BABU SO HAUSA NOVEL

AUREN TAGWAYE HAUSA NOVEL

Bayan sunkammala breakfast ne daddy ya kalli Hussaina tare da d’dd’aure fuska kamar beta6a dariyaba yace “inaso kigayamin gidan ubanwa kikaje jiya.

“Uh…im asibiti naje ganin mamar ‘kawata.
“Da izinin wah kika fita?
Kallon Momy tayi suna had’a ido Momy ta watsamata wata muguwar harara, ba shiri ta saddar da kanta ‘kasa, tayi shiru.

Dadyne yacigaba da magana “koma waye ya d’aure maki gindi a gidannan kike Neman lalacewa tonidai ba agabana ba, kuma yau basai gobeba zan d’auki mataki kanki dan bazan zauna ina kallonki kijamin surutu a gariba, yana gama fad’in haka ya d’auki jakarsa yafice daga gidan ranshi a matu’kar 6ace.

Love u all my Fan’s ???????? shoki ????????
[1/2, 8:33 AM] Zee Elkaseem: ???? AUREN TAGWAYE ????
????????????????????
????????????????
????????????
????????
????
Written & Story by
Zee Elkaseem
{Mmn khady}

Dedicated to All member’s group of Ciwon “ya mace ????????

Page………………….15

Daddy ne Zaune office d’insa yahad’a hannu bibbiyu ya buga tagumi ba abinda yake tunani sai irin rayuwar da Hussaina take neman jefa kanta,

Mi’kewa yayi tsaye ya maida hannuwansa duka biyu baya tare da fara zagaya office d’in yafara zancen zuci “yanzu wane mataki yakamata in d’auka dan ganin nayima tufakar hanci bata war-wareba, yau kimanin shekara ishirin ina tarbiyantar da yarannan amma lokaci d’aya suna nema su bijiremin, komawa yayi kan kujera ya zauna tare da maida kanshi sama ba abinda yake tunani sai abinda ‘yan sandan dasuka kawo Hussaina gida suka fad’i na cewa sun kamata cikin Halin maye, wato rayuwar dazata jefa kanta kenan, wadda daga haka mutum ze iya aikata kome hatta da kisan kai mashayi na iya aikatawa batare da shakka ko shayin irin hukuncin daze biyo bayaba.

“Assalamu Alikum, da sallama jabeer yashigo office d’in hannunsa d’auke da wasu files-files, jin shiru ba’a amsa sallamar ba yasa ya’kara yin wani sallamar karo na biyu, nanma shiru daddy be amsaba dan yayi nisa cikin tunanin dayake, guri jabeer yasamu ya zauna tare da ajiye files-files d’in kan tebur d’indake gabanshi da d’an ‘karfi yanda daddy zeji karar ajiyewar. Hakan kuwa ya maidoshi daga dogon tunanin dayake ya d’ago da kanshi ya kalli jabeer “Ah jabeer badai har kagamaba, “eh nagama gashinan saura wad’annan files d’inne sunada ‘yar matsala akwai takardun da babu aciki, yafad’a yana ware wasu files guda biyu gefe.

“Owk to ba Matsala idan na duba zanyima magana sai a gyara, “to kawai yafad’a tare da mi’kewa ze fita daga office d’in harya kai bakin ‘kofa daddy yayi kiransa “jabeer, cikin girmamawa jabeer ya amsa tare da dawowa ya zauna,

Saida daddy yayi shiru na kimanin minti biyu kafin ya sauke ajiyar zuciya “Jabeer dama inason magana dakai “to Alhj Allah sa dai lafiya,
“Eh to lafiya lao, kan maganar Aurenka da Hussaina kanasonta kuwa har yanzu?
Cike da jin kunyar tambayar da daddy yayimasa ya amsa da “eh.

“To bakada matsala inaso da anjima bayan sallar azahar kataho da magabatanka da shedu koda basu wuce mutum gomaba, nima zan sananar da ‘yan’uwana za’a d’aura aurenku kaida ita, bani bukatar kome naka sadaki kawai zaka taho dashi naira dubu hamsin,
Kada kayi mamaki kan wannan abin dana aiwatar akwai dalilin yin hakan Wanda nasan koda kaji dalilin na tabbata bazaka’ki jininaba,

Jabeer dai shiru yayi yana sauraron Alhj cike da mamaki a zuciyarshi yana cewa “wannan shine ikon Allah me tsaida wando koba zariya, kome wannnagaggawar take nufi Allahu wa’alamu.

Haka ya kauda kowane tunani cikin zuciayrshi yayima daddy godiya sannan yakoma office d’inshi.
Koda ya koma tunanin dai yahanashi sukuni saboda haka rufe nashi office d’in yayi Yakama hanyar gida.

