GIDAN UNCLE COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

GIDAN UNCLE COMPLETE HAUSA NOVEL

Tana gama fadin haka ta miqe ta kwasa da gudu ta fada dakinta a guje ya bita yana qwala mata kira amma Ina ta datse qofar ya durqushe a gaban qofar cikin rawar murya idonsa na zubar da hawaye yace “wal…wlh duk yanda kike tunanina ba haka nakeba bloody ki bude kiji abinda zan fada miki ni kaina shaidane kin canza daga yanda na sanki bakya tausayina amma koma ya kika zama inasonki sonki ya rufemin idona banaji bana ganin kowa sai ke zan rayu dake a haka Umaimah so dangin mutuwane baya duba rarrashi so gubane kamarsu daya da madara wlh ko zaki rinqa tsinkar gashin jikina ina mutuwa Ina dawowa kece zabina sonki yariga ya illatani bana iyayin komai sai Ina tare da tunaninki Umaimah baki taba soba shiyasa baki gane so ya yakeba wlh Hameed nakine ki yarda dani bloody….”

Shassheqar kukan Hajiya ne yasashi waiwayawa ya miqe da sauri yana dafe da qirjinsa ya fadi a gabanta yace “haj… Hajiya ki tayani bata hqr kinsani baa cikin hankalina na saki Umaimah ba wlh duk duniya bata da masoyin da yafini Hajiya ku auramin Umaimah idan ba haka ba komai zai iya faruwa dani wlh duk ma abinda take tunanin nayi mata a baya don zalinci nasani banyi don cutar da itaba Hajiya bayin kaina bane ciwone da ubangiji ya jarabceni dashi kuma na samu lfy wlh duk yanda takeso haka zamu rayu idanma tace batason na riqe ko yatsanta ne na amince nidai naji a raina itadin tawace matata ce yafimin komai dadi Hajiya kice wani abu mana”……….

UMMUH HAIRAN CE…✍????
[2/4, 6:58 PM] UMMUH HAIRAN CE…✍????: GU

Kawar dakai Hajiya tayi tace “toni meye nawa a lamarin nan Hameed tsakaninku ne babu wanda zaiyi ma Umaimatu dole kaje kaci gaba da jarraba sa’ar ka idan rabonka ce zata sauko ku daidaita amma abin da ciwo kuma Umaimah bazata fahimceka ba sai kayi da gaske saboda haka Allah yabada saa” tana fada masa haka ta shige dakinta ya buga kansa da kujerar kusa dashi yanajin wani ciwo a zuciyarsa baisan meyasa son Umaimah yaqi qyale rayuwarsa ta hutaba tabbas so masifa ne yanzu badon ta fahimci yana sonta ba da bazata fada masa mgnr nan ba amma babu komai a juri zuwa rafi.

Miqewa yayi daqyar ya shige dakinsa ya fada gado yaci gaba da rera kukansa ya kasa control tear dinsa akan lamarin daya shafi Umaimah kuka yafi masa komai sauqi akan lamarinta baitaba zubarwa da mace hawaye ba sai akan Umaimah miqewa yayi yayi sujjada yace “Allah ka mallakamin Umaimatu a karo na biyu Allah banyi zato ba ka bani ita a karon farko Allah kada kabata ikon wahalar dani” yana addu’ar yana kuka me shiga jiki.

Haka kwanaki sukayita shudewa duk ta inda Hameed ya biyo Umaimah gocewa takeyi duk wani wanda yasan zai hadata dashi ta saurareshi ya hadata dashi amma taqi sauraron kowa kalmarta daya ce tagama zaman aure da Hameed.
Wannan kalma tana caccakar zuciyarsa da haka har lkcn da aka bashi a gurin aiki ya qare ya juya California zuciyarsa taf da damuwa Umaimah tana neman fin qarfinsa qarfi da yaji ana ya gobe zai taho ne yayi mugun ganin da ya daki zucciyarsa ya rabonsa da sanyata a idonsa kwanaki uku kenan daya bita makaranta ta zage ta cire girmansa da nasabarsu ta debe masa albarka tsaf har tana fada masa ta tsaneshi ya fita daga rayuwarsa ranar yayi nadamar zuwanshi duniya da kasancewarsa namiji haka ya koma gda jiki babu qwari.

