GIDAN UNCLE COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

GIDAN UNCLE COMPLETE HAUSA NOVEL

Alwala ta daura ta tayar da sallah saboda ta gama cire tsammani da jin dadin rayuwa tagama cire rai da farin ciki a rayuwarta tana sallah tana kuka tana neman zabin Allah tanason Hameed amma dole ta barshi bata farga da gangancin da tayi ba sai yanzu hakanan Umaimah ta kwana daga sallah sai karatun qur’ani sai zikiri da hailala da neman gafarar ubangiji takuwa samu sauqin abinda takeji a zuciyarta.

Shikuwa Hameed yana fita ya fada cikin motarsa ya jima a zaune yana kuka kamar qaramin yaro yana nema gafarar Allah saboda ya sani girman laifin da yayima ubangiji na sabonsa da ganganci shine dalilin da yasa ya jarabceshi da Salma matar da ko a baya yakejin kamar zai kasheta saboda ballagazancin ta da rashin kamun kanta amma yau shine yaje ya biya sadaki da hanunsa aka daura musu aure yau gata a cikin gdansa wai tana amsa matsayi daya da zuciyarsa Umaimah mata.
Da sauri ya girgiza kai yace “kai! kai!! Qaryane wlh” fita yayi ya nufi bangaren nata cikin dauriya da dakiya ya qara bata wata minti goman kafin ya bude yana mai furta “ Bismillahir rahmanur rahim La’ilaha illah anta subhanaka inni kuntu minazzalumin Allahummah la sahala maja’altahu sahala wa’anta taj’ala iza shi’ita sahala” sannan yayi sallama cikakkiya ta musulumci ya sanya kansa ciki da sauri yaja da baya saboda qaurin da yaji mara dadi ya daki hancinsa ya rintse idonsa yace “warin mene wannan?” Bai jira amsa ba ya fara raba idonsa a parlourn dako arzikin TV babu an kwashe kudi duk ankaiwa matsafa idonsa ya fada kanta ta bude qofa ta fito tana wani kwarkwasa kamar zata karye ita dama ba jiki ba ya tabe baki a ransa yace “kuma wai donta dauki hankalina takeyi ko banza shashasha” bai ida tunaninsa ba yaji tayi hugging dinsa wani irin hautsinawa zuciyarsa tayi amai ya fara qoqarin taso masa saboda ita kanta qaurin takeyi ga wani tsami tsami da takeyi kamar wacce tayi wanka da ruwan tsamin gasarar daya fara lalacewa da sauri ya saki kayan hanunsa ya tureta da sauri ta fadi gefe ya nufi dakinsa da gudu ya fada bathroom ya fara sheqa amai kamar zai amayar da kayan cikinsa.

Mamaki da tsoro suka cika Salma na yanda yayi watsi da itan ya shige dakinsa amma dake batada zuciya saita miqe ta bisa daidai lkcn daya gama amansa ya fito daga bathroom din ta shigo ta mayar da qofar ta kulle tace “Haba Hameed wai wannan wanne irin wulaqanci ne ina binka kana guduna kamar bakai kace kanasona ka auroni ba nifa bana daukar wulaqanci yanzu zan saitawa mutum zama ta qarfin tsiya tunda bashi yayi kansa ba” ko kallonta baiyi ba ya fara rage kayan jikinsa ya rage dagashi sai boxes a juyo ya dubeta yace.

“Zan kwanta kema kije ki kwanta” da sauri ta dawo daga duniyar tunanin da ta lula tace “bangane naje na kwanta ba aidai kasan wannan daren nawane dole ka bani haqqina” kallonta yayi da sauri yace “dole kuma? Aa kidai gyara kalaminki qaddarar auranki ce dole a gurin Hameed ba kwanciya dake ba ke bari kiji Salma wlh na tsaneki Salma I hate you please get out from my room”

