BIBIYATA AKEYI COMPLETE HAUSA NOVEL
BIBIYATA AKEYI COMPLETE HAUSA NOVEL

Juyawa tayi da niyyar daukan jakarta dan nunawa hameeda tsarabar da anty tabayar abata,"
Karaf!!" idanuwanta yasauka akan mama wanda da alamu tadade awajan. "
Kallon tuhuma take binsu dashi,”
Lokaci daya idanuwansu yayi zuru-zuru alamun rashin gaskiya ya bayyana tattare dasuu”
Shigowa tayi tazauna ta fuskancesu,”
Mekuke zance akai?? ” ta tambayesu, mutsu- mutsu sukafarayi alamun basasan fadin abinda aka tambayesu” shiru sukayi nadan lokaci sannan tace” ba daku nakeyiba ne??”
Mama daga najeeb ne “nan takwashe duka yanda sukayi dashi tafada musu,”
Shiru mama tayi sannan tace Allah yakyauta " muci gaba da addu'a, tabbas wannan jarabawa ce ta ubangiji Allah yabamu ikon cinyeta"
Su duka suka amsa da ameen. "
Sannan mama tatahi tafuta” bayan tafita ne tajuyo ta kalli kofar dakin,”
Bawai bata yarda da abinda tafad’a ba” amma tanada tabbacin ba zancen da sukeyi ba kenann,”
Hasalima tun shigowar ta tabiyota ganin tashigo ahargitse ko lura da Ita datake zaune afalo batayiba, haknne yasa tabiyota danjin maiyafaru? Zancen da dataji ne yadau hankalinta yasa taki shiga. "
Tadaura niyyar bazata gwada mata tajiba amma zata tsananta addu'a, kan Allah yakare mata d'iyarta daga kowani irin sharri."
Ganin mama tafita yasa ta sauke ajiyan zuciya, hameeda ne takalleta sannan tace" sis bakya Kallon yakamata mufadawa mama?"
Um Um ba yanzu ba dan kokadan banasan tashin hankalinta “
Ok amma ki Kara kiyayewa, in sha Allah"
Tashi sukayi suka nufi falo."
Hameeda ce tace” mama kin kira momynsu amiran?? Nakirata amma kushirya kuje kukara tambayar ta da kanku. “
Cikin sauri suka shirya suka nufi gidansu amiran.”
Dakyar momy ta amince data barta tazo amma sai satin bikin.”
Haka suka nufi gida bayaan da sukaso ba, dan sunso abarsu sutafi da Ita tare, “
================
MG ne zaune afalonsa wayane sakale a kunnensa, kana Kallon sa za’a hango bacin rai karara a fuskarsa, ji nayi yana cewa” Mekuke nufi da hakan kenan??”
Cikin karaji naji yakuma cewa!!”
Captain bala!!
Karka yarda Irin haka takara faruwa??”
Cikin rawar murya wanda ake waya dashi naji ya amsa da” yess sir,” tsaki yaja ya kashe wayar, hadeda cillata a daya kujerar,
Ya kishin gid’a a jikin kujerar hadeda lumshe ido, jiyayi an tabashi, a hankali ya bude idon yasaukesu akan Abubakar amininsa, tashi yayi ya zauna, sannan shima yasamu waje ya zauna.”