Sai yau a karin banza ya ganta tsaye da wani qato Alh Jabir a shopping suka hadu ya gigice ya rinqa binta tana yagashi hardai ya samu ta saurareshi ya biya mata kudin siyayyar da tayi naira dubu tamanin sannan ya karbi compliment card dinta sukayi sallama ta shiga motarta shima ya shiga tasa suka tafi ranar sai gashi yazo gdan suna tsaye suna hira yanda take bawa Alh Jabir amsa kawai ya isar masa ya gane ba shine a gabanta ba amma ya kasa ganewa daidai lkcn Hameed din ya fito tsayawa yayi turus gabansa na tsananta faduwa mutum na uku kenan da yazo ya tarar da ita da maza mabambanta suna hira suna dariya amma shi da yayi mata mgn sai ta daure fuska wannan abu na cizonshi ba kadan ba to ranar ma daurewa yayi yaja qafarsa yace gurin yayi mawa Alh Jabir sallama ya amsa tare da miqa masa hanu suka gaisa ya kwantar da murya kamar mutumin kirki yace “am duk da nasani yarda da amincewa ka samu daga gurinta amma bazan fasa fada maka Umaimah nine zan aureta ba kayi hqr ka rabu da ita Allah zai mayar maka da wadda tafita”

Kallonsa sukeyi dukkansu da mamaki musamman Umaimah da ta fara gajiya da wulaqancinsa tayi saurin kawar da kanta tace “am manta dashi Alh na yanada yar matsala ne kawai dai yanzu zan sanar da Daddy yanda mukayi dakai saika turo ayi mgn amma wlh da banida niyar aure kawai dai takura dasa idone banaso” tana mgnr tana sanya hanunta ta cire hanunsa daga na Alh Jabir.

Sosai wannan wulaqancin ya girgiza nutsuwarsa da kwanciyar hankalinsa harma da lfyrsa wato qiyayyar Umaimah gareshi har takai wadda zatake dangantashi da hauka? Tambayar daya rinqa yiwa kansa kenan yana kuka jikinsa yana rawa duk ya rame yayi duhu saboda damuwa da azabar kishin da yasawa ransa koda yake ba laifinsa bane kishi halitta ne bare a Shuwa’arab ba mazansu ba matansu wannan dalilin yasashi dole ya hada komatsansa cikin dare yayi booking na jirgi da asuba zakara ya bashi saa saboda Idan ya zauna a 9ja tsaf Umaimah kasheshi zatayi da baqin cikinta.

Watansa daya a California ya kasa hqr ya juyo gda 9ja saboda kiran duniya Idan ya kira wayar Umaimah bata dagawa ko WhatsApp ko SMS idan yayi Mata bata bashi amsa abun ya fara fin qarfin tunaninsa da farin cikinsa ya isa gdan ko driver bai kiraba saboda zaquwar da yayi yazo yaga sanyin ruhinsa gabansa ba qaramar faduwa yayi ba ganinta da balaraben da yataba ganin sun jera da ita a makarantarsu idonsa har lumshewa yakeyi saboda bala’i ya isa gurin kamar zaiyi musu mgn sai kuma ya fasa ya shige gdan fuuuuu yana shiga yayi watsi da system dinsa da wayoyinsa ya zube a gurin yana kiran “ya Allahu ya hakimu ya razzaqu ya rahamanu ya rahim” yama rasa meye zaice qarar faduwar kayan ne ya sanya Hajiya da Daddy fitowa da sauri daidai lkcn da Nawwas ya fito yanz rarrafe ya shige jikinsa qanqame yaron yayi yanabin iyayen nasa da kallo zuciyarsa na ciwo yace.

“Fisabilillahi Daddy adalci kenan kubar Umaimah ta rinqa kwashe² kowanne kare doki yanzu wannan kuma me yazoyi gdan nan?” Hajiya ce ta tafa hanu tace “Heee Allah na dawo inji dan cirani yanzu Hameed sanyata zamuyi a gaba mu kwadata muci ko kuwa hanata zabin ranta zamuyi shita kawo tace tanaso mgn har tayi nisa ma aure saura sati daya kayi hqr ka rungumi sorry Umaimah ta daina yayinka….” Daga mata hanu yayi a fusace ya miqe kamar mahaukaci yace “ya isa Hajiya basai kin kasheni ba naji naji abinda kikeso kice amma wlh tallahi bai isa ya auri matata ba nagaji da binku din da nakeyi kuna neman turani kabari nine na farko kuma nine na qarshe ko Sulaiman don babu yanda zanyi ne na barshi yayi shuka a gonata amma wannan kodadden balaraben bai isaba wlh saidai muyi mutuwar kasko zan saceta nabar qasar da ita idan yaso kowa ya huta kuma wlh Idan na dauketa guba zan dura mata sannan nima nasha tunda naga Allan ma bazai kasheni na huta ba gara na kashe kaina da kallon wannan ta’addancin da akeyimin ni banida gata banida masu sona bani da wanda zai tausaya min bayan kunsan komai….”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button