BABU SO HAUSA NOVEL

AUREN TAGWAYE HAUSA NOVEL

Tashi Hafiz yayi yabi bayanta, Hassana na kallo amma bata kawo kome a rantaba, iatadai fatanta kawai idan Hussaina tagama wayar datadawo sutafi gida.

Love u all my Fan’s ???????? shoki ????????
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: ???? AUREN TAGWAYE ????
????????????????????
????????????????
????????????
????????
????
Written & Story by
Zee Elkaseem
{Mmn khady}

Dedicated to All member’s group of Ciwon ya mace ????????

Page————————-3

Bud’e motar Hafiz yayi gidan baya suka shiga, kasancewar motar tanada ba’kin glass bazeba wanda ke waje damar ganin nacikiba dukda dama gurin akwai duhun dare,

Ac Hafiz ya kunna musu, take motar tad’au sanyi tare da wani daddad’an ‘kamshi
Zaune suke gaf da juna har jikinsu na had’uwa dana junansu, Hafiz ne yafara magana cikin kwarewa da gogewa na yan duniya “Babyna ammafa kin had’u kinganki kuwa kamar matan hurul’ayni, wani ‘kawataccen murmushi Hussaina tayi tare dasa hannunta tarufe fuskarta, duba Hafiz yakai kan shantala-shantalan yatsun hannunta wanda yake d’auke da awarwaraye da wani had’adden zobe na azurfa, hannu yasa Yakama hannun nata yamatse a hannunsa, sannan yafara wasa da zoben “kai amma ring d’innan yayimin kyau babyna, amma set ne tare da sarkarki koh?
Yafad’a tare dakai hannunsa kan wuyanta yana wasa da sarkarta, lokacin yagama kashema Hussaina jiki yanda yake shafar wuyanta, ko magana bata iyawa sai maida numfashi datake d’aya d’aya, hakan yabashi damar yin ‘kasa da hannunsa zuwa cikin rigarta yafara wasa da breast d’inta, wani irin yarrrr taji ajikinta, saboda ba’kon Al’amarin daya risketa yau, domin Hafiz shine mutum na farko daya fara yimata irin wannan wasan, suna soyayya da Jabeer amma koda wasa beta6a kai hannunsa kan jikintaba, “hakan yana nufin jabeer be iya soyayyabane ko miye….

Tana cikin wannan tunanin taji Hafiz ya rungomota yahad’ata da jikishi, yana rad’amata kalmar “I love you a kunnenta, cikin kasalalliyar murya tace “mee too my Dear,
“Wow nice my Baby, Hafiz yafad’a tare da had’e bakinsa da nata yacigaba da kissing d’inta.

Dare yafara Hankalin Hassana ya masifar tashi dan tanemi Hussaina ko’ina a cikin hall d’in da wajen hall d’in amma bata gantaba, duk tabi tarud’e, gashi Zuby tunda tashiga fagen rawa batako wai-waiyesuba barantana ta tambayeta kotasan inda Hussainar take gashi tatafimata da waya barantana takirata.
Komawa tayi kan kujera ta zauna tayi tagumi hannu bibbiyu,

Can Hankalin Zuby yayo kan inda tabarsu Hussaina amma batagansuba sai Hassana wacce tahad’a hannuwa biyu ta tallabe kumatunta kwalla suncika idanunta, da sauri zuby takaraso inda take “Ke ina ‘yar’uwarki? Hassana batajitaba dan tayi nisa cikin tunanin irin hukuncin da daddy ze yanke masu idan yadawo ya tarar da basunan, batakaran suba ranar momynsuma bazata fitaba dan dady mutumne me zafi tsaye yake kan tarbiyar iyalanshi.

Ta6ota zuby tayi “tambayarki nake ina Hussaina?
Sai lokacin tadawo daga tunanin datake “nima wlh ita nake nema dan Allah ki kiramin ita da wayarki danni tatafi da tawa wayar.
“To ina Hafiz? Zuby ta’kara jeho mata wannan tamabayar
“Kinga ni dukansu bansan inda sukeba, nidai dan Allah ki taimaka ki kiramin Hussaina mutafi gida.

Take zuciyar Zuby tabata akwai wata kulalliya tsakanin Hafiz da Hussaina, idan kau hakane lallai Hussaina tad’auko ruwan dafa kanta.

Wayarta ta fiddo daga cikin poss tafara lalubar number Hussaina, kusan kira takwas zuby tayima Hussaina no answer, hakan ba ‘karamin ‘kular da ita yayiba, batako kalli Hassanaba tabar gurin tana cika tana batsewa.

Ganin dare na’karyi yasa Hassana tambayar wata budurwa kusa da ita “dan Allah ‘karfe nawa?
Duba wayar tayi “karfe tara da Monti takwas tabata amsa a ta’kaice.

