BABU SO HAUSA NOVEL

AUREN TAGWAYE HAUSA NOVEL

Dare ya tsala misalin ‘karfe biyu na dare motar yan’sandan tayi parking bakin get din gidansu Hussaina, nocking sukayi lokacin mal bala yana kwance cikin d’an karamin d’akinsa yafito da sandarsa a hannu yana tamabayar “waye? Hussainace tayi magana “nice mal bala, “kece wah? Ya tambaya.
“Nice Hussaina.
“Husssaina da wannan daren subhanallah bud’e ‘kofar yayi ahankali yana le’kowa yayi ido hud’u da ita da ‘yansanda biyu tare da ita.

Da Sauri Hussaina tashiga gidan ‘yansandan suka take mata baya, a harabar gidan suka tsaya “kishiga kiyimana magana da mahaifin naki.
Bata ko sauraresuba tayi cikin gidan da gudu,
Lokacin Daddy,Momy da Hussaina suna Zaune a falo, Momy sai Addu’a take Allah maidomata da ‘ya lafiya a Zuciyarta tana cewa “danasan haka zata kasance daban amince da fitartaba.
Hassana kuwa kuka kawai takeyi, yayinda dady Zuciyarsa tagama ‘konewa jiyake inama yaga Hussaina yanzu Allah kad’ai yasan irin dukan dazeyimata.

Begama wannan tunaninba yaga anturo ‘kofar falon, mikewa yayi da sauri dan ganin me shigo masu gida da wannan tsohon daren, ido Hudu sukayi da Hussaina saurin isa yayi Inda take a zuciye ya dun’kule hannu yakaimata wani mugun naushi sannan yasa ‘kafa ya hard’ota.
Fad’uwa tayi ‘kasa tana maida numfashi sama-sama ko kukanma yakasa zuwamata saboda tsananin azabar datake ciki.

Dukda haka Daddy beyi ‘kasa a gwiwaba gurin ciro cherger wata fitila dake jikin soket yarin’ka tsulamata, sai lokacin tasamu damar fasa ihu tare da d’aukewar numfashinta ta sulale ‘kasa sumammiya.

Ganin tafad’i yasa Momy ‘karasowa gurin tana kuka “innalillahi Alhj miye haka kake shirin kasheta, kabari mana kaji ta bakinta, “Bazanbariba da bata fitaba da hakan be faruba, kuma ko mutuwa tayi bani nadamar kasheta saboda da inyi mugun gani ‘kara narasata baki d’aya.

Hassana kuwa ganin ‘yar’uwarta kwance ba Alamar rai tattare da ita yasata rud’ewa tafito zuwa harabar gidan dagudu tana kuka, ganinta yasa ‘yansanda sukayi saurin tarbarta a tunaninsu Hussainace saida suka kula da kayan jikin wannan basubane jikin wacce suka kawo yanzu “ke lafiya suka shiga tambayarta, a gigice take nunamasu cikin gidan tana cewa “daddy yakasheta, ya kashemin ‘yar’uwa.
“What suka fad’a tare da abkawa cikin gidan baki d’ayansu..

Love u all my Fan’s ???????? shoki ????????
[1/2, 7:21 AM] Zee Elkaseem: ???? AUREN TAGWAYE ????
????????????????????
????????????????
????????????
????????
????
Written & Story by
Zee Elkaseem
{Mmn khady}

Dedicated to All member’s group of Ciwon ya mace ????????

Page————————-14

A gigice Momy tabi Hassana da kallo tare da ‘yan’sandan dake tare da ita.
“Hassana Kina Haukane, mahaifin naki kika kirama ‘yan sandan.
Cikin muryar kuka Hassana tace “Wlh momy bani nakirasuba ina fita nagansu a harabar gidannan.

Kallonsu daddy yayi a gadarance yace “waya kawoku gidana, kuma da izinin wah kuka shigo har nan? Yafad’a yana nuna inda suke tsai-tsaye.

“Babban cikinsune yayi magana “Sunana inspeter Sabi’u wale, mune wad’anda suka kawo wannan yarinyar gidannan bayan mun tsinceta cikin halin maye, bayan ta dawo hayyacinta mukayimata ‘yan tambayoyi shine tasanar damu kaine mahaifinta shine muka kawota, muna tsaye a haraba munajiran tayimana magana dakai shine mukaga wannna tafito tana fad’in a taimaketa ankashemata ‘yar’uwa shine dalilin dayasa muka shigo domin gudanar da aikinmu kamar yanda doka ta tanada.

“Owj naji duka bayaninku nagode, inaso kutafi kawai ni zan iya solving kowace matsala tagidana batare da wani yasamin hannuba nagode da taimakon dakukayima ‘yata.