Abubakar ne yakara cewa" Wato dabazaka dawo aurena ba kenan ko mai kake nufi?? "
Eh!!” yanzun ma dan antakuarni ne da sai lokacin yacika, “
Dakuwa anga dan iskan aminin ango” Abubakar yace”
Kaikasan dan kai nayita jawa iyayen yarunyar nan rai. “
To ai gani nadawo, haka sukayita shirye shiryen yanda zasu tsara bikin Abubakar dan gidan waziri wanda za’ayi satin sama,
===+============
Amma ce gaban malam nakaranki hankali tashe
Kuyi hakuri da jina shiru kwana biyu sai jiya nadawo amma in sha Allah yanzu kullum zaku ringa ganina
To be continued
Ur’s
Z33yyb3rw3r
BIBIYATA AKEYI
_
Bismillahirahmanirrahim
_
Writting by
© zaynab bawa
( z33yyb3rw3r )
Page 26
*
Washe gari da sassafe, Ammah tashirya da niyyar zuwa gidan malam,
Bayan ta shirya tafito, tawuce gidan kawarta hajiya larai, wanda duk wani tuggu da muggan abubuwa Ita take koya mata, “
Bayanin duk wani abinda taji jiya tamata, sannan takara da cewa, hajiya konawa zankashe arabata dashi," natabbata ba karamin mutum bane dan kinsan abinda malam yafada, har inde nayi sake asirin ya karye, toh mijin da zata aura samunsa nawuya, "
Gaskiya bazan iya ganin zuwan wannan rana ba, wallahy yanda natsani uwarta haka natsaneta, intakaice miki hannafi tsanarta fiyeda uwarta,”
Wata yar shewa hajiya larai tasa, haba kekuwa hajiya banfa sanki da sarewa haka ba, duk kin wani bi kin rikice akan yarinya karama, “
Ammah ne tace bazaki gane ba ne hajiya, har wani lokaci nadaban fa babansu yake ware mata wai najin damuwowinta, komu matansa bamu samu wannan lokacin ba,"
Wallahy tun lokacin da aka haifeta dana fahimci Irin son da yake mata nakejin tsanar yarinyar. "
Kedai yanzu ki kwantar da hankalinki, halin malam saidai kifadawa wani dan shekara da shekaru yana miki aiki, baki taba Kallon ba dai-dai ba dan haka yanxu barina shirya saimu wuce,”
Aitsabar tashin hankali kanmuje har na kirashi, mukawai yake jira,”
Sai bayan tagama shirinta sannan tafito, a motar hajiya larai, suka shiga suka nufii kauyen,”
Banisa ne dashi sosai ba, idan aka d’an futa agari yake,
Bayan isarsu ne kaitsaya gidan malam suka nufa,”
Dama ya dade yana jiran zuwan su,”
Bayan sun shiga ne amma ta gama koro masa bayanai, “
Shiru yayi nadan wani lokaci sannan yace, tabbas akwai wanda ke nemanata,” kicin kidima Ammah tace malam arabasu, dan yadda uwarta ta kuntata min na auren mijina itama saina kuntata mata na ganin yarta agaban ta ba aure har abada, “
Shiru yayi sannan yace, hakan mai yiwuwa ne amma dole sai mun dakatar dasu da yawan addu’o in da sukayi, kullum Cikin addu’a suke bbu rana bbu dare,
Budar bakin hajiya larai sai cewa tayi alagafarta malama akaashesu kawai itada saurayin, nikuwa araina nace wannan katon bokan basajin kunyan kiransa da malam shikuma yayita yake baki yana amsawa."
Ammah ne tayi saurin katseta, A’ah” baza’a kaahesu ba, idan nakasheta aiban cusawa uwarta bakin Ciki ba, tazauna arayende uwarta taci gaba da ganin bakin Ciki, shikuma idanna kasheshi ai ban cusa musu bakin cikiba, gwamma suganshi araye amma yaki, auranta. “
Kinga daganan na bata mata suna nace ya lalata tane yaki auranta, hajiya larai ce tayi saurin karbewa yanzunma waya sani tunda kince binsa takeyi wajan sa, shi bai taba zuwa ba."
Cikin gamsuwa da shawarar su malam yace” yanzu mufara raba tsakaninsu kafin muzo zuwa wannan stage din, “
Wani dan magani yabata yace ta zuba masu a abinci, idan ta zuba kasala data sauka musu bbu mai iya tashi nafila acikinsu, acikn wannan daren yakeson yin aikin.”
