GIDAN UNCLE COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

GIDAN UNCLE COMPLETE HAUSA NOVEL

Murmushi Daddy ya fadada yace “kayy alhmdllh amma dai duk wannan ribace babu uwa a cikinta ko?” Daga kai yayi da sauri cikin qosawa da mgnr yace “kafin nayi lissafin riba saina fitar da uwa tukunna” dariya sosai Daddy yayi yace “kana samun million bakwai da kusan rabi a duk watan duniya kenan ko? Kayy naji dadi sosai” dakatar da dariyar yayi yace “am dubeni da kyau babana daga wannan watan inaso dole bisa umarnina idan ka hada kan kudadenka kazo ka kawomin million uku da dubu dari bakwai da hamsin wannan shine kason da zakake warewa na kula da lfyr Umaimah da cikin jikinta harsai ta haihu sannan a sake sabon lissafi tashi maza ka tafi gda dare yayi”

UMMUH HAIRAN CE…✍????
[1/20, 9:30 AM] UMMUH HAIRAN CE…✍????: GIDAN UNCLE

Ki biya kafin ki karanta idan kinaso ki kira number nan; 09031307566:

PAGE THIRTY-SIX

Kallon Daddy yake da tsananin mamaki yace “amma Dad….” katseshi yayi da cewa zaka samin ciwon kai “ka tashi ka tafi gdanka nace dare yayi” yana fada masa haka ya shige dakinsa ya kullo itakam Hajiya dama ta dade da tashi a gurin ya jima yana saqawa da warwarewa kafin ya miqe a salube ya sauko daga upstairs din ya nufi dakin Umaiman ya murda ya shiga.

Kaka ya tarar a tsaye tana ninke kayanta kallonsa tayi da sauri tace “Lfy Umbamban meye ya kawokada darenan?”

Zubewa yayi a qasa ya ruqo hanunta idonsa na zubar da hawaye yace “kiyiwa girman Allah Kaka ki bani aron Baby inason yin mgn da ita….” daquwa ta watsa masa tace “qaniyarka umbamban ubanme zaka fada Mata wanda baka fads mata ba a tsayin shekara daya da kukayi kuna sheqe ayarku ta banason shirme da sakarci waima kay anya qlau kake kuwa?”

Miqewa yayi ya hau gadon ya birkito Umaiman dake bacci ya dora bakinsa saman nata tare da dora hanunsa daya a cikinta yanayi mata wata irin tafiyar tsutsa wadda yasan duk nauyin baccin da dakeyi idan yayi Mata saita tashi.

Miqa tayi ta banqaro masa boobs dinta yaja ajiyar zuciya tare da sanya hanunsa da sauri ya cafka yace “ohhhhh! Baby dadi…”
Bude idonta tayi da sauri ta sauke su cikin nasa lumshe idonsa yayi yana yamutsa boobs dinta, a matuqar zafafe ta tureshi ta miqe yayi saurin miqewa yabita Allah ya taimaketa qofar a bude take ta kuwa kwasa da gudu bayanta yabi yana qwala mata Kira kicibis din da sukayi da Hajiya ne ya sashi yin baya da sauri yana sosa qeya a kunyace yace “am… Hajiya Ina… Inason mgn da it…ita Baby… Kallonsa tayi tsaf tayi baya saboda ita kanta Hameed tsoro yake bata ganin yanda saitin uhum hum dinsa taga yanda take miqewa da sauri ta fuzgi hanun Umaiman ta cillata dakinta itama ta shiga ta datse qofar da key.

Shafa kansa yayi cikin tsananin feeling da jarabarsa tasashi tsokanowa kansa ya koma ya zauna a kujera yana mayar da numfashi.
Yafi 30 minutes a zaune a gurin kafin ya miqe ya fita ya shiga motarsa da Daddy ya basa key din ya tafi gda.

Yana zuwa ya fada saman gadon yana sauke numfashi tare da janyo pillow ya rungume qam a jikinsa kamar zai shigar dashi jikinsa zuciyarsa nayi masa wani tuquqi yanzun ta tuni Babynsa ce a rungume a qirjinsa amma su Daddy sun kasa fahimtarsa.

Hakanan ya kwana juyi ita kanta feeling ya yarda kwanciyar hankali ke kawota saboda gabadaya tunaninsa ya karkata yanda zai samu Babynsa ta dawo gareshi amma bai hango wata hanya ba.

Shi ji yakema da ace Daddy cewa yayi ya bashi duk abinda ya mallaka shikuma ya barshi da Babynsa da yafi masa sauqi fiye da wannan hukuncin rabasun daya dauka.
Daqyar ya it’s tashi yayi sallah ya shirya ya nufi gdannasu babban tashin hankalinsa yanda Umaimah taqi daga wayarsa ko kadan qarshema yajita a kashe.

