BIBIYATA AKEYI COMPLETE HAUSA NOVEL
BIBIYATA AKEYI COMPLETE HAUSA NOVEL

To be continued
Ur’s
Z33iiyyb3rw3r
BIBIYATA AKEYI
Bismillahirrahmanirrahim
Writing by
© Zaynab Bawa
( z33iiyyb3rw3r )
*Allah subhanahu wata Ala yace,” duk mutumin dakafii k’auna dashi za’a tasheka ranar tashin k’iyama, * Ya rabb ka k’ara mana k’aunar manzonka acikin zuqatan mu, Ameen.”*
*Ka/ki kasance mai yawan tuna mutuwa, domin hakan zaisa ka/ki kasance cikin tsoron Allah."*
*Kada ki/ka kasance mai k'askantarda mutane," domin bakisan wataran waye mai taimakon kaba."*
Nasiha ce
================
Wannan shafii sadaukarwane ga duk wani masoyin BIBIYATA AKEYI inasonku ina alfaharii daku, dabazarku nake taka rawa????
Page 64
*
Najeeb ne zaune gaban mahaifinsa, jinayi mahaifinsa yana cewa Wai najeebu mai kakeson fad’amunne eyeh? “
Mai kakeson nafad’awa mahaifin yarinyar?”
Sunkuyarda kansa yayi yace Abba wallhy bana sonta, kabani time in Sha Allah zanfito da mata. “
Nisawa mahaifiyar sa dake kusa dasu tayi, tace tunda ya amince Kan cewa zai fito da wata, ni aganina abarshi, yanzu ai godiya zamu yiwa Allah daya amince zaiyi auren,”
Macene za’a iya aura mata Wanda bataso tazauna Amma namiji abin zaiyi wahalan gaske.”
Maida gilashin idonsa yayi sannan yace to Allah yaza6arda mafii alkhairii,”
Bari nasamu mahaifinta namasa bayanii, zai fahimta, mutum ne mai sauk’in kai, godiya najeeb yayi sannan yatashi yafice,”
Tunanin yakeyi aranshi yanzu idan yasamu Wanda tamasa zai sanarda mahaifinsa, dan yanzu yagama cire hanna ababin rayuwarsa, duk da cewa tana cikin zuciyarsa.”
Fadah suka shiga, sannan yace ma hanna *sweety * kishiga nizantabii, akwai aikinda zanyi.”
Kallonsa tayi tace akwai abu mai mahimmanci danakeso muyi Magana akai.”
Kallonta yayi yace kibari saina dawo, ankirani gidan minister of health yayi k’one, girgiza kai tayi tace ba k’onewa yayiba k’onawa akayi, “
Zaro ido yayi yace,”
Kinsan me kike fad’a kuwa? “
D’aga kai tayi tace, eh nasani, yanzu hakama iyalansa sunanan na taho dasu, Kuma itace ta sanar danii haka,”
Suna inahh? “
Yatambaya nuna masa motar bayansu tayi tace suna cikin can,”
Fito dasu ku shiga gida inazuwa, ina zakaje? ta tambaya,”
Babu zan biyoku Abaya,”
Zan yiwa soldier’s magana ne,”
Bud’e motar tayi tafita, sannnan ta Isa zuwaga motarsu, kar6an kabir tayi dake hannun sa’ad tafara tafiya suka biyota,”
Side d’insu ta shiga suka biyota Abaya,”
Kafin su zaauna har MG ya iso dan dama ahankali suke tafiya,”
Zama sukayi, yayinda k’anannin yaran sun kasa zama zubewa sukayi ak’asa,”
Hanna ce tace inkaiku kushiga kuyi wanka? “
Abida cikin muryar kuka tace wallhy bazan iyaba, yunwa nakejii,”
Idon hanna har yakawo ruwa na tausayinsu, shikuwa MG binsu kawai yakeyi da kallo na tausayinsu. “
Sa’ad ne yak’ar6e yace yau kwananmu uku bamucii komaiba.”
Alokacin Idon hanna hawaye yak’i tsayuwa, ” Shikuwa MG sa tafin hannuwansa yayi kawai yarufe fuskarsa tausayi da takaicii, bazai barii yace komai ba. “
Jansu d’ayan falon hanna tayi tad’auko wermer’s d’in da sukacii abincii, zuba musu tayi kowa da nasa sannnan ta ebo ruwa da roba tabasu suka wanke hannu,”
Faracin abincin sukayi kamar wasu mawuyacin zakii, ko k’akkautawa bbu. “
Hassana har tana kwaruwa, kuka ne ya cufcewa hanna tayi saurin barin falon,”
D’akinta tashiga ta ringa kukan tausayin bayin Allah nan, “
MG ne yashigo yaja jikinsa yana rarrashi,”
Ce mata yayi yanzu anemo likita ya duba su, nizan tafii wajen, wani likita kake ganii za’a nemo? “
Wa kake ganii zai riqe Amana, dan ita babbarsu ta tabbatarmun, nemansu sukeyi zasu kashesu, wani likita kake ganii zai iya yin shiru da bakinsa?.”
Niasawa yayi dan MG shi kwata-kwata ma yaman ta cewa akwai doctor acikin sojojinsa.”