Kar6a sukayi Cikin murna da ganin kaman burinsu yacika, suka zube masa kudi, suka koma gida,
Direct gida tasauke ta, sannan itama tawuce nata gidan, "
Tana zuwa kuwa tasamu inna kaltu tad'auura miyar dare,"
Ko dar bata jiba ta aiki inna kaltu kasuwa, sannan tashiga tajuye, tarage kadan dan ta tabbata ba lallai su *hanna* da hameeda suci abincin darenba, dan saudayawa tana kallo da daddare abincinsu daban sukeyi,
Bata damu da duk wanda zaici abincin ba, tajuye aduka, itadai bazata bari 'ya'yan ta suci ba, "
Yamma likis yaya jalal ya iso, zuwa gobe da safe dasu wuce, da dddare bayan anzubo mishi abinci, ya kalli hanna da hameeda dasuke zaune, ku sauko muci abinci yace tareda kawar da idanunsa daga garesu hanna ta yatsine fuska yaya na koshi nikam,
Wani kallo daya wulla mata, aitabaaan lokacin data sauko ba tasa hannu a abuncin, hameeda batajira anmata nata Kallon ba, tayi saurin sakkowa,” Wani Irin dadi abincin ya musu wanda su kansu basusan dalilin hakan ba, kuma bawai abincin yawani hadu bane, amma ku masu karatu basai nafada muku abinda ke Ciki ba????. “
Sanda suka cinye abincin tass sannan hameeda, takwashe kanukan zuwa kicin, hanna uwarsan jiki kuwa tayi d'ai-d'ai."
Basu dade da cin abincinba suka kwanta, bacci sosai sukayi, adaran boka yafara aikinsa."
================
Wani mutumi magani gaban likita hankali tashe, da police guda biyu acikin office din. “
Magana naji yafarayi yana cewa” tayaya za’ace ba’asamu Wani dalilin da zai nuna shaidan wanda sukayi hakanba, jinayi kamar nasan muryan nan amma a’ina? ???? masu karatu kubiyoni dan musamo amsa amma nima nakasa tunawa police dinne yafara magana sir” duk wani bincike munyi yanuna mana ba accident yayi ba bigeshi akayi, dan munsami mashin power bike dinsa akasa bbu alamun kokewar Wani abu ajiki, gakiya i _ asaured u that wannan dasa hannu aciki munakan inveatigeting duk wani mai hannu zaisamu punishment mai tsaurin gaske. “
Yaja Wani deep breath sannan ya kalli doctor, doctor” please yaushe zai farfado??? “
_Sooner_ in sha Allah inji _doctor_ ,yar buguwa ce _and then_ ya razana _so_zuwa nan da _few hour's_ zai iya farfadowa, fita yayi zuwa dakin da aka kwantar da yaron, sosai ransa yake bace, dan ya tabbata duk mai hannu sayya kasheshi,
Cikin yan minute’s yakira shugaba police ya shaida musu akan su duba CCTV camera dake layin sukawo masa result Cikin hour’s suka gama hada komai suka kawo masa abinda yafaru alayin a wancen ranan.”
===============
Sai wajan 6:30 iyalan gidan alh muhammad suka tashi dawata Irin kasala, dakyar sukeyi sallah, kowa mamakin Irin wannan bacci yakeyi, dakyar su *hanna* suka samu suka fara shiri dan dawuri zasu wuce kano. "
===============
MG ne zaune shida Abubakar a farfarjiyan sha shunsa , sojoji sai shawagi sukeyi,
MG ne yakara magana _in angry tonge_ , Wani Irin banzan zancen wannan har sai mun jira _sister's_ kafun a shirya yanda za'ayi _event_ din, haba *yareemah* sunkussan zuwa dan yanzu inada tabbacin tasowarsa, mtswww Yaja tsaki tareda _hot n sexy eyes_ dinsa bai Kara cewa komaiba, dan
A rayuwar sa, he hates acewai umarnin wasu zaibi, wayarsa ce tafara ringing ganin kiran daga captain bala ne yasashi yin picking abinda yadada masa ne yasa shi saurin mikewa zaune yarasa farinciki zaiyi ko akasin hakan,
Gabansa ne yahau dukan uku-uku.”
