BABU SO HAUSA NOVEL

AUREN TAGWAYE HAUSA NOVEL

Hafiz yad’an 6ata rai “Haba babyna sabodame zaki hanamin kanki?
“Saboda kwakwkwaran dalili, Hussaina tabashi amsa.
“Inaga babu wani dalili dazesa ki hanamin wannan lallausan jikin naki me tarin ni’ima, a da kika amince dani baranrantana kuma yanzu da kome zamuyi baza’a ganeba kawai ki amincemin mu shana, yafad’a tare da jawota jikinsa ya matseta gam.

sai kunyi ha’kuri da typing saboda ‘yar matsalar da wayana ya samu koda aka gyara sai naji duk ta canjamin typing d’inma baya sauri

Love u all my fan’s ???????? shoki ????????
[1/26, 3:05 PM] Zee Elkaseem: ???? AUREN TAGWAYE ????
????????????????????
????????????????
????????????
????????
????
Written & Story by
Zee Elkaseem
{Mmn khady}

Dedicated to All member’s group of Ciwon “ya mace ????????

Page………………….31

®TALANTED WRITER’S GROUP (T.W.G) ????

Saurin tureshi tayi daga jikinta tare da mi’kewa tsaye cikin 6acin rai take magana “haba Hafiz wannan wace irin rayuwace, kabar ganin nakawo kaina gareka hakan ba yana nufin zan mallaka maka duk abinda kake bu’kataba daga gareni, akwai dalilin dayasa na amince da zuwa gidanka harna baro gidan aurena, duk wannan maganganun Hussaina tanayinsune cikin tsananin fushi da matsananancin 6acin rai.

Ran hafiz ya 6aci da jin maganganun Hussaina yayi niyyar gayamata magana kamar yanda gayamar amma sai wata zuciyar tace “fushi ba naka bane kabita a hankali har kasamu ha’karka ta cimma ruwa.

Cikin sanyin jiki hafiz ya dur’kusa gabanta shikenan babyna na ha’kura amma kitaso muje mu kwanta yafad’a tare da kama hannunta.

Fizge hannunta tayi daga rikon dayayimata tare da komawa kan kujera ta zauna tace “kaje kawai ni anan zan kwanta, tashi hafiz yayi yanufi bedroom jikinsa a sanyaye a zuciyarsa ba haka yasoba yaso ace ya kwashi gara ta hanyar kusantar Hussaina dan dama ya dad’e rabon dayayi mu’amula da wata mace tunda suka samu sa6ani da zuby kusan sati batazo gidanshiba wanda ada yasaba baya kwana biyu basu had’u suka she’ke ayarsuba.

Da haka ya haye gadonsa zuciyarsa fall da tunani “to miye amfanin zuwan wannan yarinyar guna tunda bazanji dad’i da itaba, amma bari inbarta inga iya gudun ruwanta zuwa gobe kuwa idan ta’ki amincewa zan danneta kota ‘karfi, dan nariga na kwad’aitu da ni’imar jikinta da wannan tunanin bacci 6arawo yayi awon gaba dashi, yayinda Hussaina batayi wani baccin kirkiba sakamakon wani mummunan mafarki datayi da Hassana Hakan yasa ta yanke hukuncin komawa gida gobe dan ganin halin da ‘yar’uwarta take ciki.

** ** **

Kiraye-kirayen sallarY asubah yatashi jabeer daga bacci yakai hannunsa inda yake tunanin jin matarsa amma sai yaji wayam tunaninsa yakai ga tana toilet yadad’e yana jiran firowarta amma har ana niyyar kabbara sallah masallaci batafitoba ahankali ya tura ‘kauren toilet d’in ganin bata ciki yabashi mamaki shiga yayi ya d’auro Alwala yafito falo ga mamakinsa ganinta yayi kwance kan kujera ta tada kanta da pilon kujerar tanata sharar bacci.

Cike da mamaki jabeer ya’karema Hassana kallo wacce shi atunaninsa Hussainace a zuciyarsa yace “me hakan ke nufi Hussaina ta canja hali ta ko’ina tana kyautatamin amma kuma yanzu tana ‘kauracema shimfid’ata sa6anin da da bata kyautata min amma kuma tana bani Ha’kkina na aure dan koban kirataba zata kawo kanta to kodai tana cikin lalurane, amma kotana lalurar fashin sallah tasan duk hanyar sazatabi ta biyamin bu’kata kuma bata ta6a ‘kin kwana tare daniba, amma koma miye zan tambayeta inji dalili.

Da wannan tunanin yatasheta sannan ya umarceta dataje tayi sallah, ba musu tatashi cikinagagin bacci tanufi toilet ta d’auro Alwala ta kabbara sallah, shikuma ya wuce massallaci dan gabatar da tashi sallar.