Yana zuwa gdan sama ya hau gurin Daddy suka gaisa babu wata alama ta bacin rai a tattare da Daddy itama Hajiyan yaga sauyi a fuskarta ba kamar jiya ba hakama Kaka amma gwanar tasa ko kallon tsiya bai samu a gurinta ba balle yasa ran samun na arziki duk hankalinsa yana kanta so yake ta dago idonta amma taqi har qafa ya rinqa turawa qasan table din yana zungurin qafarta amma ko gezau batayi ba qarshema miqewa tayi ta nufi dakinta zata shiga har takai bakin qofar yace.

“Am Baby ga motarki tazo jiya kije ki gani idan tayi miki I batayi ba sai a kawo miki wata” tana gama sauraronsa ta shige dakin ta datse qofar ta fada gadon tana sauke ajiyar zuciya quru kawai tayi ta shareshi saboda famfon da Hajiya ta kwana tanayi Mata akan halayyar da namiji ita kuwa ta hau ta zauna daram.

Haka lkc yayita tafiya kullum da sabuwar rigimar da Hameed za bullo da ita duk yanda yake tunanin samun sauqi a gurin Umaimah abin ya gagara kwata² bata sakar masa fuska kayy yanzun takai ma ko a parlourn bata zama kuma kullum qofarta a garqame yabi takan qawarta Sa’ud amma abin yaci tura saboda ita kanta Sa’ud din yanzu Umaimah bata daga wayarta sai taga dama.
Tafi² cikinta kullum qara girma yakeyi gashi har ya shiga wata na shidda ya fara fitowa sosai Daddy da Hajiya sun kasa sun tsare sun hanata fita ko qofar gda saboda sun lura batason cikin idan ta samu dama zata iya barar dashi.

Sadiya zama ya miqa a gda tunda suka rabu da Hameed bai qara waiwayarta ba gashi yaqi bata damar ganin yayanta ko sau daya suna gurin Hajiya Umaimah ke kula dasu kamar ita ta haifesu kullum basu da aiki sai shafa dan qaramin cikinta daya fara turawa suna cewa “aunty Uncle yace kin kusa ki haifa mana qani mune zamu rinqa rainonshi muna goyashi muna tafiya mkrnta dashi” itadai saidai tayi yaqe wanda akace yafi kuka ciwo saboda Allah ya sani tana cike da nadama da danasanin abubuwan da shaidan yasasu aikatawa a baya qashi tunda cikin ya shiga wata na bakwai take fama da rashin lfy ciwon ciki da ciwon mara sunje asibiti da Hajiya aka tabbatar musu da kwanciyar yarinyar ne ba daidai ba saboda haka tana buqatar kulawa sosai kallon Dr Saleem tayi tace “to amma Dr ya lfyr abinda ke cikinta?”

Murmushi yayi yace “lfyr baby qlau Hajiya amma dai a qara kulawa” da wannan kalamin suka dawo gda Hajiya tanajin so da qaunar cikin jikin Umaimah wanda tasani bata tabajin haka akan yayan Sadiya ba kodan Umaimah jininta ce oho.

Ita kuwa Umaimah a ranta ji takeyi dama ace cikin ya lalace idan taji motsin cikin ji takeyi kamar ta bigeshi daga jikinta haushi da tsanar Hameed na nunkuwa a zuciyarta saboda badan shiba da rayuwarta bata shiga wannan gararin ba.

A kuma wannan dan taqin ne Sadiya tayi aure saboda ta bibiyi Hameed yana wulaqanta ta harta gaji ta hqr ta saduda ta auri wani abokin aikinta me Mata biyu saboda takurawar da babanta yayi Mata akan cewa saidai tabar masa gda bazai iya zama da ita suna hada kafada da matansa ba kasancewar babanta matansa uku.
Hakanan ta auri Alh Salisu badon tanasonsa ba saidon gudun korar karen da babansu yakewa duk wata yarsa bazawara da taqi aure yazo kanta musamman ita da kowa yasan ita ta kashewa kanta aure da masifa da zafin kishinta da kuma qin karbar qaddara ga uwa uba rashin daukan miji a bakin komai.


Tun farkon dawowar Umaimah gda Hajiya tayima Daddy mgn akan cigaba da karatunta to lkcn semester tayi nisa saboda haka ya biya mata Jamb ta zana ya Allah ya taimaketa ta samu abinda ake buqata ta zauna jiran lkcn da zaa koma hutu saboda komai na mkrntar an gama mata Skyline University ce Daddy ya biya mata.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button