka san halin da nake ciki, Ya Allah Ya kare min ita.” Haka ya tadda motar suka bar kofar gidan, har ya. Kaita gida, bata daina kuka ba, sannan ta roke shi da ya dawo da su Jamilah, ba zata iya zama ba a can ba zata zauna a kofar gida tana jiran dawowar Rabi’ah.  Duk yadda yaso ta zo asibitin fir taki domin ta zuciya baki daya gani take idan ta bishi Rabi’ah ba zata dawo ba, shi yasa tace yaje kawai.

  Tunda ta shiga cikin gidan, ta shiga daki ta zube akan gwiwowin ta, take kuka, cikin tausayin halin da Yarinyar take ciki, ita sai a saninta Rabi’ah bata da lafiya, tunda ta dauke ta taji yarintar ta koma kamar takarda, babu zuri. Amma Gwaggo Lami ta hanatae’ da tafiya da ita ashe rabon su gana ne yasa ta je gidan, domin idan ba shi ba, babu abinda zai ta mintsinin ranta, har sai da ta je ta ga halin da take ciki, haka tayi ta kuka.

   ..
Sadam ya tafi asibitin anan ta samu likita ya sallame Jamilah saboda wani damuwar da ya kuma taso musu, haka suka sallame Jamilah, Rahmah tana rike da hannunta suka fito, kallon garin take kamar yau ta fara gani da idanun ta, shaÆ™ar iskar da yake kad’awa me zafi, ta bude shi akan Buharin Baba Haliru, da mugun tsoro ta damke hannun Rahmah. Jikinta yana rawa, bude mata mota wasilah tayi zata shiga yazo da sauri zai fincikota, Sadam ya rike hannun shi.

Zaro idanu yayi yana kallon su, zai magana ya nuna mishi hanya, yana matsawa Sadam ya d’aga gefen rigar shi dan dole yayi shiru tare da nufar hanyar shi.
300â‚?… Insha Allah’
+2347035133148 a tuntube Zahrah Addah Ramlat, Yan Niger su tuntubi Nana A’ichah
+22784506476
0472282105 Ramlat abdulrahman manga GT bank

Mai_Dambu

3/1/22, 18:53 – Nuriyyat: WATA ALKARYAR…!
The Beginning of Destiny
Na
Mai_Dambu

BUZHUWA Emphire🐪🐪
Assalamu Alaikum,Barkanmu da wannan lokacin ,Sannun mu da shigowa Halarar mu na buzaye.... Albishirin ku matan Aure💃💃💃 BUZUWA EMPIRE ta taho maku da sirrika na MALLAKAR mijin ki yar uwa a hannun ki ba tare da boka ko malam ba. Matan da yawa na fuskatan matsalolin su da maxajen wato kalubalen a gidan auren mu...kuma irin wannan maganin matan Asha tabaje...mene wani shirme wani gayinan dai ,bashi ne ba... Ina macen da daga zarar mai gida yy sallama gaban ki keda yara ya hau fadi?. Ina macen da mijin ta kullum idanun shi na akan matan banxa?. Ina macen da ga kudin mijin yanada amma babu ci sai dai duniya suci yy kyautan riya? Kai duk wani matsalan ki na gidan Aure kizo taskar BUZUWA EMPIRE. zata baki mallaka ta hanyar sirorin kur'ani da dai sauransu. Mallaka ta hanyar kwai Mallaka ta hanyar nama ,madara ,kifi , yan shila da dai sauran su.. Ga kuma mallaka ta hanyar suratul yusuf . Mallaka ta hanyar jauhara. Mallaka ta hanyar Yaseen Mallaka ta hanyar fatiha umul qur'an. Mallaka ta hanyar turaruka da dai sauran su... Ina Yammata marasa farin jini ?💃 Kuzo kuma da naku ,sai kaji ana gata mummuna baka kirin amma sai farin jinin manyan alhajazai masu jifa jifai kome take dashi oho..!! Kuji ita tasan inda tazo ta taho taskar BUZUWA EMPIRE . sai kin taho yar uwa gaba daya sirrin nan na farin jini dana mallaka 5k ne duka . Idan kuma mallaka ne kadai munayin na 2k da kuma 3k. Na farin jini kacal 3k ne ,gamasu bukata zasu tuntu6a wannan number 08081202932/09061466409.

