AUREN TAGWAYE HAUSA NOVEL

⏱. *Misalin 'karfe 3:00pm*
Aka taru a masaalacin dake ‘kofar gidan Alhj mansir mutane ‘kalilan suka sheda d’aurin auren Jabeer Suleiman tankuri da Amaryarsa Hussaina Mansir kamfani, bisa sadaki dubu hamsin.
Bayan ankammala Alhj mansir yasa aka gabatarma duk mutanen dasuka halarci d’aurin auren abun lasawa take away akayima akaiyma kowane suka wuce suna sanya Albarka.
Bayan ankammala wannan daddy yashiga gida da sallama, su duka falo ya taraddasu zaune Momy ce ta amsa sallamar, Hassana tace “daddy sanu da dawowa “yauwa ya amsa,
Hussaina kuwa daddy nashigowa jikinta yafara kyarma dan wani masifaffen tsoronshi takeyi, cikin muryar tsoro tace “d…dad…daddy sannu da zuwa.
Wani matsiaycin kallo ya watsamata sannan yawuce d’akinsa batare daya amsa sannu d’inda tayimashiba.
Can bayan kimanin minti baiyar yafito ya kalli Hussaina “ki shirya yanzu inaso zan fita dake kuma minti talatin nabaki, kinajina “inaji daddy tafad’a tare da mi’kewa tanufi d’akinsu jiki na kyarma.
Daddy kuwa fita yayi harabar gidan, waya yakira jabeer “ya masu aikinnan sun kammala kuwa,? Ya tambaya
cikin ladabi jabeer yake magana “Eh Alh sunyi kusan minti sha biyar ma da gamawa.
“Sun had’a kome dai yanda yakamata ko?
“Eh sun had’a kome 2 bedroom ne da falo 2 sai kitchen ba abinda ba’a zubaba na bu’kata.
“Owk to anjima ka shiryar tarbar Amaryarka,
Kasa magana jabeer yayi saboda kunyar Alhj yakeji sosai.
“Basu dad’e da kammala wayaba wata had’addiyar mota tayi parking ‘kofar gidan sannan wasu maza suka ri’ka jido akwatina suna shigowa dasu saida suka shiga da guda goma manya- manya, sannan sukayima jabeer bayani Alhj mansir yace akawo kayan amaryane.
Mamakine yahana jabeer magana danshi harga Allah yayi niyyar had’a wannan kayan Amma Alhj yahashi had’a kome.
Love u all my Fan’s ???????? shoki ????????♀
[1/5, 8:31 AM] Zee Elkaseem: ???? AUREN TAGWAYE ????
????????????????????
????????????????
????????????
????????
????
Written & Story by
Zee Elkaseem
{Mmn khady}
Dedicated to All member’s group of Ciwon “ya mace ????????
Page………………….17
Da misalin ‘karfe biyar na yamma Hussaina tafito cikin shiri sanye take da riga da zani d’inkin simple atamfar brown colour haka takalmin ‘kafarta yayi kala da kayan jikinta sai ‘katuwar hijab data sanya, ahankali take takowa hartazo gaban dadynsu cikin ladabi tace “na shirya daddy
“Owk muje ko, yafad’a yana nunamata ‘Kofa.
Ganin tana tafiya Ahankali kamar kazar da Kwai yafashemawa a ciki yasa daddy yayi gaba ya zauna a mota yana jiran fitowarta.
Fanin fitarsa yaba Hussaina damar yin magana “Momy wai ina zamu?
Momy tace “kin tambayi kaza hanyar rafi…..
Ni kaina da kike gani bansan meke wakanaba nidai kawai abinda nasani naga tunda Alhj yatashi yau yaketa hidima ko zama yaci abinci beyiba.
Hassana dake zaune tace Allah dai yasa Alkhairi ne, ni kaina ina mamakin yanda daddy yace Hussaina ta shirya su fita batare daniba, Alhalin nasan ko’ina tare muke zuwa.
Momy tace “to wannan abu dai Allah kad’ai yasani, kiyi sauri kibishi kada kuma yaga kin 6atamai lokaci.
Juyawa tayi tafita daga falon batare data ‘karayin wata maganaba.
A mota ta iske daddy zaune yana jiran fitowarta, gidan gaba tanufa da niyyar tashiga harta kama murfin motar zata bud’e daddy ya watsamata wani matsiyacin kallo “koma baya.
Jiki na ‘kyarma takoma ta bud’e bayan motar tashige, sannan daddy yatayar da motar Malam bala yabud’emasu get yana d’aga masu hannu suka d’au hanya sannan yamaida get d’in yarufe Yakoma kan d’an bencinsa ya zauna yana cewa “gaskiya Alhj ya iya maganin d’an iska, wato yarinyar nan wlh da Alhj beyi saurin Aurar da itaba saita d’aukomar abin kunya. Kodayake bansaniba shin itace koba itabace oho nikam bani ganesu, radio shi yajawo ya kunna yacigaba da sauraron abinshi.