To be continued
Ur’s
Z33yyb3rw3r
BIBIYATA AKEYI
_
Bismillahirahmanirrahim
_
Writting by
© zaynab bawa
( z33yyb3rw3r )
Banida bakin yimuku godiya gaskiya naji dadin yanda kukeson littafinnan, da masu bina ta prvt nima inasonku kamar yadda kuke sona luv u all My fans
Page 27
- Karfe tara na safiya suka dauki hanyar kano, hanna da hameeda na baya sai saleem dake gaba, a mazaunin mai zaman banza, yaya jalal kuma yana tuki, sosai sukejin dadin tafiyar dan ya jalal Allah yayishi mutum mai saukin kai, dajan kannensa ajiki, ============== Gabaki daya yarasa dadi zaiji ko kuma akasin haka shi kansa ya kasa ganewa.” Shi kansa zaiso haduwar su amma da d’an sauran lokaci, ” Juyawa yayi ga abubakar,” MG ne yace waishin amaryar tamu kam asalinta yar inace?? Kallon mamaki abubakar yabishi dashi, “dan a’iya saninsa yareema bai iya tambaya ba, kuma koda waya sukeyi idan yabashi su gaisa baya kar6a saidai yace agaidata.” Ganin Irin Kallon dayake binsa da shine yasashi murtuke fuska, wanda shi kanshi abubakar sanda yasha jinin jikinsa.” Asalinsu yan bauchin yakubu ne yanxu amma suna zaune a kano tadabo, saidai wan mahaifinta nacan bauchin, i knew it yafada acikin zuciyarsa, amma afili tabe baki yayi, kamar wanda bashi yatambaya ba, akabashi amsa ba, amma Cikin ransa so yake ya tambayi sunan babanta, dan Kara tabbatarwa, amma bayason raini, hakanne yasa yaja yamatse. ” Tashi yayi yashigo daki, kan lallausan bed dinsa yafada yana tunani, afili ya furta, i knw now she’s big and matured enough
Wani Irin kasaitaccen murmushi yayi hadeda shafa gashin kansa.” Haka kawai ya tsinci kansa dason ganin ta, he wats to see her , koda ace batasan koshi wayeba, amma saiiya ganta.” Nougty girl yafada hade dayin wani kasaitaccen murmushin.” Sosai yashigo niahadi aranar wanda duk wanda ya kalleshi saiya yi noticing yana Cikin good mood =============== Sir gashi munkawo, record na CCTV camera, umurtan daya daga Cikin guard dinshi yayi, kan yamasa playing , adan kankanin lokaci ya yi connecting komai yafarayi. ” Dai-dai wajanda take tsaye atsakiyar titi, yafara, dan camera tabaci daga dai-dai wajan tafara, dan basuga daga Ina tafuto ba, har wajan da dannasa yaso kadeta aka yi hitting dinsa.” Ganin hakan yasa suka dasa aransu cewa, anyaudareshi da mace ne suka aikata masa hakan. ” Har za’a kashe, yayi saurin dakatar dasu, mai nake Gani kamar wandan soldier ajiknsa??” Zooming akayi aikuwa kaki yafuto baro-baro a jinsa wandon kaki ne sai rigan t-shirt. ” Dayan police dinne yace, Sir wannan ba kakinmu bane dan soldier’s dinmu Basa amfani da Irin wannan, bincike akafarayi na sojoji masu amfani da kakin.” Cikin dan kankanin lokaci akasamo kuwa, cikin ladabi yace Sir, tawagar soldier’s din MG Abdullahi abdulaaziz lamido ne kawai suke amfani dashi, Cikin firgita ya buga bench din gabansa, i knew it nasani” nasani” nasan wannan hatsabibin yaron bazai barni hakaba, amma this tym i will make sure that i teach him an unforgetable lessons you will regret treating me sai kayi danasani yafada Cikin karajii. “
================
Tunda suka dauki hanya *hanna* tayi noticing ana binsu abaya, kuma tabbas tasan motar wannan mutanenne."