“Muma mungode Alhj Amma dan Allah ari’ka kai zuciya nesa, saboda gudun danasani….
Sai a hanzarta a kaita asibiti suka fad’a suna kallon Hussaina dake kwance bako motsi.

Bayan fitar ‘yansandan momy ta kalle daddy Wanda yaketa mazurai da Alama har ‘yanzu zuciyarsa bata gama hucewaba,

Hussaina kuwa har ‘yanzu tana kwance batasan inda kanta yakeba, momyce tamatso inda take ta tallabo kanta ganin ba alamar rai tattare da ita yasata fashewa da kuka, “Dan Allah Ahj mukaita asibiti kada tamutu…..

“Tamutun mana, yafad’a cikin d’aga murya.
Sannan yayi ‘kasa da muryarshi yana cewa “ba inda zan kaita na kwammace inrasata baki d’aya da mugun halin datake Neman jefa kanta.
Tajamani abin fad’i a gari, yana gama fad’in haka yashige d’akinshi ya maido ‘kofa yarufe.

Cikin kuka Momy ta kalli Hassana tace kawomani ruwa.
Da sauri Hassana ta d’ebo ruwa cikin cup takawo, amsa Momy tayi tashiga kwarama Hussaina a jiki amma ko motsi batayiba saida ta zubamata a fuska sannan tayi firgigi ta tashi ta ‘kan’kame Momy tana fad’in dan Allah kibashi ha’kuri wlh bazan ‘karaba.

“Ke Hussaina kitsaya mana, ki nutsu nace ba daddynku bane nice Momy
‘Kara ‘kan’kameta tayi tana fad’in “wayyo Momy wlh bazan ‘karaba kigayamashi na tuba.

“Cikin tsawa Momy tace “dallah ni sakeni tare da tureta daga jikinta, kinsan kina tsoro kikaje yawon har kika kai wannan lokacin baki dawoba, itama tana gama fad’in haka tayi tafiyarta d’akinta tabar Hussaina nan tana kuka itada Hassana.

Hassanace tamatso kusada ita takama Hannunta ta mi’kar da ita tsaye suka nufi d’akinsu.
Koda suka shiga d”akin zaune sukayi jugum-jugum suduka suna sharar kwallah.

Ita Hassana tana kukan halinda ‘yansandan nan suka fad’i sunkama Hussaina na maye.

Itakuma Hussaina tana kukan yaudara da Hafiz yayimata har yayi nasarar rabata da budurcinta.
Wasu sabbin hawaye suka zubo a kuncinta.

Hassana ta kalleta tare dasa hannunta ta sharemata hawaye
“Dan Allah ‘yar’uwata naro’keki ki gayamin gaskiyar inda kikaje har kikakai wannan lokacin baki dawo gidaba, kuma da gaskene abinda ‘yansandan nan suka fad’i na kamaki dasukayi cikin halin maye?

Tana gama fad’in haka ta tsareta da idanu tana jiran jin amsar dazatabata “Hmm ko d’aya Hassana wlh bansha komeba, kuma ni ba inda naje nasan dai naje asibiti kamar yanda na tambayi momy zanje kuma ta amincemin, ana gaf da magariba nabaro asibitin ina tsaye inajiran abin hawa wani me mota yatsaya gabana yaro’keni da inshiga yaragemin hanya nikuma ganin ina sauri yasa na Amince nashiga motar to shinefa daganan ban ‘kara sanin abinda yafaruba saida na tsinci kaina yashe a titi, wannan shine gaskiyar abinda yafaru.

Hassana najin haka ta ‘kara fashewa da kuka tare da rungume ‘yar’uwarta tana fad’in “sister Allah yasa da rabon sauran shan ruwanki a duniya, ya Allah na godema daka kwatomin ‘yar’uwata daga hannun muyagun mutane.

Hussaina kuwa dad’i taji har cikin ranta dan ganin Hassana ta yarda da ‘karyar data tsaramata, a zuciyartama cewa tayi aiko gobe idan daddy da Momy sun tuhumeni abinda zan fad’amasu kenan, da haka suka kwanta bacci yayi awon gaba dasu kowace da tunani barkatai a zuciyarta.

      *Washe Gari.*

Koda suka tashi bayan sunyi duk abinda yadace na gyaran gida, komawa sukayi d’aki sukayi wanka wasu dogayen riguna suka sanya masu kyan gaske tare da ‘yan ‘kananan hijab.

Lokacin Momy tagama had’a break fast zuna zaune kan dining tana zubama daddy kasancewar tara hartayi yana sauri yafita office saboda yanada ayyuka da dama a can.

Jerawa sukayi gwanin ban sha’awa suka nufi inda iyayen nasu suke sannan suka zazzuna bayan sun gaishe da iyayen nasu.
Hussaina sai sunne kai takeyi alamar rashin gaskiya.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button