     *Waye Jabeer*

Jabeer Suleman shine asalin sunanshi Haifaffen garin katsina, Alh sule tankuri shine mahaifinsa sai mahaifiyarsa Hajiya sa’ada sunada rufin asiri Bakin gwargwado amma ba’a kiransu masu arziki, su biyu iyayensu suka haifa dagashi sai ‘kanwarsa Nusaiba wacce akwai tazara sosai tsakaninsu dan ahalin yanzu nusaiba bata wuce shekara sha shidda zuwa sha bakwaiba yayinda jabeer yakeda talatin da d’aya.
Tun yana d’an shekara sha bakwai mahaifinsu yarasu lokacin mahaifiyarsu na d’auke da ‘karamin cikin nusaiba bayan rasuwar mahaifinsu da wata bakwai ta haifi nusaiba, haka sukacigaba da rayuwa yau da dad’i gobe babu, yayinda mahaifiyarsu ta tsaya tsayin daka dan ganin jabeer yayi karatu, da kyar da sud’in goshi sukasamu ya kammala karatunshi a F.C.Ekatsina kasancewarshi hazi’ki yasa yasamu sakamako me kyau amma dukda haka samun aiki yayi wahala kusan shekara biyu yana neman aiki besamuba, kwatsam rannan yaji ana Neman ma’aikata a Company Alhj mansir badan yasa ran zesamuba yaje yayi interview cikin ikon Allah kuwa saiga sunanshi cikin wad’anda aka d’auka aiki, sunyi matu’kar farinciki shida mahaifiyarshi da ‘kanwarshi, ranar dazefara zuwa aiki mahaifiyarshi tayimashi nasiha me ratsa jiki akan ri’kon amana da gaskiya, sannan tabishi da addu’ar samun s’a.

Bayan wata shidda dafara aikinsa Alhj mansir yalura da Halin gaskiya da ri’kon amana na jabeer hakan yasa yajawoshi jiki tare da ‘karamashi matsayi a office d’in Wanda a halin yanzu shine mataimakin manager company.

Masu yimin magana ta prvt najina dasukayi shiru kwana biyu Dan Allah kuyi hakuri na rashin ganin reply d’ina naga sa’konku saidai be karantuwa kasancewar nasake download whatapp ne nagode da kulawarku.

Love u all my Fan’s ???????? shoki ????????‍♀
[1/4, 7:48 AM] Zee Elkaseem: ???? AUREN TAGWAYE ????
????????????????????
????????????????
????????????
????????
????
Written & Story by
Zee Elkaseem
{Mmn khady}

Dedicated to All member’s group of Ciwon “ya mace ????????

Page………………….16

Saboda haka cike da tunani barkatai jabeer ya isa gidansu, ‘kanwarsa Nusaiba yafara gani zaune falo tana kallon wani Indian film me suna salam namaste, da sauri ta tarbeshi tanamashi sannu da zuwa, bayan ya amsa d’akinsa yanufa ya ajiye jakarsa sannan ya dawo falon, har yanzu dai nusaibar ce ita kadai a falo tambayarta yayi “ina mama?
“Tana bedroom,
“Owk kawai yafad’a tare da nufar ‘kofar dazata sadashi da d’akin kwanan mahaifiyar tashi, da sallama yashiga d’akin zaune ya isketa gefen gado hannunta ri’ke da waya da Alama waya tagama, kallonshi tayi bayan yasamu guri ya zauna kan bedsite “a’a jabeer yanaganka kadawo tun yanzu ko mantuwa kayine?
“A’a mama ba mantuwa nayiba wani babban Al’amari ya maidoni Wanda ni kaina ya d’auremin kai,

“Wannan wane Al’amarine tafad’a tare da maida duka hankalinta gareshi,
“Watako yanzu danaje office shine Alhj yakirani yake cemin inje insanarda magabatana kuma inbada kud’in sadaki naira dubu hamsin yau ze d’aura aurenmu da Hussaina.

“Alhamdulillahi mama tafad’a tare da d’aga hannuwanta sama tana godema Allah, kai Amma naji dad’i wannan abu ai abun farincikine dama kullum Addu’ata be wuce inga aurenkaba, Allah sanya Alkhairi yabaku zaman lafiya.

“To amma mama kina ganin babu wata matsala, “wace matsala haba jabeer me kanema karasa inaji kadade da kammala gidanka, kuma Hallacin da Alhj mansir kamfani yayimana ai kobakada kome yace ka auri d’iyarsa ka aureta kazubama sarautar Allah ido dan nasan baze barka hakaba,
“To mama Allah dai yasa haka shine mafi alkahiri,
“Ameen haka nikeso naji kana fad’i.
Daga nan yafita zuwa d’akinshi ya canja kaya sannan yakoma yayima mamarsa sallama tare da sanar da ita zeje ya d’auko mutum ukku dangin babanshi sannan mutum ukku a dangingin ita mamar tashi, fatan Alkhairi tayimashi sannan yafita.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button