BIBIYATA AKEYI COMPLETE HAUSA NOVEL
BIBIYATA AKEYI COMPLETE HAUSA NOVEL

Wajen su hanna kuwa yau kwanansu biyu da zuwa garin kano, duk yadda za’ayi event abubakar yazo sungama shiryawa biki sai k’aratowa yakeyi.”
Suna daki *hanna* na kokarin saka kaya yayinda hameeda ke zaune akan chair na dressing mirror sai kwalliya takeyi. "
Shiri sukeyi dan zuwa wajen kai dinku nan su,
Hanna Sis wai me yasa ya jalal baya fitowa ne kwana biyunna, ta6e baki hameeda tayi lokacin da take shafa, lipgloss
Barina je dakin sa nadu bashi tana fadin Haka tasakai tayi waje, dakin ya jalal tanufa, hameeda uwar gulma itama aguje tabita. “
Sallama tayi amma Shiru babu amsa, kai tsaye tasakai ta shige,”
Ganinsa tayi yayi rigin gine, yayi zurfi atunani, Zama tayi a bed side drawer amma baimasan da shigowarta ba, aranta tace su yaya anfad’a fahh, dan wannan tunanin sai wanda ya nutsa kogin soyayya. “
Ya jalal!” ya jalal ” takarkarewa tayi ta kwala ihunda yasashi mikewa zaune bbu shiri,
Kada kai tayi sannan yafara rero waka.”
????Alamar tambaya tanaga mai yawaita tunani ????????musamman yashiga halin soyayyar zamani????????yau gashi ciknta ????????yarasa wanda zai fiddashi ????????sai ita masoyiyarsa wanda sukayi kyau da kamanni????????
Kallon mamki kawai yatsaya yana mata, bai k’ara sarewa ba Sanda yaji hameeda tashigo tana nata wakar. “
????abinda yake ranka zaka fitar ka huce tunani????soyyace aranka????garaka fada bazata ficeba????????
Tunani yafara aransa, kaddai yarannan sun fahinci yana son hanna ne
Hanna ce takatse masa tunaninsa, ta6ashi tayi yajuyo gira daya tad’aga masa wacece? “
Kece yace” zaro kwala kwalan idanta tayi ” saurin gyara zancen yayi Kece fitinanniyar dakika katseni daga tunaninta ai.” sauke ajiyan zuciya sukayi daga itah har hameedan, toh yaya wacece? “
Katse zancen yayi kutashiku fita kubarmin daki, Haka dole ya korasu.”
Maya fansu suka dauko suka fita dan kai dinki. “
Duk wani abinda ammahtasan zai kawowa amma kudi sanda tad’aga tasayar, yanzu Haka tagama hada kudin zuwa gobe dasuje gun malam.”
Hanna sunfito daga gidan anty hindatu, kasncewar anguwar bame jama’a bane yasa titin bbu kowa. “
Kaitsaye suka nufi titin dan tsallake shi, a lokacin motocin MG suka danno hancinsu atitin.”
To be continued
Ur’s
Z33yyb3rw3r
[12/2, 9:26 AM] Anty Jamila D Ili: BIBIYATA AKEYI
_
Bismillahirahmanirrahim
_
Writting by
© zaynab bawa
( z33yyb3rw3r )
My first novel
Wannan fage din nakune masoyana maman zarah ???? murjanatu(admin)
And zuwairat(addansumy) zaynab bawa na kaunarku kamar yadda kuke kaunarta ILYSM
Page 31
*
Titin sukaje tsallake wa a lokacin motocin MG suka danno hancin motarsu Titin dake layin. “
Hanna ce ta juya da sauri sis na manta phone dina Adakin anty bari nadauko,” sai kin dawo amma nikam barin tsallaka zan jiraki. ” juyawa tayi da niyarr komawa ihun da hameeda ta sakene yasata juyowa da sauri, ganin hameeda tayii akasa, ashe lokacin da tajuya take yiwa Hanna magana a lokacin motocin sun rigada sun zo tsakiyar titin, hameeda bata luraba ta shiga sukuma basu tsaya ba sukaje gadan gadan kanta,” aikuma kunsan base nafada ba kunsan sojojin bazasu tsaya danta tsallaka ba. “
Aikuwa hakan ya bala’in 6ata ran Hanna ganin ko tsayawa basuyiba dan duba lafiyarta, afusace ta dauki wani katoton dutse, dan niyar jifan motocin, hanata hameeda takeyi amma fir taki jefa dutsen tayi Aikuwa kamar ta saita sai motar da MG yake ciki.”
K’aran dutsenne yadawo da hankalin MG dayake Waya, lokaci daya hankalin sojojin duk yatashi. “dan sun d’auka hari aka kawo musu, MG ne ya umarci a tsaida mota, ganin fuskar da yafiso aduk duniya idan aka cire na mahaifansa, ta madubi sai huci takeyi.”
Ganin antsaida motane yasa sojojin fir fi towa kowa da bindigarsa a hannu suka zagaye motar da MG Ke ciki. "
Umarta yayi da abude masa kofa babu musu suka bude, captain Ahmad dake gaban motanne yafitoh yana tambaya ina zaije amma ko kulashi baiyiba ya nufi wajan su hanna su sajen ma’aroof da motar su kecan gaba suna gadin hanna suma ganin haka yasa suka futo, suka nufi ogannasu. “
Su captain bala ma da suke can baya wanda dama sunga wucewar ogannasu amma ganin ya tsaya suka fito suka nufesu, hangosu yayi daga nesa ya musu alama dasu juya, bbu musu suka koma, ya karasa wajenesu hanna datake rikeda kafan hameeda tana mata sannu. “
Hameeda ce tafara kallonsu, ahankali tabugi Hanna tanuna mata ai suna kallonsu atake suka mike tsaye cikin su yahau lugude.”
