BABU SO HAUSA NOVEL

AUREN TAGWAYE HAUSA NOVEL

“Yanzu ni waye wanda daddy yaza6amin anya zan iya zama dashi, ita ko kad’an bata kawoma ranta jabeer ne wanda aka d’aura mata auren dashiba.

Zaune take tabuga uban tagumi hannu bibbiyu ba abinda ke mata yawo a kwalwa sai kalar salon soyayyar da Hafiz ke nunamata, yanzu shikenan anrabamu baze ‘kara shayar dani zumar ‘kaunarsaba.

Mi’kewa tayi tsaye kamar wacce aka tsikara “baze yiyuba tafad’a a zahiri bazan iya rabuwa bada Hafiz ba ko ana ha maza ha mata, Hafiz shi kad’aine namijin dazan aura in kasance cikin farin ciki, ko waye wannan yayi gan-ganci daya yarda da aurena, tabbass zesan abinda ya auro ya kawo gidanshi.


Momy da Hassana kuwa tun bayan fitar daddy da Hussaina suketa sa’ke-sa’ke da kwancewa sun rasa ina daddy zashi da Hussaina batare da yar’uwartaba Alhalin shine yasaba masu da duk inda zasu tare suke tafiya.

Da sallama ya shigo falon suduka binshi sukayi da ido ganin yadawo batare da Hussaina ba,
Momy ce tayi ‘karfin halin tambayarsa “Alhj ina Hussaina take naga ka dawo kai d’aya kuma bayan tare kuka fita.

“Tana gidan mijinta, yabata amsa a takaice sannan yawuce d’akinsa, binshi tayi daga baya zuciyarta cike da mamaki.

Hassana dake zaune tanajin abinda daddy yafad’a itama tashi tayi tanufi d’akinsu tana cewa “innalillahi wa’innalaihirraji’un “Gidan miji…. tafad’a cike da mamaki, yaushe aka d’aura auren sister bamu saniba dan gashi alamu sun nuna itama momy batasan da zancen ba,
“Ya salam tafad’a tare da dafe kanta da hannu biyu dataji yana saramata kamar ze rabe biyu, fad’awa tayi kan gado tana zubar da hawaye.

: Cike da 6acin rai momy take magana “haba Alhj ban fahimce inda zancenka yadosaba.

Juyowa daddy yayi ya kalleta tare da yin wani murmushi, sannan yace “baki bu’katar in maimaita maki abunda nafad’a d’azu saboda inada tabbacin kinji kome nafad’a.

“Lalai Alhj yanzu ka tabbatar min da baka ‘kaunar Hussaina akan me zakayimata irin wannan hukuncin, aure cikin kwana biyu kamar auren d’iyar kara, haba Alhj kuma amatsayina na mahaifiyarta yaci ace nasan da maganar amma bansaniba kuma banida labari kawai saika tafi da yarinya kace wai wani ka kaita gidan miji, gaskiya ni ban yardaba kawai kafad’amin inda d’iyata take inje in d’aukota idan kai baka sonta ni ina sonta, duk wannan maganganun da momy keyi tanayinsune cikin 6acin rai da d’aga murya.

“Dakata Maryam, daddy yafad’a cikin d’ga murya “wannan auren na d’aurashi kuma yariga ya d’auru ba wanda ya isa ya war-wareshi, ince idan yarinyar nan ta jawo mana abin kunya zagin daza’ayimin baza’ayimaki rabinshiba, saboda haka nariga na yanke hukunci idan kinji hukuncin danayimaki bemakiba zaki iya kama gabanki hanya a bud’e take yara kuma nawane inada iko akansu.

Tunda daddy yafara fad’a momy ke kallonsa cike da mamaki a zuciyarta tace “lallai Alhj da gaske yake kuma ba wasa tattare dashi dole nima inbi ahankali.

Cikin langa6ar da kai momy tamatso kusa da daddy ta dur’kusa gabansa “Haba Alhj meyakai na 6acin rai haka, indai kan wannan maganar ne inshaAllah kome ya wuce Allah sa haka shine mafi Alkhairi a rayuwar Hussaina, itakuma yar’uwarta Allah kawomata miji na gari.
“Ameen daddy ya amsa tare da shigewa toilet ya watsa ruwa sannan ya d’auro Al’walar magrib dan lokacin sallar yayi.
Itama Momy d’akinta tanufa ta d’aura Al’wala ta kabbara sallah bayan tagama ta dad’e kan abin sallar tana kwararo addu’a ga yaranta.

Love u all my Fan’s ???????? shoki ????????‍♀????
[1/8, 9:50 AM] Zee Elkaseem: ???? AUREN TAGWAYE ????
????????????????????
????????????????
????????????
????????
????
Written & Story by
Zee Elkaseem
{Mmn khady}

Dedicated to All member’s group of Ciwon “ya mace ????????