Shiru hanna tayi nad’an wani lokaci sannan tace,”
Barina kira Yaya Jalal yazoshi,”
Shid’in doctor ne? “
MG Yatambaya, eh kawai tace,”
D’aukan wayrta tayi takira Yaya Jalal, ringing uku yad’auka,”
Gaisheshi tayi Jin muryar ta kaman tayi kuka, yace, hanna lafiya? “
Lafiya klau Yaya Jalal, dan Allah kazo gidana, and Yaya idan zakazo kazo da first aid box d’inka,”
Rikicewa yayi yana cewa hanna kifad’amun abunda yasameki? “
Bbu da Yaya kawai saikazo dan Allah kayi saurii tana fad’in haka ta katse Wayan,”
Tass Sanda suka tashi da abincinan,”
Alokacin tafita tasamu wani soldier, ta aikeshi yasiyowa su sa’ad, kabir Hassana da usaina Kaya, amma su Abida da karima nata zai masu.”
D’ayan flate d’in da MG yazauna kafin auransu ta nufa dasu, dan ahad’e yake da nasu saidai wata y’ar k’ofa da corridor dake tsakanii.”
Bud’ewa sa’ad d’aki d’aya tayi, sannan ta bud’e d’aki d’aya masu karima,”
Haka kawai ta tsincii kanta da kishin d’akin da MG yazauna tak’ii Bud’ewa,”
Sa’ad Bayan yayi wanka yayi wa kabir, alokacin ankawo kayansu basu tayi sukasa, sannan Alokacin Yaya Jalal ya’iso, treatment d’in ciwowin dake jikinsu yayi sannnan, suka shiga danyin bacci su huta, “
Fitowa sukayi shikuwa Yaya jalal yafi to,”
Kallan hanna yayi yace, wallhy nad’auka wani abune yafaru danaji muryarki bbu alamun walwala aciki, ” yaya ainace Maka bbu komai, Kuma kqima ksan bazan Maka k’aryaba,”
Sallama sukayi harya juya zantafii hanna tace yaya, juyowa yayi, tace kada kadamu kanka da tambayan su waye idan lokacii yayi zan sanar dakai, murmushi yayi yace, nasan baki abuu sai mai amfanii dan haka bazan damu kainaba, “
Sallama sukayi ya wuce, sai Alokacin hanna tasamu tayi sallar adhahar, dan lokacin biyu tayi,” k’ara Zuwa tayi ta dubasu, har lokacin bacci sukeyi dan yaya Jalal harda maganin bacci yabasu. ” sai 3 MG yadawo Alokacin hanna nakwance akujera ankawo abincii Amma takasa ta6awa, wata irin kewar MG dake damunta,”
Samunta yayi ahaka yak’arasa gabanta, tana kallonsa tamiqe, sannan ta tura baki tace, takafii kawani dad’e, kinyi missing d’inane ya tambaya, girgiza kai tayi tace niii? Aknme? “
A’a, kokad’qn baijii dad’in amsartaba, canja akalar zancen yayi Zuwa, kincii abincii?”
Girgiza kai tayi tace ina jiranka ne, d’an karamin tsuka yaja afili, azuciya Kuma yace kajii mun yarinya da kini bibi, natambayta tayi messing d’ina Kuma tace A’a, “
Tashi muje kicii abincin, A’a muje kafara wanka tafad’a atakaice,”
Zakimun wankan ne? ” yqtambaya, niii A’a hanna tafad’a had’eda Zaro ido.”
Gyara zamansa yayi yace Kinga ni kuwa idan bazakimun ba, is better na hak’ura.”
Shareshi tayi kamar bata jisu ba,”
Ganin tana 6ata masa lokacin yasa yahaura yayi wankansa, “
Kamshin turarensa ne doki hancinta, D’aga idanuwa tayi tana kallon sa yanda yake saukowa,”
Fara polo ce kall ajikinsa, sai bak’in wandon Jean’s, sai bak’in takalmi, yatsun kafarsa sai suka haska sosai, kamar kita6a jini yafi to, gashin sai sheki farcunansa sukeyi, “
D’auke kanta tayi kada ya kamata tana kallonsa, kawarda idanunta tayi dan karya kamata tana kallonsa, abunda batasaniba yad’ade da Ganin tana kallonshi,”
Kallonta yayi yanda kayan yanzu sukafii k’arbanta fiyeda na d’atsu, “
Akowani shiga tayi k’ara kyau takemasa,”
Bayan yak’arsso sukacii abincii sannan ta d’auki basu takai musu,”
Bayan sungama cii ne, hanna ta kira MG, shigowa yayi da sallama suka amsa dukansu, “
Kallonsa dukanta suka tsayayi, dan tabbas idan Ana nufiin had’uwa MG karshe ne.”
Ran hanna Sanda yad’an sosu ganin irin kallon dasuke masa, “
Kusada ita yazauna, yariqo hannunta, duka suka zauna, karimane tace sa’ad tashiga da hassana da hussaina da kabir d’aki yadawo,”
Bayan yadawo karima tafara basu labarin da mahaifinta yabasu bata rage ba Har izuwa biyosu da’akayi dakuma, ganin hanna datayi, tak’ara da cewa, mahaifina yanada y’an uwa dayawa, yanada dangii bila adad’in haka Kuma mahaifiyarmu ma, Amma mahaifina kune yatsaba, way’anda zasu taimaka mana, pic d’inki yabamu yace mu naimeki, dan naiman mijinki zaimana wahala,”
Sannan tafashe da kuka, itama hanna kuka sukeyi,”
Balle su abida da sa’ad da sukajii cewa mahaifinsu ya rasu, “
Nisawa MG yayi yace, yanzu haka zannema muku wajanda zaku zauna,”
Dan jibi sassafe zamuyi tafiya ina dawowa Akan, case d’innan zan sauka, Allah yajikansu yabaku hakurin rashinsu, dak’yar karima ta iya amsawa da amin.”
Mamaki ne yacika hanna ita batasan da wannan tafiya ba, Kuma tajii suu ya ambata. “
Fita yayi hanna Kuma tatsaya rarrashinsu.”