Uwa mana da Mama<17>

Last Free page

NA HAD’AKI DA GIRMAN ALLAH IDAN XAKI SAYA KI FITAR MIN DA SHI WALLHI NA YAFE IDAN KUMA KIKA FITAR MIN DAN KI B’ATA MIN RAI ALLAH ZAI SAKA MIN DARI UKU NE BAN TSAWWALA BA BAN KUMA TAKURA KI BA BANA SON RIGIMA DA KANANUN MAGANA MA’ABOTA HANKALI DA NUTSUWA SUN SAN YAREN DA NAKE NUFI

Ganin bindiga a kugun Sadam ya sa shi barin wurin ba dan yana jin ya hakura ba, sai dan tanadin da yayi musu na idan ba a fito mishi da Uban shi ba sai ya illata su baki daya, dan haka ya kudiri Aniyar samar kan shi hanyar da zai na samun su yana cin Uban su.

            A hanyar  komawa gida Sadam yana tuki, wayar shi tayi kara, bai dauka ba sai da ya isa kofar gidan su, kafin ya dauka ya ga number Aaman ce. Zai kira wani kiran ya shigo mishi dauka yayi tare da sallama ya ce mishi.
“Man baka da kirki, kayi kokarin ganin kazo domin kome ya lalace fiye da da can baya”

A kage ya tambaye shi.
“Meke faruwa?”
“Hmm bari zan maka bayani an jima ya kashe wayar sai da ya ga sun shiga cikin gidan sannan ya juyar da motar yayi tafiyar shi a hanya ne ya kira Aaman yayi mishi bayanin halin da ake ciki, kamar zai yi Hauka kafin ya kashe wayar dan Ihu yake da masifa, sai kace Sadam din ne ya kai ta aiki dan haka ya shiga masa masifa.

    A cikin gidan kuwa sun sami Ammyn tasha kuka ta koshi, idanunta basu daina zubda kwalla ba, kuma sun tambaye ta taki gaya musu halin da ake ciki, tayi tasan halin Yaran ta, sau su kuma dulmiyar da Jamilah cikin wani hali, dan haka tayi shiru, tana jin a ranta kuka ba shi bane mafita, ta karfafa zuciyar ta, yadda Yaran suma zasu tsaya da kafar su,.ba yadda zasu koma bayan wani suna kuka ba, sai abu na gama da ta ji a ranta babu makawa Allah yana tare da su, shine addu’oi. Dan haka ta rike wannan gam a ran ta.

   **
Dutse.

Dake me motar dama mutumin Yar duwala ce, yasan inda zai ajiye ta Yaran, dan haka wani Unguwa ne can irin tsofin unguwar nan ya kai ta, suna isa aka bude Yaran, suka yi ta fita kowannen su yana komawa gefe.

  Duk cikin Yaran Rabi’atu ita ce karama kuma mara lafiya, akwai wasu yan mata biyu manya sunan dayan Altine dayan kuma Hinde,. Tunda suka shiga cikin motar Altine take kula da Rabi’ah, dan tayi mata kyau, ita kuma haka Allah yayi ta da son abu me kyau, gashi tana mata dibi da kanwarta Hansiya, haka yasa ta rike hannun Rabi’atu, har suka shiga cikin gidan da aka nuna musu, yar Duwala na tare da driver.

“Gaskiya kin kara min wani abu, ko kuma ki zab’a min wacce kika san wani kato bai fasa ta ba, nazo na rage dare da ita” ya fada tare da zama cikin motar shi yana dariya. Itama cikin ko in ta ce mishi.
“Amma kasan kan duniya ba zaa rasa ba, kuma zaka samu me dadi dan kasan Yan matan kauye ba irin na birni bane masu taurin kai.”

          Tab’e baki yayi cikin kwarewa da iskanci ya ce mata.
“Anya ba zan koma gurguran kananun Yara ba? Domin na fahimci manyan nan basu da wata kamun kai kamar Yaran”
“Hmm! Akwai su kuwa amma kasan idan ka tab’a karamar yarinyar zai zama laifin cin zarafi ne, ka gwada manyan mana.”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99 100 101 102 103 104 105 106 107 108 109 110 111 112 113 114 115 116 117 118 119 120 121 122 123 124 125 126 127 128 129 130 131 132 133 134 135 136 137Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button