GIDAN UNCLE COMPLETE HAUSA NOVELNOVELS

GIDAN UNCLE COMPLETE HAUSA NOVEL

Tunda ya fara mgnr numfashinta yake bugawa da qarfi tanayi masa wani irin kallo da bazata iya cewa ga irinsa ba harya gama mgnrsa ya ruqo hanunta yace “nasan bazan samu matsala dake ba Ummuh Shurafah zaki bani hadin kai shiyasa banyi darr din sanar dake ba kuma nasani bazaki samu matsala da Salma ba saboda tanada kirki da sauqin kai kuma tanasonki tun bakisan kanki ba tasanki saboda duk wanda yasanni yasanni dake yasan matsayinki a gurina Umaimah ban boye Mata ba na fada mata matsayinki a guna kedin ta dabance saboda ke amanace a gurina kuma ke farin cikina ce……”

Kallon da yaga tanayi masa ne yasashi hadiye mgnr sa daidai lkcn wayarsa tayi ring ya daukota da sauri ya duba tare dayin murmushi ya kara a kunnensa yace “yar halak yanzun mgnrki nakewa Hearty ashe kema ina ranki” shiru yayi sannan ya kuma murmushi yace “to alhmdllh nanda sati biyu kin zama tawa kenan ok bari anjima zamuyi mgn” yana fadin haka ya juya gurin Umaimah da duk yanda takai da saurin kukanta yau hawayenta sun qafe qaf sai zugin zucci da tafasa da zuciyarta takeyi abinka da shuwa masu kishin gado.

Kallon kallo suka tsaya sunayi kafin tayi qarfin halin miqewa zatabar gurin yayi saurin riqota shima ya miqe ta juyo ta zuba masa jajayen idanunta jikinta da bakinta sai rawa yakeyi sai yanzu hawaye suka samu nasarar zubo mata cikin in’ina tace “Sak…keni Abu Shurafah…” tana fadin haka ta fincike hanunta ta dauki yarta data tashi daga bacci ta nufi bathroom da ita ta cire Mata kayanta ta sanyata a cikin bath din amma hakanan tunda ta durqushe ta kasa tashi jin zuciyarta takeyi kamar zata faso qirjinta wai ita Umaimah ita zaayiwa kishiya kishiyar ma kusan saar yayarta Jameelah kuka ya kuma kwace mata wannan karon harda shshsheqa ashe da gaske ne da mata suke cewa ko labarin mutuwa baikai na kishiya ciwo ba “Allah ka kasheni na huta” abinda ta furta kenan jitayi an sanya hanu an dagota ta daga kanta ta dubeshi da sauri shima itadin yake kallo idanunsa sun kada sunyi jawur.

Har cikin ransa yakejin ciwon kukan Umaimah ya rasa meyasa kullum shine yake zama sanadin kukanta kullum shine sanadin baqin cikinta ya rasa yaushe ne zai zamewa Umaimah farin ciki a rayuwa yaji komai daya faru tun daga kwanciyar sa jinya har kawo yanzu a gurin Aunty Zarah yasani sarai ba raayinta bane sake rayuwar aure dashi tausayinta gareshi da sadaukarwarta da kuma gudun bacin ran iyayensu shine yasata aminta da sake auransa towai shi meyasa ma yakeson qara auren ne iyakar saninshi shi ba meson tara iyali bane kuma babu abinda yakeso a gurin mace wanda matarsa bata dashi to wai meyasa yakasa bijiirewa auran Salma ne?………

Kuyi hqr wutarmu ta lalace Ina fama da matsalar charge insha Allahu zaku jini anjima idan baku jini ba kuma kuyimin uzuri.

UMMUH HAIRAN CE…✍????
[1/26, 3:14 PM] UMMUH HAIRAN CE…✍????: G.U

Ki biya kafin ki karanta idan kinaso ki kira number nan; 09031307566:

Janye jikinta tayi daga nasa a hankali sai yanzu ta sami qwarin gwiwar bude baki a sanyaye cikin sarewa da sallamawa farin ciki tace “kishiya zakayimin Uncle me nayi maka meyasa bazaka bamu damar gyara aurenmu da tsarkakeshi ba sai ka zabi kawo wata cikin rayuwarmu a lkcn da mukafi buqatar kusanci da juna ko badon komai ba don rayuwar yarmu bazance maka kada kayi aure ba Uncle amma ka sani tunda na taso a zuri’ar mu banga gdan da ake zaune da mace sama da daya ba wayyoh ni Umaimatu meyasa qaddarorina suke da tsauri ne….”

Saurin rufe Mata baki yayi da nasa ta tureshi da sauri saboda jitayi kamar ya sanya mata garwashin wuta a lebanta ta qarasa gaban Shurafah da taketa wasan ruwa ta dauki sabu ta fara sabawa yarinyar batare da tana ganin komai ba saboda zuciyarta da tayi mata nauyi.