Bayan an idar da sallah jabeer yadawo gida tundaga falo yake jiyo sautin karatun al’qur’anin da Hassana ke rerawa abin ya matu’kar bashi mamaki dan yasan tunda yake da Hussaina bata ta6a yin karatun Qur’anic irin wannan lokacinba, cike da mamaki ya wuce bedroom yahaye gado ya kwanta yana sauraren yanda karatun ke ratsa kwalwarsa cikin zazza’kar muryarta.

Saida tayi da yawa sannan ta tsaya tayi addu’a tashafa inda jabeer yake kwance taje ta zauna nesa dashi cikin ladabi tace “barka da kwana
“Barka dai jabeer yafad’a batare daya d’ago daga kwancen dayakeba.
“Antashi lafiya? Takuma tambayarsa “lafiya lao, ya amsa tare da gyara kwanciyarsa.

Daga nan bata ‘kara maganaba tafito tanufi kitchen domin sama masu abin karyawa.

Love u all my fan’s ???????? shoki ????????
[1/28, 8:12 AM] Zee Elkaseem: ???? AUREN TAGWAYE ????
????????????????????
????????????????
????????????
????????
????
Written & Story by
Zee Elkaseem
{Mmn khady}

Dedicated to All member’s group of Ciwon “ya mace ????????

Page…………………. 32

®TALENTED WRITER’S GROUP (TWG) ????

Gidansu Hassana kuwa Hankalinsu yayi matu’kar tashi ganin ankwana d’aya ba Hassana ba labarinta, Momy tayi kuka harta godema Allah yayinda dady yarasa sukuni ankai report police station sannan daddy da kanasa yaje duk wani babban asibiti dake garin ko Allah zesa yaga Hassana koda kuwa gawartane hankalinsu ya kwanta anma kome kama da ita be ganiba.

Dole ya hakura ya dawo gida ya zauna hankali a tashe yasaka cigiya gidajen redio da television,

Maganar 6atan Hassana ta bud’e ko’ina ‘yan’uwa da abokan arzi’ki sai zuwa suke jaje, Momy Kuwa kuka kawai take idanunta sun kumbura abinci kuwa sai dai tad’an tuttura abinda ya sauwa’ka dan abincinma d’acinsa takeji ga matsanancin ciwon kai dake addabarta.

** ** **

Da misalin ‘karfe takwas ta kammala had’a masu breakfast ta jera kome a dining Sannan ta hau gyaran d’akin duk da bawani datti yayiba ta ‘kara gyarashi ta share sannan ta kunna turaren wuta, a hankali ta tura ‘kofar bedroom d’in wani dad’i taji ganin jabeer baya d’akin saboda haka da sauri tashige tare da maida ‘kofar ra rufe hada sa key. A gaggauce ta gyara d’akin ta goge ko’ina sannan ta feshe da freshener, kayan jikinta ta cire ta d’aura wani ‘karamin towel tafad’a toilet ta she’ka wanka bayan tafito gaban dressing mirror ta tsaya simple makeup’ tayi sannan tanufi wadrope wasu riga da siket na less tasaka, kayan sun masifar fito da ainafin kyawunta dukda ba wata kwalliya tayiba.

Lokacin kuma jabeer yafito cikin shirinsa sanye yake cikin ‘kananun kaya milk d’in riga da ba’kin wando ‘kafarsa sanye da ba’kin takalmi yan kamfanin masaraci, hannunsa ri’ke da jakarsa ta Zuwa office, ajiye jakar yayi kan kujera sannan yanufi d’akin da Hassana take tura ‘kyauren d’akin yayi da mamakinsa sai yajishi gar’kame da key, saboda haka nocking yayi sannan yanufi dining ya zauna yana jiran fitowarta dan bayaso ya makara office dan yanzu ayyuka duk sun dawo hannunsa saboda daddy baya fita office saboda 6atan Hassana

Saida gabanta yayi ‘yar’karamar fad’uwa lokacin da jabeer yata6a kyauren d’akin.

Jiki a sanyaye ta bud’e tafito kan dining ta hangeshi saboda haka can tanufa tana takunta cikin nutsuwa, idanuwa jabeer ya ‘kuramata ko ‘kiftawa beyi wata matsananciyar sha’awarta ke fizgarshi dan jabeer irin mutanannane masu ‘karfin sha’awa dan baze iya kwana biyu batare daya kusanci matarshiba kuma itama ta sabamai da hakan dan kobe nemetaba take kai kanta gareshi shikuma bewuce tayi. lol

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button