Page………………….19

Zaune take cikin d’akin tarasa mekemata dad’i a duniya, wayarta ta Dauko sunan zuby ta lalubo sannan ta danna kira, bugu d’aya zuby ta d’auka.
“Hellow ‘kawata kin 6oye kwana biyu.
“Hmm kedai bari kawai zuby idan ana sallah ba’a magana.
“Banganeba ‘kawata wani abune yafaru dake?
“Abubuwa da dama sun faru dan ahalin yanzu wayar nan damuke dake ina gidana.
Saurin tashi zaune zuby tayi daga kwancen datake “bangane gidankiba ‘kawata, gidanki ko gidanku?
“Hmm gidana dai dan daddy yamin aure kuma yau natare.
“Aure kuma Hussaina, to waye angon zuby ta tambaya gabanta na dukan ukku-ukku kada Hussaina tacemata Hafiz ta aura, idan ko haka ta kasance da ba abinda ze hana abkuwar ‘karamin ya’ki tsakaninta da Hussainar.
Hussainar ce tadawo da ita daga duniyar tunanin data lula,
“Wlh nima har yanzu bansan ko waye mijin ba, amma inaso kizo gobe,
“To shikenan ‘kawata zanzo amma wane unguwane?
Nan Hussaina tabata full address sannan sukayi sallama kowanensu ya tsinke wayar.

Zuby kuwa tashiga tsananin rud’ani, tashi tayi tsaye tafara kai komo cikin d’akin “tabbass idan har tunanina ya tabbata Hussaina Hafiz ta aura tofa sainayi yanda nayi narabasu koda kuwa ta Hanyar salwantar da rayuwartane, inason Hafiz ina ‘kaunarsa bazan juri ganinshi tare da wata maceba bayan ni, wasu zafafan hawaye suka zubo daga idonta tasa hannu ta goge,sannan tanufi lokar dake jikin gadon d’akin tasa hannu ta fiddo kwalbar kodin ta tuttule a bakinta ta shanye sannan tafad’a gado tana mayarda numfashi kafin bacci yayi awon gaba da ita.

: Hussaina kuwa cigaba tayi da bin d’akin da kallo kad’an-kad’an takai dubanta ga ‘Kofa tana jiran ganin shigowar angon nata.

Ringing d’in wayarta tajiyo da sauri tasa Hannu ta d’auka dan tana tunanin zuby ce takirata kozata gayamata wani abu amma sai ganin sunan Hafiz tayi 6aro-6aro yana yawo kan screen d’in Wayar, sai da gabanta yayi mummunan fad’uwa bin wayar tayi da kallo har kiran ya tsinke sake kira akayi karo na biyu nanma batayi gigin d’aukaba dan ganin kiransa kayar mata da gaba yakeyi, duk dahaka beha’kuraba ya’kara kira karo na ukku hannunta na rawa ta daure ta danna OK tare da karawa a kunnenta batayi maganaba sai shi yafara magana.
“Hellow babyna kina lafiya?
Shiru tayi duk illahirin jikinta kyarma yake dan jin muryar Hafiz kad’ai jefata yake cikin wani yanayi me wuyar fassarawa.
Magana ya’karayi karo na biyu “hello babyna ko bakyajinane.
Sannan ta daure murya can ‘kasa-‘kasa tace “ina jinka.
“Amma kuma kikamin shiru, kinsan kuwa yanda nadamu dake, kinsan halin dana fad’a na rashinki danayi kwana biyu……

Cikin d’aga murya da masifa Hussaina tafara magana “dakata Hafiz bakada wani dad’in baki dazakayimin bayan ka cuceni ka cuci rayuwata karabani da abinda duk wata mace take ta’kama da tin’kaho dashi a duniya.
Amma bakome ba laifinka bane laifinane dana d’auki yardata nami’ka maka d’ari bisa d’ari, gashi yanzu ina gidan mijina banida wata daraja da ‘kimar daze kalleni da ita.

Dakata Hussaina nifa bangane inda maganganunki suka dosaba,
“Tunda ka yaudareni ka kaini gidanka da sunan zan gaisheda hajiyarka ashe da wata manufar ka kaini danka ketamin haddi…….

Jitayi ana doka sallama daga falo hakan yasa tayi saurin kashe wayar baki d’aya ta turata ‘kar’kashin filo, sannan tayi saurin janyo hijab d’inta tarufe fuskarta dashi.

Jitayi annufo d’akin datake hakan yasa fad’uwar gabanta ya yawaita,
“Assalamu Alaikum warahamatullah, yafad’a tare da ‘karasowa cikin d’akin ya zauna bakin gado.
Koda jin muryar kunnenta ya tabbatar mata da tasan me wannan muryar jin ‘kamshin turarensa yadaki hancinta ya’kara tabbatarmata datasan kowaye,
Saurin bud’e lullu6in datayima fuskarta tayi dan tabbatarma idanunta abinda take tunani.
Tana bud’ewa kuwa sukayi ido hud’u da jabeer, a firgice ta nunashi da hannunta tana fad’in “Jabeer dama Kaine mutumin dayaimin yankan ‘kauna, karabani da Wanda nakeso, kasa daddy yayimin aure irinnan d’iyar wasan yara aure cikin kwana biyu, bayan nadad’e da sanar maka inada wanda nakeso bakaiba, to ina me tabbatarma saikayi danasanin aurena dakayi, idan kayine dan farincikin rayuwarka nikuma ka ba’kantamin rayuwa to wallahi kaima ze zama ba’kin ciki a gareka.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button