Cike da rud’ewa Hassana tatashi tafita harabar hotel d’in Allah ya taimaketa lokacin wani me napep ya sauke wasu, tagayamshi inda ze kaita, saida suka d’au hanya tafara tunanin inda ‘yar’uwar tata tashiga “Toni yanzu mezanfad’ama Momy idan aka tambayeni Hussaina, wasu hawaye suka gangaro kan kumatunta.
“Allah sa dai tana lafiya duk inda take.
Tana cikin wannan tunanin har suka iso ‘kofar gidansu batamasan sunzoba saida me napep yace “hajiya mun isofa sannan ta sallameshi tafita daga napep d’in.

Jiki a sanyaye tanufi gidansu, ahankali ta kwankwasa megadi yabud’emata bayan yatambayeta tagayamashi itace.

Ahankali tashiga gidan da sallama Momy tagani zaune tayi tagumi koba tambaya tasan jiran dawowarsu takeyi, ganin Hassana yasa Momy sauke wata ajiyar zuciya, “Alhmdlh ina ‘yar’uwar taki take?

Hawaye yacigaba da zuba daga idon Hassana batare databa Momy amsar tambayar datayimataba, cikin tashin hankali Momy ta’karaso inda Hassana take takama kafad’unta “ina take nace? Ko wani abu ya sameta? Kifad’amin……

Ganin hankalin Momy yatashi yasa Hassana goge hawayenta “bawani abu yasametaba kawai na nemeta bangantaba, kuma gashi dare yayi…

“Subhannallah Momy tafad’a Allah sa dai lafiya, kin kira wayarta? “Nima wayata tana hannunta.

Hankali tashe Momy tasa wayarta takira Hussaina itama no answer aka gayamata kamar yanda duk wanda yakira ake gayamai, saida tayi kira kusan na goma sannan Hussaina ta d’auka cikin kasalalliyar murya tafara magana dan lokacin tana jikin Hafiz yagama rabata da rigarta yana ‘ko’karin ciremata breziya,

Cikin fad’a Momy tace “dan Ubanki kiyi maza ki dawo gidan tun kafin dadynku yadawo, batajira me Hussaina zatafad’aba Momy takashe wayar

Lokacin sukajiyo horn d’in motar Alamar dawowar me gidan, cikin tsananin tashin hankali Hassana tafara magana “Momy dadyne yadawo nashiga ukku tafad’a tana yarfe hannu.

Da sauri Momy tace “maza ki shige d’akinku kada yazo yaga batanan, Dan batakaran itadayi laifinba mu kanmu sai rayukanmu sun 6aci.

Da sauri Hassana tashige d’aki, zama tayi bakin gado tayi tagumi hannu bibbiyu tana tunanin ‘yar’uwarta.

Love u all my Fan’s ???????? shoki ????????
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: ???? AUREN TAGWAYE ????
????????????????????
????????????????
????????????
????????
????
Written & Story by
Zee Elkaseem
{Mmn khady}

Dedicated to All member’s group of Ciwon ya mace ????????

Page————————-5

Jitayi an sha’kota ta baya a firgice ta juyo, ido biyu sukayi da daddy beyi wata-wataba yafara zabga mata cable wayar dake hannunsa nan tafasa ‘kara tana ihu, amma daddy be sauraramataba, tsulamata wayar yakeyi iya ‘karfinshi, mommy da Hassana suna daga falo sukajiyo ihunta, wani sabon kuka ya kwacema Hassana cewa take “Momy dan Allah ki taimaki Hussaina kiba daddy ha’kuri kada yajimata ciwo, kallonta Momy tayi cikin nuna rashin halin damuwa tace “koma miye ita tajama kanta ‘kara yadaketa gobe bazata ‘karaba.

Da gudu tashigo falon kamar wacce aka jeho, bayan Momy tanufa tana kuka ta ‘kan’kameta “wayyo Momy dan Allah ki taimakeni wlh bazan ‘karaba,
6an6areta Momy tayi daga jikinta tare da barin gurin tana cewa “lokacin dakikayi rashin jin naki kinyi shawara dani, dan haka kada ki nemi taimakona can ki ‘karata jiki magayi, shigewarta tayi d’aki ta maida ‘kofarta tarufe, wani irin kuka Hassana tafashe dashi ganin momy batada niyyar baiwa dady ha’kuri shikuma beda niyyar hakura, rugowa tayi tari’ke hannun daddy tanamashi magiya “dan Allah daddy kayimata ha’kuri bazata ‘karaba, a harzu’ke daddy ya hankad’ar da Hassana gefe guda yacigaba da suburbud’ar Hussaina, suduka suke kuka suna bashi ha’kuri amma beko sauraresuba saida ya tabbatar Hussaina ta daku sannan ya rabu da ita yanufi d’akinshi yana huci yana cewa “gobema ki kara tafiya ki wuce magrib baki dawo gidaba wannan kad’an nayima shashasha kawai.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button