Daddy kuwa ba inda ya zarce da Hussaina sai unguwar dutsin safe malali Quarter’s inda nan tangamemen gidan jabeer yake, bakin get yayi horn da sauri megadi ya bud’e mashi ciki yashiga ya ajiye motarshi inda aka tanada dan ajiye motocin, fitowa yayi sannan ya umarci Hussaina data fito itama, ba musu tafito tunda suka shigo take yaba kyan gidan, saikuma yanzu ta’kara ganinshi sosai tsarin gidan ya burgeta, a zuciyarta tace “nan kuma ko gidan waye? Amma ko gidan abokanin daddy ne bamu ta6a zuwaba, kuma sabodame daddy yaza6i yazo dani ni kad’ai banda Hassana Alhalin duk inda zamu tare muke tafiya da ita……
Daddyne ya tsinkemata tunanin datake ta hanyar cewa “shigo mana.
Ba musu tabi bayanshi wata ‘Kofa yabud’e wacce tasadasu da babban falon gidan me d’auke da maka-makan kujeru irinna zamani a tsakiyar falon gefe kuma kan wani step kujerun dining ne da ‘katon table d’insu, daga gaba kuma inda suke facing wata ‘katuwar TV ce plasma ma’kale jikin bangon sai manyan speaker’s (Home theaters) gefensu kuma wasu kyawawan flower’s ne masu d’aukar ido, duka kayan falon sun kasance purple colour hatta da pentin d’akin kalarsa kenan,
Daddy yace “to Hussaina wannan gidan da kike gani bana kowa bane face gidan mijinki……
Dammmm gabanta yayi wani mummunan fad’uwa da sauri tad’ago ta kalli daddy ganin ba wasa tattare dashi yasa tamaida kanta ‘kasa gabanta nacigaba da fad’uwa.
Daddy yacigaba da magana “naza6i na aurar dake dakijawomin abin kunya, saboda nan shine gidan aurenki, ki zauna kibi mijinki kiyi mashi biyayya Aljannarki tana ‘kar-kashin tafin ‘kafarsa idan kinbishi kisamu idan kuma kin baud’e wannan kuma Allah yasan hukuncin daya tanadar maki.
Saboda haka iname umartarki daki zama me biyayya a gareni ni mahaifinki dakuma mijinki ki zauna lafiya.
Nan daddy yayimata nasiha me ratsa jiki kafin yayimata bankwana ya ajiyemata bandir d’in kud’i yan dubu yace “saboda idan kina bu’katar wani abu bance ki matsama mijinkiba,
Bayan tafiyar daddy kasa tashi tayi daga inda yabarta, tunani take “wannan wane irin aurene daddy yayimin kamar auren wasa, to wai yaushema aka d’aura auren? Kuma waye mijin? Ina daddy yasamu mijin daya yarda da aure cikin kwana d’aya tak? Haka tagama jerama kanta tambayoyi amma batada amsarsu kuma batada Wanda ze amsa mata, hakan yasa tafashe da wani irin kuka, tana cewa “shikenan yanzu nasan daddy baya ‘kaunata menayi….menayi daza’a yankemin wannan hukuncin.
Love u all my Fan’s ???????? shoki ????????♀
[1/7, 10:28 AM] Zee Elkaseem: ???? AUREN TAGWAYE ????
????????????????????
????????????????
????????????
????????
????
Written & Story by
Zee Elkaseem
{Mmn khady}
Dedicated to All member’s group of Ciwon “ya mace ????????
Page………………….18
Kuka take iya ‘karfinta babu me rarrashinta sai da tayi me isarta sannan ta tashi falo na biyu tashiga wanda shima yaji set d’in kujeru da kayan kallo amma sai dai shi bekai na farkon haduwaba shikuma kome nacikinsa green colour ne, tsayawa tayi ta’karemashi kallo sannan tanufi wani d’akin nan kuma bedroom ne wanda aka zubama kaya yan Dubai ba ‘karamin kyau d’akin yayiba, fitowa tayi daga nan tanufi gudan d’akin ahanakali tatura ‘kofar tashiga nan ma karo tayi da wani ‘kawataccen d’akin kwana shikuma duka kayan yan Nigeria ne aka zuba amma harma sunso Sufi na Dubai d’in kyau.
Bayan tabi ko’ina na gidan ta’karemar kallo dawowa tayi a bedroom ta zauna tsakiyar gadon tare da rufe fuskarta da hijab d’inta, take tunanin Hafiz ya dirar mata a zuciya, wani irin kuka tafashe dashi a zuciyarta tana cewa “yanzu shikenan anrabani da Hafiz mutumin danafi so nafi ‘kauna akan kowane namiji, bazan iya zaman aure da kowane namiji ba bayan Hafiz yazanyi da rayuwata, haka tacigaba da kuka tana zancen zuci.