Yana karasowa gabanta yafadi, subhanallah yahadu Addu'oi kawai takeyi dan azatonsu gamo sukayi deyi wuya samun namiji mai kyansa, hameeda kanma dabadan kartayi karyaba datace har daukan idoh yakeyi, "
Ta6a Hanna tayi kinga abinda kikaja mana ko” kin ta6o mana dan balarabe. ” yana karatosu wani ni’imtaccen kamshi na ziyartarsu” dakyar Hanna tattaro kuzarinta cikin jarumta dan kwarjini gareshi kamar zaki, duk sai taji yacika mata idanuwa idanuwa, adan zafafe tace. “
Tsayawa kazo yi ko kazo bata hakuri ne?? Shiru yayi ya tsaya kallonta, Eyhem tambayan ka nakeyi kawani tsareni da idoh” azafafe wani soldier yayi kanta da niyyar marinta, captain Ahmad ne yayi saurin tsareshi, katsira da aikinka kawai yafada masa. “
Rike k'ugu tayi tana karar raya, sannan taciga ba dacewa" ai dama nasan irinku bakusan darajar dan adam ba burinku kawai kuci mutuncin kowa." kokadan baiji zafin magan ganinta ba saima wani sanyi dayake ziyartar zuciyarsa, gawani irin girma kyau da cika idoh datayi masa, wutar santa ne take kara ruruwa acikin zuciyarsa. "
Hameeda ce take ta ta6a ta akan tabari amma ture hannunta kawai takeyi.”
Wasu daga cikn sojojin ne sukayi kanta a hasale, daga musu hannu yayi alamun su koma Haka suka koma badan ransu yasoba saiwani huci sukeyi, araina nace yanzu yanda kuke zabga-zabga dinnan idan aka barku saiku daketa? “????. “
Karasawa yayi har gabanta alokacin sai faduwa gabanta yakeyi, gawani irin kamshi dayake shirin rikitata .” yatsunsa guda biyu yasa ya 6alle mata baki ai babu shiri tasaki ihun azaba, sannan yace” bbu kyau yin rashin kunya anah gaba dakai” yafad’a kamar mai yin rad’a, aikuwa tana sakee bakin tace Allah ya’isa na mugu azzalumi. “
aibaisan lokacin dayawaro idanuwansa ba, wato ita wannan yarinyar batada tsorone ko kad’an?” aikuwa bata ankaraba ya k’ara 6alle mata bakin, nanma tasake sa wani ihun Atake kuma tace Allah ya’isana, aibata k’arasaba yakara 6alle mata baki,”
Ihu tasa wannan karan kan harda bubbuga k’afa takusan sa MG dariya dakyar ya danne,” Allah yahhh, aibashiri tasa tafukan hannunta tarufe bakin,”
D’an sunkowa yayi yace Allah yayime? “wata uwar harara da doka masa,” haderai yayi yace, idan kika k’ara yiwa wani rashin kunya nidake, yafada had’eda nuna kansa da ita wanda inba ita data ganiba bbu wanda yafahimta.”
Yana juya baya tace kuma sai Allah yasakamun, a hankali kaman mai tsoron yajita, aikuwa karaf a kunnensa juyawo yakara yi atsorace tayi baya, dakatar da ita yayi sannan yamatso yanda bbu wanda zaijishi, yace idan kikayi hakuri kwannan ma zaki rama da kanki, yana fadin Haka yajuya yabarta adaskare agun takasa gane wannan maganarsa ta karshe. “
Juyawa yayi wajen hameeda, sake fuska yayi, yayi wani killer smile yamata wanda yasa hameeda sake baki kamar wata doluwa.”
Cikin kwantar da murya yace _sorry_ _dear_ bansan haka zaifaru ba kiyi hakuri. "
Hadiye wani miyau tayi bakinta har yana 6ari tace bbu” “”babu komai. ” wata ‘yar dariya yayi, ok ko zaki shigo musaukeki?”
Wani bakin ciki ne ya turnuke hanna ganin yanda hameeda ke binsa da ido kamar sokuwa. ” haka kawai ta tsinci kanta da jin haushinsu duka, fuuu tabar musu wajan tayi ta nufi gidan anty hindatu.”
Kallo suka bita dashi, sannan yadawo da kallonsa kan ta, muje ko yace mata, kallonsa sa tayi sannan tace, idan na tafi bazataji d’ad’iva kuma kaga ita bakuwa ce batasan gari bah. ” tafad’a irin bahaka taso dinnan ba.”
Karki damu, kije ki kwantar mata da hankali naga kaman ranta yabaci karki barta cikin bacin rai."
Kallo mamaki tatsaya yimasa, kanne mata ido daya yayi sannan yajuya, ya nufi motarsa, captain Ahmad yagani sai wani rike dariya yakeyi, harara ya 6alla masa. “
Kai tsaye mota yawuce, suka rufa masa baya suka tafi.”
Duk abinda malam yabukata Ammah ta shirya Kai tsaye suka Kai masa, ya umurcesu dasu dawo gobe. “
Kaitsaye washe gari sassafe suka wuce ya shaida musu cewa komai ya wakana amma bazaiciba harsai randa hanna suka had’u da najeeb.”