Shashashar batama san me yace ba sai qara matsawa da takeyi jikinsa yana janyewa hanunta ta daga tayi saurin cadkar penis dinsa yayi wata irin zabura ya maketa tayi baya zata fadi yace “zanci kutumar ubanki billahil lazi zan kasheki a dakinnan idan baki fita ba banza jaka jahila wadda batasan abinda ke mata ciwo ba wlh bantaba jin tsanar wani abu a duniya kamarki ba narasa meyasa na kasa bijirewa aurenki na sabawa iyayena saboda ke na bata da abokina saboda ke nayi fada da kowa nawa saboda ke hatta kakata saida tayimin baki akanki badon komai ba saidon kin tsafaceni bazan iya bijirewa aurenki ba uwa uba matata Umaimah yarinya marainiyar Allah mai halin yan aljannah itama na barota tana fushi dani tana kuka saboda ke duk juriya da qarfin imanin Umaimah saida kika sanya zuciyarta tayi rawa har tayi yunqurin rabuwa dani kota hanyar kisa kota hanyar saki to ki rubuta ki aje Hameed baya qaunarki kuma bazai taba baki farin ciki ba ba asiri ba ko tsafi kikeyi da jini bi’izinillahi ta’ala dani da matata munfi qarfin sharrinki Salma ki ficemin daga rayuwata salin alin ki barni na rayu da farin cikina kadai bazaki taba samun gurbi a zuciyata ba kin sani na fada miki saboda haka kada kiyi yunqurin sani dole na kusanceki wlh wahala zakisha idan kuma kin dage kinason jin ya nake to a gwada nasan babu macen da zata iya daukata sai Umaimah”

Yana fadin hakan ya kamota ya riqe qugunta ya matse a hanunsa yayi tsaki yace “qugunki yayi kadan ya dauki Hameed wlh ki samawa kanki lfy ki nemi miji daidai dake ni zanyi miki komai na auren harda gdan zama da mota zan baki” kuka takeyi sosai saboda tunda take a rayuwarta namiji bai taba fada mata kalamai masu zafin na Hameed ba bata taba haduwa da namiji me taurin kan Hameed ba duk wani aikin asiri ko tsafi baya wucce kwana uku a jikinsa yake warwarewa har Togo taje gurin bokan da yake mata aikin qarshe amma Hameed da Umaimah sunqi tabu daqyar aka cusa masa nauyin bakin da bazai iya bijirewa aurenta ba to gashi anyi auran amma ta gaza samun nasara a kansa a daren farko ya caccaka mata mgnr da taji dama bata auresa ba.

Jan hanunta yayi ya fitar da ita daga dakin ya kulle qofarsa amma memakon ta tafi sai ta tsaya jikin qofar tace “na roqeka don Allah Hameed ka tausayamin ka bani haqqina karka duba halina ka duba girman haqqin aure” tsayi yayi yace nabaki damar ki fita ki nemi wani ya biya miki buqatarki amma nidai kinyimin qanqanta idan na danneki mutuwa zakiyi keni bamaki da komai da zanyi sha’awa a jikinki keba gaba ba keba baya ba dibeki kamar muciya tsohuwa dake guzumar saniya” fadawa wayi gadon ya kwanta ya dauki headphone yasa a kunnensa ya soma kiran layin Umaimah amma taqi dagawa kuma tana gani yayi ajiyar zuciya yace “Allah na gode maka bloody tayi bacci” kunna suratun junnu yayi yana saurara yanabi a haka har bacci ya daukeshi.

Da asuba ya tashi yayi wanka ya fita nufi masallaci saida ya zauna yayi azkar sannan ya fito kai tsaye bangaren Umaimah ya nufa ya bude ya shiga ya haura saman ta idar da sallah ta kwanta rungume smda Shurafah a jikinta bacci ya dauketa saboda daren jiyan gabadaya bata rintsa ba, zuba mata lulu eyes dinsa yayi yana hango damuwa kwance a fuskarta ga shatin hawaye nan kwance a oily skin dinta ajiyar zuciya yayi ya matsa a hankali ya haura gadon ya janye Shurafah ya kwantar da ita shikuma ya kwanta a jikinta nauyinsa da qamshin turarensa sune suka sata sauke ajiyar zuciya tare da bude idonta ta zubasu akan kyakkyawar face dinsa ta lumshe idonta tayi ta fara qoqarin tureshi yayi saurin kwantar da kansa a jikinta yace “nayi missing wannan oily skin din bloody babu wani jiki a duniya da yakai naki laushi da dadin tabawa” wani mugun kishi ya taso mata wato har yaje ya latse matarsa ya kwana yana kwasar dadinsa saboda ya raina mata hankali yazo zai cikata da surutun banza da wofi…….

UMMUH HAIRAN CE…✍????
[1/29, 3:14 PM] UMMUH HAIRAN CE…✍????: GU

Tureshi tayi ta miqe zata shiga bathroom ya ruqota ya hadata da qirjinsa ya matse yana shinshinar qamshin jikinta yana shafa weast dinta, tureshi tayi da sauri ta fada bathroom ta kulle ya tayi zamanta a ciki ta dora kukanta dags inda ta tsaya kuka me gunji da shassheqa tana dafe da kanta.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button