Da sauri ya qaraso ya janyeta saboda yaga neman kashe yarinyar takeyi ya qarasa mata wankan lkcn daya fito tana hada kayanta a trolly ya tsaya sake da baki yana kallonta bata dago ta kalleshi ba har saida ta gama ta miqa masa hanu domin ya bata yarinyar amma yaqi haushi ne yasata jan akwatinta zata fice yayi saurin riqeta yace “kina hauka ne Babyn Uncle Ina zaki da safennan”

Dagowa tayi da idanunta da suka dade da canza kala zuwa jajaye ta watsa masa wani mugun kallo tace “gda zani Abdulhameed idan naci gaba da zama dakai a qasar nan sai ka kasheni kayiwa Aunty Jameelah asara don na tabbata ita kadai keda asarar rashina” tana fadin haka ta figi jakar kayanta ya kuma fincikota jikinsa na rawa yace “kiyiwa girman Allah ki tsaya ki fahimceni Umaimah wlh nima bason auren nan nakeyi ba bansan meyasa nakasa cewa aa ba plz Umaimah ki yarda dani ki karbi aurannan a matsayin qaddara ki amince dani wlh bazan taba cutar dake…..”

Marin data daukeshi dashine yasashi hadiye mgnrsa bata damu da yanayinsa ba ta dora da cewa “ ya isa haka Abdulhameed qaryar nan taka ta isheni so nawa ka cuceni cuta ta nawa kakeson yimin Hameed ka lalatamin quruciya ta wajan jarabarka ka yaudareni da kalamanka na qarya na sabawa ubangijina kayimin cikin zina na haifa ina kallon Shurafah a matsayin ciwon da bazai taba warkewa a rayuwata ba sannan yanzu kazomin da mgnr aure auren ma bana yarinya me qarancin shekaru kamar ni ba na guzuma sa’arka saar yayata sannan guzumar ma ka rasa wadda zaka hadani da ita sai Salmah Hameed Salman da babu wanda baisan tambari da kirarin gdansu ba ba kishiya ba dan miji babu uwar miji wannan shine kirarin da akewa uwarta Hameed tun ina qanqanuwata nasan da wannan kirarin sannan yanzu kazo saboda tsabar kai dan akuya ne qaramin mara kunya kacemin wai mutuniyar arziki ce ok na yarda a gurinka tunda idanunka sun rufe Salmah mutuniyar arziki ce amma ni a gurina bata isa na hada miji da ita ba wlh na hqr dakai Hameed nabar mata kai….”

Kamata yayi da sauri ya rufe bakinta a duniya babu kalmar daya tsana kamar yaji tana furucin ta hqr dashi.
Girgiza mata kai yayi yace “na…naji duk naji Umaimah amma ya zanyi wlh jinake kamar idan ban auri Salmah ba mutuwa zanyi kamar yanda nakejin idan na rabu dake zan mutu don Allah ki bani hadin kai Umaimah…” Kokowa suka rinqayi sosai ta akan saita fita inda shikuma ya dage akan bazata fita ba daga qarshe cillata yayi saman gadon ya fice ya kulleta ta waje.

Kifa kanta tayi a saman pillow ta rinqa kuka kamar ranta zai fita tanajin dama mutuwa tayi ta huta indai mutuwar hutu ce a gareta Shurafah ce ta rarrafo ta kwanta a jikinta itama tasa kukan miqewa tayi ta dauki yarinyar tana kuka tasa mata kaya ta bata nono tasha ta sake komawa ta kwanta tanajin zuciyarta kamar tayi tsalle ta fito.

Abin na Hameed kamar wasa saida suka qara kwanaki goma a Saudi babu wata mgn dake shiga tsakaninsu saidai kawai idan zai fita da safe ya kulle qofar parlourn idan ya dawo ya bude ya shiga yayi abinda yaga dama duk yanda yaso yaga ya shawo kanta taqi shawuwa takai ta kawo ma basa hada daki indai yananan to ita kuma zata kulle kanta a daki ta yini bata fito ba yasha tashi cikin dare yana buqatarta yayita dukan qofar yanayi mata magiya amma kamar batama san yanayi ba.

Hakanan a daddafe sukayi kwanaki goman suka dauki hanyar 9ja taso batace masa qala ba har suka isa katafaran gdan daya gina a tudun yola me part biyu har ciki dan taxi din ya shiga dasu suka fita ya sallameshi ya nufi wata qofa ya bude suka shiga tabi parlourn da kallo yayi kyau sosai sai qafar benen ya nufa tana riqe a hannunsa Shurafah tana daya hannun ya bude wata qofa yajata suka shiga ya sauke Shurafah dake bacci a wani qaramin gado dake gefe ya mayar da qofar ya danna Mata key ya tako zuwa gabanta yakai hanu zai ruqota ta zille da sauri yayi murmushi ya fara balle bottle din rigarsa ya balle belt din wandonsa ya zare Shortnicker din jikinsa ya nufota jikinsa na rawa ta janye ya cafkota da qarfi yace.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61 62 63 64 65 66 67 68 69 70 71 72 73 74 75 76 77 78 79 80 81 82 83 84 85 86 87 88 89 90 91 92 93 94 95 96 97 98 99Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button