Kusan 11 :30 tamusu a birnin kudu," inda suka tsaya a gidan kaninsu umma wanda yake zaune a birnin kudu, " sun tsaya domin akwai aikar" da zasu karba suwuce da itah."
Sosai suka samu tarba dayake ansan da zuwansu, abinci kala-kala akamusu, hadda snacks, da drinks da ruwan faro. "
Matan kawu abdul nada kirki Sosai, haka tayita jansu da tadi kamar kannen ta, duk da hanna bawani saninta tayiba amma matar tashiga ranta Sosai,
Da yaranta guda biyu, Kareem da bazai wuce d’an shekara takwas ba sai k’anwarsa khadija anace mata (nana) sunan umma akasa mata.”
Sun fara cin abinci inda ya jalal Da saleem Da kawu abdul suna babban falo. "
Sai hanna Da hameeda Da maman nana suna falonta, hanna bataci wani abinci Sosai ba gabaki d’aya tausayin mutanen wajan nanne ya lullu6eta.”
A yanda taga alamunsu tasan tafiyar bawai sunyita acikin shiri bane Tunda basusan niba, kawai binta sukeyi ko’inah.”
Kuma ayanzu haka ta nada tabbacin bawai sunci abinci bane, suna nan aqark'ame (arufe) a mota kamar wasu kaji. "
Ganin maman khadija da hameeda sunmike dan zuwa yin sallah ne wani tunani yafado mata,”
K'ara gyara zamanta tayi dake itah tana fashin sallah. "
Sanda ta tabbatar sunyi ciki sannan ta ebi faro biyu Da sugar drinks sannan tajuya snacks a leda hadeda, naman kajin Da aka soya musu duk ta eba ta zuba a leda na sweet home tayi hanyar waje da sand'a kamar wata marar gaskiya, (nikuwa araina nace ai marar gaskiyar ce) "
================
Karfe goma yayiwa, ammmah Da hajiya larai a gidan malam, danjin sakamokon aiki.”
Malam ne yafara magana, aiki dai amfara amma haryanzu ba'a karasaba, dan basu kadai sukeyin wannna addu'ar ba, dan haka yanzu saimunbi duk maihanu aciki mun tura masa aljanun Da zasu sasu kasala, shima kuma wannna aiki nadaukan lokaci dan, saimunyi yarjejeniya Da aljanun,"
Yanzu haka ina bukatar kudi masu yawa dan gudanar Da aikin,.
Hajiya larai ce tayi saurin cewa kaman nawa malam?? "
Zaku iya kawo dubu dari dan wannna ba karanim aiki bane."
Zufa ne tafara ketowa ammmah dan batada hanyar Da zata samu makudan kudinnan. "
Cikin rawar murya tace malam anama sassauci mana."
Ai iya yanda za’a bukata a aikin kenan. “
Haka su amma suka tashi suka tafi jiki babu kwari,”
Acikin motane hajiyaa larai ke ce mata, kiyi yanda zakiyi anemi kudinnan, ko k’adararki kisayar inyaso na ciki miki sauran, ai matsalarki tawace. “
Ahaka ranta yadan samu ya sanyaya, subhanallah wai akan cutar Da dan uwanka sai salwantar Da duk abinda ka mallaka dan kuntatawa wani, wa'iya zubillah Allah yakaremu."
Ahaka suka tsayar da zance bayn sun sqyar sukoma gidan malam. "
To be continued
Ur’s
Z33yyb3rw3r
BIBIYATA AKEYI
_
Bismillahirahmanirrahim
_
Writting by
© zaynab bawa
( z33yyb3rw3r )
Maman manal Wannan baby na wahalar damu dayawa ????Allah dai ya futo dashi lpy, saura kuma kice na miki terere ????????????